Amurka ta bayyana mutane 5 da suka kai hare-hare ta intanet a kan muhimman cibiyoyin ta
Gwamnatin Amurka ta fitar da wata sanarwa mai cike da ƙayatarwa a ranar Juma’ar da ta gabata, inda ta bayyana sunayen mutane biyar da ake zargi da kai hare-hare na intanet a kan muhimman cibiyoyin Amurka.
Waɗannan mutanen, a cewar ma’aikatar tsaron Amurka, suna da alaƙa da ma’aikatar Leƙen asiri ta Iran da kuma dakarun kare juyin juya halin Musulunci (IRGC), wadda Amurka ta ayyana a matsayin ƙungiyar ta’addanci.
Ku kuma karanta: Ana zargin Trump da sace Almakashi na zinare a ziyarar da ya kai na bude gidan tarihi na Roosevelt
Sunayen mutanen da ake nema su ne:
- Behzad Mesri – wanda ake zargi da jagorantar hare-haren intanet akan tsarin samar da wutar lantarki
- Keyvan Fayyaz – wanda ake zargi da kai hari kan cibiyoyin kudi.
- Mojtaba Ghaleh-Kuh – wanda ake zargi da shiga cikin hare-haren satar bayanan sirri.
- Arman Kahzadian – wanda ake zargi da kai hari kan tsarin sufuri
- Saber Shahbazi – wanda ake zargi da kai hari kan cibiyoyin lafiya.
Ma’aikatar jihar Amurka ta bayyana cewa za ta bayar da tayin dalar Amurka miliyan 10 ga duk wanda ya ba da bayanan da za su kai ga kamo wadannan mutane, tare da ba da kariya da sabon wurin zama ga mai ba da bayanin.
ƙungiyar ‘Rewards for Justice’ ta bukaci duk mai da bayani ya tuntuɓe su ta hanyar layin Tor da aka tanada, ko kuma ta lambar wayar da aka buga a sanarwar.
Wannan mataki na Amurka ya zo ne a daidai lokacin da tattaunawar nukiliya tsakanin ƙasashen duniya da Iran suka tsaya cak.
Iran kuwa ta ƙi amincewa da waɗannan zarge-zargen, inda ta ce ‘Amurka na kokarin ƙara tsananta rikicin da ke tsakaninsu ta hanyar yaɗa labaran karya’.


