2023: Obasanjo Ya Bada Tabbacin Goyon Bayan Atiku Da PDP – Inji Shugabannin Matasan Arewa

0
396

…Sun Ce Kungiyar Bata Janye Goyon Bayanta Ga Atiku Ba

Daga; USMAN NASIDI, Kaduna.

YAYIN aka amince da cewa tun farko tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo yana da ra’ayin cewa shugabancin Kasar Najeriya a 2023 ya kamata ya fito daga yankin Kudu maso Gabas ne, gamayyar kungiyoyin da ta kunshi kungiyoyi sama da arba’in (40), gamayyar Kungiyar shugabannin matasan Arewa (NYLF) ta bayyana cewa Obasanjo ya bayar da tabbacin marawa Jam’iyyar (PDP) baya kuma tare da dan takararta, Alhaji Atiku Abubakar.

Kungiyar (NYLF), ta bayyana hakan ne a wani taron manema labarai wanda ta gudanar a cibiyar kungiyar ‘yan Jaridu ta Najeriya (NUJ) reshen Jihar Adamawa da ke garin Yola a ranar Juma’a 3 ga watan Mayu, 2022, yayin da shugaban kungiyar, Comrade Eliot Afiyo ya karanta sakon sanarwar.

Ya ce “Muna so mu bayyana cewa ba shakka tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo ya tabbatar mana da cewa yana goyon bayan jam’iyyar PDP da dan takararta na shugaban kasa Alhaji Atiku Abubakar.

“Gaskiya ne tun farko Cif Obasanjo yana da ra’ayin cewa Shugaban kasa a 2023 ya kamata ya fito daga kudu musamman ma Kudu-maso-gabas.

“Amma ya kuma lura cewa abin da kasar Najeriya ke da bukata yanzu a matsayin shugaban kasa a 2023, shi ne wanda ke da ra’ayin siyasa, ya san makirci da rugujewar siyasar Najeriya gaba daya da kuma makircin siyasar Arewa, da magudin siyasa da kuma yadda ake samun sauye-sauye na siyasa da kuma yadda za a yi siyasa, sannan da jajircewar da ake bukata wajen fuskantar al’amuran kasa, daukar tsauraran matakai, canza matsayi da kuma kalubalantar ikon da ya shafi tabbatar da adalci, daidaito, da sanin ya kamata, wannan tabbas. ” kungiyar ta ce.

Sun gabatar da cewa daga dukkan alamu, da kuma bayanan siyasa, Atiku Abubakar ne kawai ke da wadannan halaye.

“A kan haka ne Cif Obasanjo ya bayyana karara cewa da sauran mabiyansa, suka yanke shawarar tare da amincewar goyan bayan fitowar Atiku Abubakar a matsayin dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP.

“Hatta sauran ’yan siyasa sun san tabbas jam’iyyar Labour ba za ta taba kafa gwamnati a kasar domin Jam’iyyar PDP da APC suke ba komai da yan takararsu.

“Ba a ma san Peter Obi a cikin yankunan karkarar Arewa ba inda kashi 70% na kuri’u ke fitowa, balle ma a ce an zabe shi,” in ji kungiyar.

Sun bayyana cewa ba za a yi zabe ba kuma ba za a taba yin nasara ta hanyar yanar gizo ko ra’ayin jama’a a Najeriya ba saboda wadanda ke tantance wadanda suka yi nasara ba a cikin birane suke ba.

“Saboda haka, ba zai yiwu a ce ko kadan, Cif Obasanjo zai yi tunanin goyon bayan Peter Obi ba.

“Acewar Cif Obasanjo da shi mabiyansa, lokaci ya yi ba tare da adadi ba da cewa 2023 zai zama mafi kyawun lokacin a gare su don gyara komai, kura-kurai ko kuskurensu da iyalen da suka kafa don su sake tsara al’amura. Don haka yanzu lokaci ne mafi kyau don gyara kurakurai.

“Muna so mu ba da shawara cewa Cif Obasanjo mutum ne mai daraja da daukaka, mai himma da jan hankali musamman a Arewa baki daya don haka kada a yi amfani da shi wajen yada karerayi na farfaganda.”

Dangane da manufar shugabannin kungiyar Ohaneze Ndi Igbo da suka furta kalamai marasa dadi, Kungiyar (NYLF) ta ce duk da rashin adalcin da ake ganin ana yi a yankin Kudu maso Gabas, ya kamata a guji furta kalamai masu tayar da hankali.

“Mun lura da kakkausar murya da takaici, kalaman da shugaban kungiyar Ohaneze Ndi Igbo ya yi wanda ya biyo bayan sanarwar shugaban kungiyar matasan.

“Yayin da muka yarda cewa akwai babban rashin adalci a cikin al’umma musamman a yankin Kudu maso Gabas, amma muna so mu ce wannan ba lokaci ne na tsaurin ra’ayi, tsokana da kalaman batanci ba.

“Muna da ra’ayin cewa wadannan kalamai ba su da hankali kuma ba zato ba tsammani na masu kishin kasa na gaske na Najeriya don haka yanzu lokaci ya yi da za mu hada kai mu hada karfi da karfe don tunkarar aljanu da gumaka a cikin surar mutane masu kishin kasa wajen ruguza al’ummarmu.” Comrade Afiyo ya ce.

Da yake karin haske, ya ce watakila Atiku Abubakar ba Joshua ba ne da zai kai Najeriya ga Ƙasar da aka yi alkawari ba, amma babu shakka, shi ne Musa wanda zai ’yantar da al’ummar daga mugun rikon bayi da masu aikin ɗawainiya kuma daga baya ya ɗauke ta daga Masar don su haye jan teku. Don haka idan kunne ya ji, toh gangar jiki ya tsira,” in ji shi.

Da take tsokaci kan abokin takarar Atiku A 2023, kungiyar ta bayyana fatanta na cewa ba za a sake yin kura-kurai irin na 2019 ba.

“Aikin mu ne cewa ya kamata a kauce wa kura-kurai da PDP da Atiku Abubakar suka yi a 2019 ko ta halin kaka.

“Mun lura da cewa wanda ya dauka a matsayin mataimakin Shugaban Kasa da babban darakta janar na kungiyar yakin neman zaben Atiku ya haifar da halin ko-in-kula na masu ruwa da tsaki da talakawa musamman masu fada aji wanda duk da cewa Atiku ne ya lashe zaben, amma duk da haka sun yanke shawarar ba za su iya ba don dakatar da magudin da jam’iyyar APC ke yi, ko kare kuri’u ko adawa da sakamakon da INEC ta bayyana ta sauya sakamakon zaben da sake fasalin Najeriya,” inji su.

Da take mayar da martani ga abin da Atiku ya goge a shafinsa na Tuwita kan kisan Deborah Samuel, kungiyar ta ce hakan ya faru ne saboda kaunar da yake yi bil’adama.

“Hakika, muna so mu yaba wa Atiku Abubakar bisa jajircewarsa, hikimarsa da kaunarsa ga bil’adama, zaman lafiya da hakuri da addini a maimakon yi masa Allah-wadai da goge sakon da aka rubuta a shafinsa na Tuwita, domin ya yi abin bajinta amma ba kuskure ba saboda ya yi amfani da shi wajen kawar da mummunan yakin addini da ke gabatowa a kasar.

“Goge sakon da Atiku ya wallafa a shafinsa na Tuwita da kuma korar mataimakinsa kan harkokin yada labarai
lokaci, shi ne abu mafi kyawun zaɓi idan aka yi la’akari da rahotannin sirri a hannunmu kamar yadda a lokacin da aka share sakon saboda ya dakatar da husuma wanda zai iya haifar da tsanani da kuma karin sabo wanda a ƙarshe zai haifar da tashe tashen hankula, ya kuma dakile shirin da aka yi na bunkasa rikicin addini da kashe-kashen kiristoci a garin Sokoto, Kano, Katsina, Kaduna, Adamawa, Zamfara, Kebbi da Plateau.

“Muna so mu sanya shi a rubuce cewa Atiku bai san da lamarin ba sakon ba har sai da aka jawo hankalinsa ta hanyar cewa daya daga cikin mataimakansa daya roke shi da ya gaggauta goge shi bisa ga bayanan sirri da aka samu daga Kodineta din mu na Sokoto, Kano, Kaduna, Adamawa, Kebbi da Zamfara.

“Ko da wannan mataki da Atiku ya dauka, an aiwatar da shirin lalata wuraren ibada da wuraren kasuwanci kadan, godiya ga Ko’odinetocinmu na Jihohi da Malaman Addinin Musulunci irinsu Gumi da sauran su wadanda nan take suka yanke hukuncin da Atiku ya yanke, sakamakon haka an dakile kashe-kashen.

“Don haka muna so mu mika godiyarmu ga Alh. Atiku Abubakar saboda daukar irin wannan hukunci domin maslahar al’umma.

“Muna kuma mika godiyarmu gare shi duk da kasancewarsa mutum mai natsuwa, mai son zaman lafiya da cika alkawari, amma har yanzu ya sadaukar da kansa don yi wa kasa hidima, gyara zalunci, magance cin hanci da rashawa da kuma dakatar da zubar da jini marasa dalili da rashin hankali a duk fadin kasar.

“Muna da karfin gwiwa wajen cewa Atiku Abubakar mutum ne da ya yi imani da hadin kan Najeriya kuma yana ganin Najeriya a kowane dan Najeriya.
Muna godiya kwarai da gaske ga iyayenmu da dattawan da suka tsaya tsayin daka don tabbatar da nasarar Atiku Abubakar da kuma dukkan mambobin Teecom karkashin jagorancin Cif Raymond Dokpesi wadanda suka biya kuma suka sadaukar domin samun nasarar wayar da kan jama’a a zabukan fidda gwani,” in ji kungiyar.

Abin farin ciki ne da girmamawa ta a yau in yi muku jawabi kan wasu batutuwan kasa da kuma shawarar siyasa da alkiblar kungiyar shugabannin matasan Arewa (NYLF).

Zaku iya tuna cewa kungiyar (NYLF) ta sauya sheka da goyon bayanta na siyasa daga Gwamna Bala Mohammed zuwa Alh. Atiku Abubakar a ranar 26 ga Maris, 2022 lokacin da daukacin hafsoshin kasar suka kai wa Atiku ziyara. Don haka muka yi masa ado tare da Cif Dokpesi da lambar yabo na zinare da azurfa, inda suka muka wuya tare da yin mubaya’a ga Atiku Abubakar.

Don haka, sun karyata wallafe-wallafen cewa sun janye goyon bayansu ga Alhaji Atiku Abubakar kafin zaben 2023.

“Saboda haka, ba gaskiya ba ne cewa kungiyar (NYLF) ta janye goyon bayanta ga Atiku Abubakar kamar yadda wasu ’yan jarida ke yi wa Atiku Abubakar yankan-baya, musamman ma shafukan Yanar Gizo na kudancin kasar nan a kan cewa (NYLF) ta amince da Peter Obi.

“Muna so mu bayyana a fili cewa (NYLF) na bayan Atiku Abubakar dari bisa dari,” in ji su.

Kungiyar ta mika godiya ga daukacin tsofaffi ‘ya’yan Kungiyar (NYLF) da na yanzu wadanda suka yi aiki a matsayin wakilai da masu tsaron ƙofa don tabbatar da nasarar Atiku Abubakar.

“A karshe muna kara jaddada goyon bayanmu da jajircewarmu wajen tabbatar da nasarar Atiku Abubakar a zaben shugaban kasa mai zuwa ta hanyar ba shi kuri’un yankin Arewa, da dakatar da magudi ta kowace hanya, da kare kuri’u da kuma tabbatar da cewa an tanadi bayanai da kuma sanar da sakamakon zaben yadda ya kamata,” sun sha alwashin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here