Online bahislerde yeniliğin ve kazancın buluşma noktası bettilt olmuştur.

Adres güncellemeleriyle sorunsuz bağlantı sağlayan bettilt önemlidir.

Dijital ortamda eğlencenin en güvenilir adresi bettilt oluyor.

HomeKasashen wajeAmurka ta bayyana...

Amurka ta bayyana mutane 5 da suka kai hare-hare ta intanet a kan muhimman cibiyoyin ta

Amurka ta bayyana mutane 5 da suka kai hare-hare ta intanet a kan muhimman cibiyoyin ta

Gwamnatin Amurka ta fitar da wata sanarwa mai cike da ƙayatarwa a ranar Juma’ar da ta gabata, inda ta bayyana sunayen mutane biyar da ake zargi da kai hare-hare na intanet a kan muhimman cibiyoyin Amurka.

Waɗannan mutanen, a cewar ma’aikatar tsaron Amurka, suna da alaƙa da ma’aikatar Leƙen asiri ta Iran da kuma dakarun kare juyin juya halin Musulunci (IRGC), wadda Amurka ta ayyana a matsayin ƙungiyar ta’addanci.

Ku kuma karanta: Ana zargin Trump da sace Almakashi na zinare a ziyarar da ya kai na bude gidan tarihi na Roosevelt

Sunayen mutanen da ake nema su ne:

  1. Behzad Mesri – wanda ake zargi da jagorantar hare-haren intanet akan tsarin samar da wutar lantarki
  2. Keyvan Fayyaz – wanda ake zargi da kai hari kan cibiyoyin kudi.
  3. Mojtaba Ghaleh-Kuh – wanda ake zargi da shiga cikin hare-haren satar bayanan sirri.
  4. Arman Kahzadian – wanda ake zargi da kai hari kan tsarin sufuri
  5. Saber Shahbazi – wanda ake zargi da kai hari kan cibiyoyin lafiya.

Ma’aikatar jihar Amurka ta bayyana cewa za ta bayar da tayin dalar Amurka miliyan 10 ga duk wanda ya ba da bayanan da za su kai ga kamo wadannan mutane, tare da ba da kariya da sabon wurin zama ga mai ba da bayanin.

ƙungiyar ‘Rewards for Justice’ ta bukaci duk mai da bayani ya tuntuɓe su ta hanyar layin Tor da aka tanada, ko kuma ta lambar wayar da aka buga a sanarwar.

Wannan mataki na Amurka ya zo ne a daidai lokacin da tattaunawar nukiliya tsakanin ƙasashen duniya da Iran suka tsaya cak.

Iran kuwa ta ƙi amincewa da waɗannan zarge-zargen, inda ta ce ‘Amurka na kokarin ƙara tsananta rikicin da ke tsakaninsu ta hanyar yaɗa labaran karya’.

Get notified whenever we post something new!

spot_img

Create a website from scratch

Just drag and drop elements in a page to get started with Newspaper Theme.

Continue reading

‘Yansanda da Sojoji sun hana tsoffin Sojoji Zanga-zanga a ma’aikatar tsaro

'Yansanda da Sojoji sun hana tsoffin Sojoji Zanga-zanga a ma’aikatar tsaro ‘Yan sanda da sojoji sun tare tsoffin jami’an tsaro da suka yi ƙoƙarin gudanar da zanga-zanga a Ma’aikatar Tsaro kan batun rashin biyan wasu kuɗaɗen gyaran fansho da suke...

Alaƙa tsakanin Isra’ila da Qatar na ƙara tsami: Isra’ila ta haramta fitar da kayayyakin masana’antun sojinta zuwa Qatar

Alaƙa tsakanin Isra’ila da Qatar na ƙara tsami: Isra'ila ta haramta fitar da kayayyakin masana’antun sojinta zuwa Qatar Rahotanni daga Isra’ila sun ce gwamnatin ƙasar ta ɗauki matakin hana fitar da duk wani samfurin da ya shafi masana’antun sojojinta zuwa...

Ana zargin Trump da sace Almakashi na zinare a ziyarar da ya kai na bude gidan tarihi na Roosevelt

Ana zargin Trump da sace Almakashi na zinare a ziyarar da ya kai na bude gidan tarihi na Roosevelt Wani labari mai ban mamaki da ya bazu a shafukan sada zumunta da kafafen yada labarai na ‘Plus News’ ya nuna...

Enjoy exclusive access to all of our content

Get an online subscription and you can unlock any article you come across.