Connect with us

Kungiyoyi

2023: Obasanjo Ya Bada Tabbacin Goyon Bayan Atiku Da PDP – Inji Shugabannin Matasan Arewa

Published

on

…Sun Ce Kungiyar Bata Janye Goyon Bayanta Ga Atiku Ba

Daga; USMAN NASIDI, Kaduna.

YAYIN aka amince da cewa tun farko tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo yana da ra’ayin cewa shugabancin Kasar Najeriya a 2023 ya kamata ya fito daga yankin Kudu maso Gabas ne, gamayyar kungiyoyin da ta kunshi kungiyoyi sama da arba’in (40), gamayyar Kungiyar shugabannin matasan Arewa (NYLF) ta bayyana cewa Obasanjo ya bayar da tabbacin marawa Jam’iyyar (PDP) baya kuma tare da dan takararta, Alhaji Atiku Abubakar.

Kungiyar (NYLF), ta bayyana hakan ne a wani taron manema labarai wanda ta gudanar a cibiyar kungiyar ‘yan Jaridu ta Najeriya (NUJ) reshen Jihar Adamawa da ke garin Yola a ranar Juma’a 3 ga watan Mayu, 2022, yayin da shugaban kungiyar, Comrade Eliot Afiyo ya karanta sakon sanarwar.

Ya ce “Muna so mu bayyana cewa ba shakka tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo ya tabbatar mana da cewa yana goyon bayan jam’iyyar PDP da dan takararta na shugaban kasa Alhaji Atiku Abubakar.

“Gaskiya ne tun farko Cif Obasanjo yana da ra’ayin cewa Shugaban kasa a 2023 ya kamata ya fito daga kudu musamman ma Kudu-maso-gabas.

“Amma ya kuma lura cewa abin da kasar Najeriya ke da bukata yanzu a matsayin shugaban kasa a 2023, shi ne wanda ke da ra’ayin siyasa, ya san makirci da rugujewar siyasar Najeriya gaba daya da kuma makircin siyasar Arewa, da magudin siyasa da kuma yadda ake samun sauye-sauye na siyasa da kuma yadda za a yi siyasa, sannan da jajircewar da ake bukata wajen fuskantar al’amuran kasa, daukar tsauraran matakai, canza matsayi da kuma kalubalantar ikon da ya shafi tabbatar da adalci, daidaito, da sanin ya kamata, wannan tabbas. ” kungiyar ta ce.

Sun gabatar da cewa daga dukkan alamu, da kuma bayanan siyasa, Atiku Abubakar ne kawai ke da wadannan halaye.

“A kan haka ne Cif Obasanjo ya bayyana karara cewa da sauran mabiyansa, suka yanke shawarar tare da amincewar goyan bayan fitowar Atiku Abubakar a matsayin dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP.

“Hatta sauran ’yan siyasa sun san tabbas jam’iyyar Labour ba za ta taba kafa gwamnati a kasar domin Jam’iyyar PDP da APC suke ba komai da yan takararsu.

“Ba a ma san Peter Obi a cikin yankunan karkarar Arewa ba inda kashi 70% na kuri’u ke fitowa, balle ma a ce an zabe shi,” in ji kungiyar.

Sun bayyana cewa ba za a yi zabe ba kuma ba za a taba yin nasara ta hanyar yanar gizo ko ra’ayin jama’a a Najeriya ba saboda wadanda ke tantance wadanda suka yi nasara ba a cikin birane suke ba.

“Saboda haka, ba zai yiwu a ce ko kadan, Cif Obasanjo zai yi tunanin goyon bayan Peter Obi ba.

“Acewar Cif Obasanjo da shi mabiyansa, lokaci ya yi ba tare da adadi ba da cewa 2023 zai zama mafi kyawun lokacin a gare su don gyara komai, kura-kurai ko kuskurensu da iyalen da suka kafa don su sake tsara al’amura. Don haka yanzu lokaci ne mafi kyau don gyara kurakurai.

“Muna so mu ba da shawara cewa Cif Obasanjo mutum ne mai daraja da daukaka, mai himma da jan hankali musamman a Arewa baki daya don haka kada a yi amfani da shi wajen yada karerayi na farfaganda.”

Dangane da manufar shugabannin kungiyar Ohaneze Ndi Igbo da suka furta kalamai marasa dadi, Kungiyar (NYLF) ta ce duk da rashin adalcin da ake ganin ana yi a yankin Kudu maso Gabas, ya kamata a guji furta kalamai masu tayar da hankali.

“Mun lura da kakkausar murya da takaici, kalaman da shugaban kungiyar Ohaneze Ndi Igbo ya yi wanda ya biyo bayan sanarwar shugaban kungiyar matasan.

“Yayin da muka yarda cewa akwai babban rashin adalci a cikin al’umma musamman a yankin Kudu maso Gabas, amma muna so mu ce wannan ba lokaci ne na tsaurin ra’ayi, tsokana da kalaman batanci ba.

“Muna da ra’ayin cewa wadannan kalamai ba su da hankali kuma ba zato ba tsammani na masu kishin kasa na gaske na Najeriya don haka yanzu lokaci ya yi da za mu hada kai mu hada karfi da karfe don tunkarar aljanu da gumaka a cikin surar mutane masu kishin kasa wajen ruguza al’ummarmu.” Comrade Afiyo ya ce.

Da yake karin haske, ya ce watakila Atiku Abubakar ba Joshua ba ne da zai kai Najeriya ga Ƙasar da aka yi alkawari ba, amma babu shakka, shi ne Musa wanda zai ’yantar da al’ummar daga mugun rikon bayi da masu aikin ɗawainiya kuma daga baya ya ɗauke ta daga Masar don su haye jan teku. Don haka idan kunne ya ji, toh gangar jiki ya tsira,” in ji shi.

Da take tsokaci kan abokin takarar Atiku A 2023, kungiyar ta bayyana fatanta na cewa ba za a sake yin kura-kurai irin na 2019 ba.

“Aikin mu ne cewa ya kamata a kauce wa kura-kurai da PDP da Atiku Abubakar suka yi a 2019 ko ta halin kaka.

“Mun lura da cewa wanda ya dauka a matsayin mataimakin Shugaban Kasa da babban darakta janar na kungiyar yakin neman zaben Atiku ya haifar da halin ko-in-kula na masu ruwa da tsaki da talakawa musamman masu fada aji wanda duk da cewa Atiku ne ya lashe zaben, amma duk da haka sun yanke shawarar ba za su iya ba don dakatar da magudin da jam’iyyar APC ke yi, ko kare kuri’u ko adawa da sakamakon da INEC ta bayyana ta sauya sakamakon zaben da sake fasalin Najeriya,” inji su.

Da take mayar da martani ga abin da Atiku ya goge a shafinsa na Tuwita kan kisan Deborah Samuel, kungiyar ta ce hakan ya faru ne saboda kaunar da yake yi bil’adama.

“Hakika, muna so mu yaba wa Atiku Abubakar bisa jajircewarsa, hikimarsa da kaunarsa ga bil’adama, zaman lafiya da hakuri da addini a maimakon yi masa Allah-wadai da goge sakon da aka rubuta a shafinsa na Tuwita, domin ya yi abin bajinta amma ba kuskure ba saboda ya yi amfani da shi wajen kawar da mummunan yakin addini da ke gabatowa a kasar.

“Goge sakon da Atiku ya wallafa a shafinsa na Tuwita da kuma korar mataimakinsa kan harkokin yada labarai
lokaci, shi ne abu mafi kyawun zaɓi idan aka yi la’akari da rahotannin sirri a hannunmu kamar yadda a lokacin da aka share sakon saboda ya dakatar da husuma wanda zai iya haifar da tsanani da kuma karin sabo wanda a ƙarshe zai haifar da tashe tashen hankula, ya kuma dakile shirin da aka yi na bunkasa rikicin addini da kashe-kashen kiristoci a garin Sokoto, Kano, Katsina, Kaduna, Adamawa, Zamfara, Kebbi da Plateau.

“Muna so mu sanya shi a rubuce cewa Atiku bai san da lamarin ba sakon ba har sai da aka jawo hankalinsa ta hanyar cewa daya daga cikin mataimakansa daya roke shi da ya gaggauta goge shi bisa ga bayanan sirri da aka samu daga Kodineta din mu na Sokoto, Kano, Kaduna, Adamawa, Kebbi da Zamfara.

“Ko da wannan mataki da Atiku ya dauka, an aiwatar da shirin lalata wuraren ibada da wuraren kasuwanci kadan, godiya ga Ko’odinetocinmu na Jihohi da Malaman Addinin Musulunci irinsu Gumi da sauran su wadanda nan take suka yanke hukuncin da Atiku ya yanke, sakamakon haka an dakile kashe-kashen.

“Don haka muna so mu mika godiyarmu ga Alh. Atiku Abubakar saboda daukar irin wannan hukunci domin maslahar al’umma.

“Muna kuma mika godiyarmu gare shi duk da kasancewarsa mutum mai natsuwa, mai son zaman lafiya da cika alkawari, amma har yanzu ya sadaukar da kansa don yi wa kasa hidima, gyara zalunci, magance cin hanci da rashawa da kuma dakatar da zubar da jini marasa dalili da rashin hankali a duk fadin kasar.

“Muna da karfin gwiwa wajen cewa Atiku Abubakar mutum ne da ya yi imani da hadin kan Najeriya kuma yana ganin Najeriya a kowane dan Najeriya.
Muna godiya kwarai da gaske ga iyayenmu da dattawan da suka tsaya tsayin daka don tabbatar da nasarar Atiku Abubakar da kuma dukkan mambobin Teecom karkashin jagorancin Cif Raymond Dokpesi wadanda suka biya kuma suka sadaukar domin samun nasarar wayar da kan jama’a a zabukan fidda gwani,” in ji kungiyar.

Abin farin ciki ne da girmamawa ta a yau in yi muku jawabi kan wasu batutuwan kasa da kuma shawarar siyasa da alkiblar kungiyar shugabannin matasan Arewa (NYLF).

Zaku iya tuna cewa kungiyar (NYLF) ta sauya sheka da goyon bayanta na siyasa daga Gwamna Bala Mohammed zuwa Alh. Atiku Abubakar a ranar 26 ga Maris, 2022 lokacin da daukacin hafsoshin kasar suka kai wa Atiku ziyara. Don haka muka yi masa ado tare da Cif Dokpesi da lambar yabo na zinare da azurfa, inda suka muka wuya tare da yin mubaya’a ga Atiku Abubakar.

Don haka, sun karyata wallafe-wallafen cewa sun janye goyon bayansu ga Alhaji Atiku Abubakar kafin zaben 2023.

“Saboda haka, ba gaskiya ba ne cewa kungiyar (NYLF) ta janye goyon bayanta ga Atiku Abubakar kamar yadda wasu ’yan jarida ke yi wa Atiku Abubakar yankan-baya, musamman ma shafukan Yanar Gizo na kudancin kasar nan a kan cewa (NYLF) ta amince da Peter Obi.

“Muna so mu bayyana a fili cewa (NYLF) na bayan Atiku Abubakar dari bisa dari,” in ji su.

Kungiyar ta mika godiya ga daukacin tsofaffi ‘ya’yan Kungiyar (NYLF) da na yanzu wadanda suka yi aiki a matsayin wakilai da masu tsaron ƙofa don tabbatar da nasarar Atiku Abubakar.

“A karshe muna kara jaddada goyon bayanmu da jajircewarmu wajen tabbatar da nasarar Atiku Abubakar a zaben shugaban kasa mai zuwa ta hanyar ba shi kuri’un yankin Arewa, da dakatar da magudi ta kowace hanya, da kare kuri’u da kuma tabbatar da cewa an tanadi bayanai da kuma sanar da sakamakon zaben yadda ya kamata,” sun sha alwashin.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Kungiyoyi

Ƙungiyoyin musulunci sun raba wa marayu 900 abinci kyauta a Katsina (Hotuna)

Published

on

Daga Abbas Bamalli

A wani biki mai ƙayatarwa da aka gudanar a gidan marayu na Katsina, sama da marayu 900 ne suka sami farin ciki matuƙa a lokacin da suka samu liyafar cin abincin rana, wanda ƙungiyoyi masu zaman kansu na Musulunci na ƙasa da ƙasa suka yi shirya.

Amir Sultana daga ƙasar Turkiyya tare da haɗin gwiwar Munazzama Da’awa Al-Islam (MADA) daga ƙasar Sudan ne suka shirya taron tare da haɗin gwiwar ofishin uwargidan gwamnan jihar Katsina, Hajiya Zulaihat Raɗɗa.

Shugaban ƙungiyoyi masu zaman kansu, Mufti Ahmed, ya bayyana cewa kimanin marayu 700 a ƙaramar hukumar Katsina da 200 a Jibiya ne suka ci gajiyar wannan kyakkyawan shiri.

Ahmed ya jaddada cewa manufarsu ita ce sanya murmushi a fuskokin marasa galihu, musamman marayu, da ke nuna irin yadda ƙungiyoyin ke gudanar da ayyukan jin ƙai.

KU KUMA KARANTA: Zulum ya raba wa iyalai dubu 40 tallafin abinci da kuɗi a Konduga

An samo kuɗaɗe don shirin ne ta hanyar gudumawa daga mawadata da ɗaiɗaikun mutane da suka amince da ƙungiyoyi masu zaman kansu.

Mufti Ahmed ya bayyana cewa, “Ta hanyar tallafin mun gina rijiyoyin burtsatse kusan 36 a wurare daban-daban a jihar.”

Ya ci gaba da cewa, “Yana daga cikin shirinmu na yin amfani da ragowar kuɗaɗen wajen sanya murmushi a fuskokin marasa galihu, musamman marayu a cikin al’ummarmu.

Wani ɓangare na ayyukanmu shi ne rarraba Alƙur’ani mai girma da kuma bayar da tallafin kuɗi ga marasa galihu.” Baya ga cin abincin rana, ƙungiyoyin sun kuma bayar da gudummawar dalar Amurka 400 ga marayun, wanda hakan ya ƙara haɓaka tasirin ayyukansu na alheri.

Alhaji Isah Muhammad-Musa, kwamishinan ayyuka na musamman, ya yaba da wannan mataki na ƙungiyoyi masu zaman kansu, inda ya ce hakan ya ƙarawa ƙoƙarin Gwamna Dikko wajen tallafawa marasa galihu da marayu a jihar.

Ya bayyana cewa, uwargidan gwamnan ta shirya yin irin wannan aikin na jin ƙai nan ba da jimawa ba, tare da ƙara azama wajen ɗaukaka masu buƙata a cikin al’umma.

Kalli hotona a nan:

Continue Reading

Kungiyoyi

Za a yi taron ƙasashen Musulmai da na Larabawa a Saudiyya kan yaƙin Gaza

Published

on

Saudiyya ta ce za ta karɓi baƙunci taron ƙungiyar Haɗin Kan Ƙasashen Musulmai don tattauna yaƙin Gaza

Ministan zuba jari na ƙasar Saudiyya ya ce, nan da kwanaki masu zuwa ƙasar za ta karɓi baƙuncin taron koli na ƙasashen Larabawa da ƙasashen Musulmai domin tattaunawa kan yaƙin Isra’ila da Falasɗinu.

“Za mu gani a cikin ‘yan kwanaki masu zuwa, Saudiyya ta ƙira wani taron gaggawa na Larabawa a Riyadh,” in ji ministan zuba jari na Saudiyya Khalid Al-Falih, a taron Bloomberg New Economy Forum a Singapore.

KU KUMA KARANTA: An harba rokoki daga Gaza zuwa Tel Aviv

“A cikin kankanin lokaci, makasudin gabatar da waɗannan tarukan guda uku da sauran tarukan ƙarƙashin jagorancin Saudiyya shi ne a kai ga warware rikicin cikin lumana.”

Kamfanin dillancin labaran Etemad ya rawaito cewa, shugaban ƙasar Iran Ibrahim Raisi zai tafi Saudiyya a ranar Lahadi mai zuwa don halartar taron kolin Ƙungiyar Haɗin kan Ƙasashen Musulmai, wadda ita ce ziyarar farko da wani shugaban ƙasar Iran ya kai tun bayan Tehran da Riyadh suka kawo ƙarshen rashin jituwar da aka shafe tsawon shekaru ana yi ƙarƙashin wata yarjejeniya da China ta kulla a watan Maris.

Continue Reading

Jan hankali

Sun yi wa likita dukan kawo wuƙa saboda ‘yar uwarsu ta rasu a Asibiti

Published

on

A ranar Talata ne wani mutum da ɗansa suka fusata inda suka sauke fishin su akan wani babban likita da ma’aikaciyar jinya a cibiyar kiwon lafiya ta tarayya da ke Idi-Aba, Abeokuta bayan da ‘yar uwansu ya rasu a cibiyar.

Rikicin ya ɓarke ne da misalin ƙarfe 2:00 na safiyar ranar Talata, a sashen bayar da agajin gaggawa na asibitin jim kaɗan bayan wata mara lafiya mai shekaru 53 ta rasu.

Shugaban ƙungiyar likitocin Najeriya reshen jihar Ogun, Dakta Kunle Ashimi yayin da yake zantawa da manema labarai, ya yi Allah wadai da harin da ‘yan uwan mamaciyar suka kai wa biyu daga cikin ma’aikatan jinya,akan mutuwar matar a sakamakon ciwon zuciya.

KU KUMA KARANTA:Lauya ya yi wa tsohon mijin wacce yake karewa duka a kotu

Ashimi ya ce Dr Pelumi Somorin likitan ne wanda abin ya shafa,yayin da ba a tantance ko waye ma’aikaciyar jinya ba.

Ya bayyana cewa mahaifin da ɗan, sun mari likitan yayin da aka sanar da su mutuwar yar uwar su.

A cewar Ashimi, matar ‘yar shekara 53 da aka kawo asibitin da ciwon zuciya mai tsanani, wanda ita kanta bayan binciken da ta kawo daga cibiyar da aka turo ta, ya nuna cewa,ba za ta ɗauki fiye da kwana ɗaya ba, sai dai wani ikon Allah.

“Watau ta kasance a matakin ƙarshe na gazawar zuciyarta. An bayyana hakan ga ’yan uwan ta, lokacin da aka kawo ta wurin, amma duk da haka mun yi imanin cewa,Allah kan iya yin wani abu, kuma muna jin cewa ya kamata mu yi iya ƙoƙarinmu don ganin mun taimaka mata.

“Ya taɓa faruwa a baya cewa, wani mutum da ke cikin irin wannan yanayin ya samu sauki tare da kulawar da ta dace.

“Amma abin takaici, wannan majinyaciyar ta mutu da misalin karfe 2 na safe kuma mijin da ɗan marigayiyar suka faɗa kan likitan da ke kula da mara lafiyar lokacin da aka sanar da labarin rasuwarta.

“Sun mari likitan , daga baya kuma suka hau matar mutanen da ke kusa da su suka yi ta jibgarta.

“Waɗannan mutanen kuma sun ci mutuncin wata ma’aikaciyar jinya” in ji shi.

Shugaban ƙungiyar ya ce an sanar da ‘yan sanda game da lamarin, inda ya ƙara da cewa duk da kasancewar ‘yan sanda a wajen,ɗan ya ci gaba da cin mutuncin su.

“An kira ‘yan sanda kuma DPO na ofishin ‘yan sanda na Kempta ya jagoranci tawagar ‘yan sanda zuwa wurin.

“Duk da kasancewar ‘yan sanda, ɗan mamacin ,ya afkawa wata ma’aikaciyar jinya kuma duk ƙoƙarin kwantar da hankalinsa da aka yi, ya ci tura.

“A karshe an kai mutanen biyu zuwa ofishin ‘yan sanda na Kemta, inda aka ɗauki bayanansu da na likitan da aka kai wa harin, ma’aikacin jinya da kuma shaidun da ke kewaye.”

Shugaban na NMA, ya gargadi ‘yan Najeriya da su daina cin zarafin ma’aikatan kiwon lafiya, yana mai shan alwashin cewa, duk wanda aka samu da laifi za a gurfanar da shi a gaban kotu.

“Mun yanke shawarar cewa wannan zai zama na ƙarshe kuma ba za mu yadda a bamu haƙuri ba, mun yanke shawarar mika ƙarar zuwa kotu kuma gobe za mu kasance a kotu.

“An fara duk wata shari’a kuma za mu kai wannan ƙara kotu.

“Muna so mu yi kira da kuma gargaɗi ga duk waɗanda suke zuwa asibitoci a Ogun cewa ƙungiyar likitocin Najeriya, da sauran abokanta da kowane likita, ba za su amince da kalmar “ayi hakuri” nan ba daga yanzu, daga duk wanda ya zagi wani daga cikin membobinmu.

“Za mu yi iya bakin kokarinmu wajen gurfanar da irin waɗannan mutanen kuma ba za mu amince da rokon kowa ba komai girman mutum.

“Don haka, muna rokon duk wanda yake da hankali ya yi tunanin zai iya roƙon mu daga baya don faranta ran jama’a. Ba laifinmu bane”.

Ashimi ya jaddada cewa, cin zarafin ma’aikatan lafiya ya zama ruwan dare gama duniya, wanda har yanzu ba a warware shi ba duk da kamfen da aka yi na daƙile barazanar.

Ya ce “a duniya baki daya, wannan batu ne da ke ci gaba da gudana kuma an gudanar da yakin akan hana hakan, da dama a duk faɗin duniya na yakar tashe-tashen hankula da cin zarafi da ake yi wa ma’aikatan lafiya.

“Musamman a cibiyar kiwon lafiya ta tarayya a Abeokuta, jihar Ogun da sauran asibitocin da ke kewayen Jihar Ogun waɗanda ke ƙarkashin ikonmu a matsayin kungiyar likitocin Najeriya.

“Mun gudanar da yaƙi da hani,da irin halayyar nan, da dama a kan wannan taron a baya kuma bayan yawan rokon da muka yi, sai da muka roƙi likitocinmu da su karɓi uzurin waɗanda suke yin abun

“Abubuwa irin wannan ba sa raguwa, a zahiri, wannan yana faruwa sau da yawa a lokuta da dama.”

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like