Tarihin Alhaji Abubakar Imam, shahararren marubuci a ƙasar Hausa (kashi na ɗaya)

3
488

Abubakar Imam, OBE CON LLD NNMC marubuci ne, ɗan jarida kuma ɗan siyasa daga Kagara, da ke jihar Nejar Najeriya. A tsawon rayuwarsa, ya zauna a Zariya, in da ya kasance editan Hausa na farko na jaridar Gaskiya Ta Fi Kwabo, Jarida ta farko ta Hausa a Arewacin Najeriya.

A lokacin da ya rasu a shekarar Alif da ɗari tara da tamanin da ɗaya (1981), ya na da shekaru Saba’in a duniya. A lokacin da ya rasu, ya kusa kammala rubuta tarihin rayuwarsa. A cikin rubutun da ba a kammala, littafin ya ƙunshi labarin tarihin rayuwar Abubakar Imam tun daga haihuwarsa a shekarar Alif da ɗari tara da goma sha ɗaya (1911), a ƙauyen Kagara, a lardin Kontagora, a Jihar Neja ta yanzu.

Ya yi karatu sosai a hannun Bello Kagara, babban yayansa kuma mai ba shi shawara. Shi kansa Bello Kagara ya na ɗaya daga cikin mutum na farko da Turawan mulkin mallaka a Arewa suka zaɓa domin su yi karatu. A ƙarshe, zai kasance ɗaya daga cikin malaman Najeriya guda biyu a kwalejin malamai ta Katsina da aka buɗe a shekarar Alif da Ɗari Tara da Ashirin da Ɗaya (1921).

KU KUMA KARANTA: Ladi Kwali, fitacciyar me ƙera tukwane da hotonta ke kan Naira Ashirin

Abubakar Imam ya koma Katsina a shekarar Alif da Ɗari Tara da Ashirin da Biyu (1922), in da ya yi makarantar firamare.Ya kasance haziƙin ɗalibi kuma a lokacin da ya dace ya samu gurbin karatu a Kwalejin Malamai ta Katsina, wadda ita kaɗai ce irinta a Arewa a lokacin. A Kwalejin Malamai ta Katsina Abubakar Imam ya yi zamani da da yawa daga cikin ɗaliban Arewa waɗanda daga baya suka zama shugabanni.

Ya yi shekara ɗaya da Sir. Ahmadu Bello, daga baya Firimiyan Arewa sannan kuma ya sha gaban Abubakar Tafawa Ɓalewa, Firayim Ministan Najeriya na farko.Wasu daga cikin abokan karatunsa sun haɗa da; Isa Koto, babban sakataren dindindin na gwamnatin tarayya, Isa Kaita, Wazirin Katsina, Ministan Ilimi na Arewa da Bello Ɗandago, Sarkin Dawaki Maituta, babban bulala a majalisar wakilai ta tarayya a jamhuriya ta farko.

Bayan kammala karatunsa na kwaleji, Imam ya zauna a Katsina a matsayin malami a makarantar Midil. A nan ne aka gano basirar rubutunsa.Ya yi fice musamman a lokacin da ya halarci gasar adabi da Sashen Ilimi da yankin Arewa ta shirya a shekarar Alif da Ɗari Tara da Talatin da Uku (1933), in da aka zaɓo littafinsa “Ruwan Bagaja” a matsayin ɗaya daga cikin mafi kyau a cikin guda uku.

Sauran litattafai guda biyu “Ganɗoki” ne wadda babban yayansa Bello Kagara ya rubuta da “Shaihu Umar” na Abubakar Tafawa Ɓalewa. An ba shi muƙamin editan sabuwar jaridar Hausa ta Gaskiya Tafi Kwabo. Ita ce ɗaukakar rayuwarsa.

Ya zama Editan Jaridar daga 1939 zuwa 1954, Matsayinsa na editan jarida mafi tasiri a Arewa ya ba shi tushe mai ƙarfi don jagorantar abubuwan da ke faruwa a yankin.Ya samu zawarcin jami’an mulkin mallaka da ƴan kasuwar da suka kunno kai a lokacin.

Gaskiya Tafi Kwabo ta zama dandalin tuntuɓar duk wasu ƴan Arewa masu ilimi da ke neman wani zaure domin fitar da ra’ayoyinsu kan muhimman al’amura na zamantakewa da siyasa. A cikin rubutun, mutum zai sami wasiƙun ra’ayi daga kusan dukkanin shugabannin gargajiya da na siyasa na lokacin.

Daga matsayin Edita, babu yadda za a yi ya kuɓuta daga ruɗani harkokin siyasa. Shi kansa ya shiga cikin harkar siyasa yayin da ya taimaka wajen zaburar da ra’ayin siyasa a faɗin Arewa. Ya kasance ɗaya daga cikin ƴan ƙalilan da aka zaɓa a zaɓen da aka yi na dimokuraɗiyya a shekarar Alif da Ɗari Tara da Hamsin (1950) da gwamnatin mulkin mallaka ta yi a cikin majalisun yanki da na tarayya.

Ya kuma kasance ɗan gidauniyar jam’iyyar NPC ta Arewa. Amma saboda wasu dalilai da aka fi sani da shi daga baya ya ƙauracewa tarzomar harkokin siyasa ya na mai da hankali kan rubuce-rubuce da sauran ayyukan gwamnati.

Abubakar Imam, ba marubuci ba ne kawai. Ya sa hannayensa a cikin kowane irin harka ta zamantakewa da siyasa, ya kasance jagoran ra’ayi ko da yaushe, mai kishin yankin Arewa da ƙimarsa. Har ma ya ɗauki hankalin Lord Frederick Lugard mai mulkin mallaka a lokacin da ya kai masa ziyara a shekara ta Alif da Ɗari Tara da Arba’in da Uku (1943) a gidansa bayan ya yi ritaya a Burtaniya. Ya yi ta rubuta masa wasiƙa har zuwa rasuwarsa.

Ta hanyoyi da dama, Abubakar Imam na irin wannan hulɗoɗi da jami’an mulkin mallaka ya sa Arewa ta iya bayyana ra’ayoyinta da buƙatunta ƙarara. Kundin tsarin mulkin Richards na Alif da Ɗari Tara da Sittin da Huɗu (1964) ya na ɗauke da ayyukan kafa da Abubakar Imam ya yi.

3 COMMENTS

Leave a Reply