Connect with us

'Yan bindiga

‘Yan bindiga sun kashe ‘yansanda da garkuwa da mutane 40 a Zamfara

Published

on

Daga Ibraheem El-Tafseer

Masu garkuwa da mutane sun kashe ‘yansanda biyu da wasu fararen hula tare da garkuwa da mutane kimanin 40 a ƙauyen Kasuwar-Daji da ke ƙaramar hukumar Ƙauran Namoda a jihar Zamfara.

Wani mazaunin ƙauyen ya tabbatar wa BBC cewa ‘yan bindigar sun kai harin ne da sanyin safiyar yau Talata inda suka riƙa yin harbin mai-uwa-da-wabi.

Hakan na zuwa ne kimanin mako biyu bayan da gwamnan jihar, Dauda Lawal Dare ya ƙaddamar da rundunar Askarawan Zamfara, waɗanda za su taimaka wajen yaƙi da matsalar tsaron da jihar ke fuskanta.

Zamfara na daga cikin jihohin da suke fama da matsalar tsaro, inda ‘yan bindiga ke far wa ƙauyuka suna kashewa da garkuwa da mutane domin neman kuɗin fansa.

KU KUMA KARANTA: Ina cikin waɗanda ƴan bindiga ke son kai wa hari — Dikko Radda

Gwamnatin Tarayya, wadda ita ce kundin tsarin mulki ya ɗora wa alhakin tabbatar da tsaro a faɗin ƙasar, na cewa tana ɗaukan matakan da suka kamata wajen shawo kan lamarin.

A tattaunawarsa da BBC cikin kwanakin baya, ƙaramin minstan tsaro na Najeriya Bello Matawalle ya ce ana ɗaukar matakan kawar da matsalar baki ɗaya.

Sai dai duk da haka ana ci gaba da samun kashe-kashen al’umma da garkuwa da su domin neman kuɗin fansa.

Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

'Yan bindiga

‘Yan bindiga sun kashe mutane 5 a iyakar Nijar da Najeriya

Published

on

'Yan bindiga sun kashe mutane 5 a iyakar Nijar da Najeriya

‘Yan bindiga sun kashe mutane 5 a iyakar Nijar da Najeriya

‘Yan bindiga sun kai hari a kan iyakar Nijar da Najeriya, inda suka kashe mutane biyar tare da jikkata wani daya a garin Dambu da ke ƙaramar hukumar Bazaga ta gundumar Birni N’Konni, sannan suka sace dabbobi da dama a garin.

Wannan lamari dai ya faru ne a daidai lokacin da damuna ke ci gaba da kankamawa a yankuna da daban-daban na Jamhuriyar Nijar.

An dai juma ba a ji ɗuriyar ‘yan bindiga a kan iyakokin Nijar da Najeriya ba, inda suka afkawa al’ummar garin Dambu da ke cikin ƙaramar hukumar Bazaga.

KU KUMA KARANTA:‘Yan bindiga sun sace ‘yan jarida 2 da iyalansu a Kaduna

Hakimin garin Dambu Halidu Assoumane ya ce maharan sun shigo garin da kusan karfe goma sha biyu na daren ranar Asabar, inda suka shigo a kafa, kafin su buɗe wuta da manyan bindigogi, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane biyar tare da jikkata wani da yake cikin mawuyacin hali yanzu haka a asibitin Galmi.

Ya ce ‘yan bindigar sun yi awon gaba da dukiya mai yawa da suka hada da rakuma da shanu kafin jami’an tsaro su isa wurin.

A kwanakin baya dai shugaban gundumar Birni N’Konni, kuma shugaban majalisar tsaron wannan yanki, Kaptin Abubakar Ali Shina, ya yi kira ga mutanen garuruwa da ke kan wadannan iyakokin da su dauki matakan kula da abin da ke kai komo da ma kariya, kamar irin yadda babban birnin yakin na N’Konni ya kafa kwamitocin ‘yan kato da gora, domin samun damar kare kai tare da gaugauta sanar da jami’an tsaro.

Shi ma masanin harakokin tsaro, Malam Yusha’u Abdullahi, ya ce yana da kyau mutanen garuruwan da ke wannan yankin su kafa kwamitocin tsaro don kare garuruwan su, kamar yadda makwabtansu na Najeriya ke yi, wanda da zarar sun ga motsi abun da ba su yarda da shi ba su gaggauta sanarwa da jami’an tsaro don su kawo musu ɗauki.

Continue Reading

'Yan bindiga

Mahara a Benuwe sun kashe mutum 18 da sace magidanci da ’ya’yansa

Published

on

Mahara a Benuwe sun kashe mutum 18 da sace magidanci da ’ya’yansa

Mahara a Benuwe sun kashe mutum 18 da sace magidanci da ’ya’yansa

’Yan bindiga sun kai hari unguwar Mbache da ke ƙaramar hukumar Katsina-Ala a Jihar Benuwe, inda suka kashe mutum 18 tare da sace wani mutum da ’ya’yansa biyu.

Shugaban riƙon ƙwarya na ƙaramar hukumar, Mista Justin Shaku ne, ya tabbatar da faruwar lamarin.

Ya ce sun samun kiran neman agaji da misalin ƙarfe 11:00 na dare kan cewar mahara sun kai hari yankin.

Shaku, ya bayyana cewar maharan sun tattara mutanen waje ɗaya ne kafin daga bisani suka harbe su a lokaci ɗaya.

Shi da sauran jami’an yankin sun gana tare da sanar da kwamishinan ‘yan sanda faruwar lamarin.

A cewarsa, harin ya tayar da hankulan mazauna yankin kan yiwuwar dawowar ayyukan ƙasurguman ‘yan bindiga.

Ya bayyana fatan cewa yanayin tsaro zai inganta, duk da ƙalubalen da ake fuskanta a yanzu.

Shugaban ya bayyana cewar duk da taɓarɓarewar sha’anin tsaro da aka fuskanta a yankin a baya, amma an samu zaman lafiya kafin sake aukuwar wannan harin.

KU KUMA KARANTA:‘Yan bindiga sun sako mahaifiyar Rarara

Ya buƙaci al’ummar yankin da su kwantar da hankalinsu tare da ba su tabbacin cewa Gwamna Hyacinth Alia ya himmatu wajen magance matsalolin tsaro a jihar baki ɗaya.

Kakakin ’yan sandan jihar, SP Sewuese Anene, ya tabbatar da kai harin kuma ya bayyana cewa ana gudanar da bincike a kai.

Anene, ya tabbatar wa jama’a cewa an ƙara yawan jami’an tsaro a yankin kuma ya buƙaci mazauna yankin da su kwantar da hankalinsu.

A cewarsa jami’an tsaro na aikin don daƙile duk wata barazanar tsaro a Katsina-Ala.

Continue Reading

'Yan bindiga

‘Yan bindiga sun kashe mutum 21 a wani bikin aure

Published

on

'Yan bindiga sun kashe mutum 21 a wani bikin aure

‘Yan bindiga sun kashe mutum 21 a wani bikin aure

Wata ƙungiya ɗauke da makamai ta kai hari a yayin wani bikin aure a tsakiyar ƙasar Mali tare da kashe aƙalla mutane 21, kamar yadda mazauna yankin suka faɗa a ranar Laraba.

Hakan na zuwa ne a daidai lokacin da shugabannin sojojin ƙasar Afirka ta Yamma ke fafutukar yaƙi da tashe-tashen hankula daga masu tsattsauran ra’ayi.

Maharan sun kutsa ƙauyen Djiguibombo akan babura wanda ke garin Bandiagara a yammacin ranar Litinin ɗin da ta gabata yayin da mazauna yankin ke bikin ma’auratan, a cewar Bakary Guindo, shugaban ƙungiyar matasan yankin.

KU KUMA KARANTA:‘Yan bindiga sun kashe malamin jami’a a Katsina, sun sace ‘ya’yansa

“Yawancin waɗanda abin ya shafa yankan rago aka musu” in ji Guindo.

Kawo yanzu dai babu wata ƙungiya da ta ɗauki alhakin kai harin, sai dai ya biyo bayan irin wanda ƙungiyar masu tsattsauran ra’ayi ta JNIM da ke da alaƙa da Al-Qaida ke kai hare-hare a yankin.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like