Connect with us

Labarai

Za mu ci gaba da ayyukan da muka faro a shekaru huɗu da suka gabata – Gwamnan Yobe

Published

on

Daga Ibraheem El-Tafseer

Gwamnan jihar Yobe, Alhaji Mai Mala Buni, ya ce, gwamnatinsa za ta ci gaba da gudanar da ayyukan da ta faro a shekaru huɗu da suka gabata domin inganta ci gaban jihar Yobe tare da kasancewa jiha mafi bunƙasa a Najeriya.

Gwamna Buni ya bayyana haka ne da yammacin ranar Laraba a Damaturu, lokacin da yake jagorantar taron ƙaddamar da majalisar kwamishinonin sa a wa’adi na biyu.

Gwamnan ya bayyana wasu daga cikin nasarorin da gwamnatinsa ta samu a wa’adin mulkinsa na farko a fannin inganta kiwon lafiya, samar da gidaje, farfaɗo da harkar ilimi, samar da wutar lantarki a yankunan karkara, shimfida tituna, ayyukan jinƙai, da sauransu. Sannan ya kuma ce gwamnatin ta samar da ci gaba mai ma’ana, duk da yadda aka fuskanci ƙalubalen annobar korona (COVID_19) tare da karayar tattalin arziƙin duniya koma bayan da ya mamaye fiye da rabin shekaru huɗu na farko na mulkin sa.

Gwamna Buni ya buƙaci majalisar zartaswar jihar su tashi haiƙan wajen fuskantar ayyukan ci gaban jihar wanda yake a gaban su tare da ɗora jihar Yobe a haƙiƙanin alƙiblar da ta dace domin kai wa ga matsayi mafi girma a wa’adinsa na biyu na mulki.

KU KUMA KARANTA: Gwamna Yobe ya ba da tallafin kuɗi a mutane 1000 waɗanda ambaliyar ruwa ta shafa

“Ya kamata mu mai da hankali kan ci gaban wannan jihar, kuma mu fahimci cewa babu wani abu da ya hau kanmu kamar tsayuwar mashi wajen tabbatar da mafarkin da al’ummar Yobe suke da shi wajen ganin mun bunƙasa ci gaban jihar.” In ji shi.

Gwamnan ya kuma buƙaci mambobin majalisar da su yi aiki tare, da jaddada cewa kowace ma’aikata kuma kowane kwamishina ɓangare ne mai muhimmanci a tsarin tafiyar da harkokin gwamnati.

Gwamnan ya ba da tabbacin cewa zai kammala dukkan ayyukan da ya fara a wa’adin sa na farko tare da ƙaddamar da sabbi da aiwatar da su domin amfanin al’ummar jihar.

A wani labarin kuma, Gwamna Buni ya sanar da naɗin Sakataren Gwamnatin jihar Yobe (SSG), Alhaji Baba Mallam Wali da shugaban ma’aikatan gidan gwamnatin (COS), Alhaji Abdullahi Gashu’a a matsayin SSG da COS.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like