Connect with us

Labari

Yan Bindiga Sun Kashe Ma’aikata 36 A Jihar Kaduna – Yan Kwadago

Published

on

Daga; Mustapha Imrana Abdullahi.

SHUGABAN kungiyar kwadago (NLC), reshen Jihar Kaduna, kwamared Ayuba Magaji Suleiman ya bayyana cewa ma’aikata mutum 36 ne suka rasa rayukansu sakamakon matsalar yan bindiga a Jihar.

Sakamakon hakan ne ya sa a wajen taron bikin yayan kungiyar kwadagon domin murnar ranar bikin ma’aikata ta duniya aka yi shuru na minti daya domin tunawa da wadanda suka rasu sakamakon matsalar rashin tsaro da kuma wadansu tsauraran yanayin da aka shiga.

Ayuba Magaji wanda ke magana a wajen taron ranar ma’aikata ta shekarar 2022 a babban filin wasa na ABS da ke Kaduna ranar Lahadi ya yi kira ga ma’aikata da kowa ya tabbatar ya mallaki katin zabe domin fitar da duk wani dan siyasa da ba zai kare miradunsu ba.

Shugaban na kungiyar kwadago ya kuma bukaci yayan kungiyar da su shiga a dama da su a cikin harkokin siyasa gadan gadan a madadin su tsaya a matsayin wadanda suke a kan Katanga.

Ya kuma bayyana damuwarsa da halin da yan fansho suke ciki musamman ma irin yadda ake samun saukin biyan kudin yan fansho da kudin alawus alawus da kuma yadda ake tsawaita batun tantance su kafin a tabbatar da an biyasu Hakkinsu kamar yadda yake a dokar aiki.

Ayuba Magaji ya kuma yaba wa Gwamnatin Jihar Kaduna bisa irin yadda take gudanar da aikin gine ginen tituna da sauransu musamman a garuruwan Kaduna Kafanchan da Zariya.

Sai dai ya ce samar da shugabanci nagari ya wuce irin yadda ake yin aikin a halin yanzu don haka ake bukatar a yi aiki sosai ta fuskar shigar da al’umma a cikin tafiyar da Gwamnati, yi wa kowa adalci da doka da oda tare da samun dai daito.

Ya kuma yi kira ga Gwamnatin Jihar Kaduna da ta canza irin salon tsohon yayin gudanar da dangantaka tsakanin ta da kungiyoyin kwadago wanda hakan zai ba ta damar tafiya da zamani kamar yadda ake yi a duniya ta hanyar tattaunawa da ma’aikata a duk abin da za ta gudanar a tsakaninsu.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labari

EMAS69 • LINK ALTERNATIF SPORTBOOK SBOBET

Published

on

By

Emas69 adalah bandar taruhan sportbook sbobet terlengkap yang saat ini sangat dikenal seluruh masyarakat Indonesia dengan melalui link alternatif Emas69. Pada permainan taruhan sportbook, setiap pertandingan sepak bola yang dilangsungkan dapat dijadikan sebagai tempat bagi seluruh masyarakat Indonesia untuk melakukan taruhan dengan menggunakan uang asli. permainan taruhan bola online dapat dilakukan dengan bebas sesuai dengan pertandingan yang berlangsung dan juga team sepak bola yang disenangi untuk memperoleh kemenangan dan kepuasan dari setiap taruhan sportbook di situs Emas69.

Continue Reading

Labari

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Published

on

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi - TUC/NLC

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

Gamayyar ƙungiyar ƙwadagon Najeriya ta ce tayin Naira 70,000 da shugaba Tinubu ya yi a matsayin mafi ƙarancin albashi da babu ne gara ba daɗi.

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

KU KUMA KARANTA:NLC ta ƙira taron gaggawa bayan gwamnati ta jingine batun ƙarin albashi

Wannan dai na nuna a karo na farko tun neman mafi ƙarancin albashi mafi yawa a Najeriya Naira 615,00 ya sauƙo Naira 477,000, shugabannin ƙwadagon sun maida wuƙa kube ta hanyar yin na’am da tayin da gwamnati ta yi.

Bayan kammala ganawa babban sakataren ƙungiyar ƙwadagon ta TUC Komared Nuhu Toro ya ce sun amshi tayin da gabatar da hakan gaban majalisun su “mun kai majalisar ƙolinmu, tayin da shugaban ƙasa ya bayar sun kuma lamunta da shi da fatan Allah ya sa albarka…ai Naira 70,000 ɗin nan da babu ne gara ba daɗi.

Tuni ma’aikata na sassa daban-daban suka fara maida martani da mafi sauƙin shi ne na nuna ba abun da suka iya don jagorori sun miƙa wuya.

Malamin makaranta Muhammad Bello Nawaila ya ce ba wani tasiri da mafi ƙarancin albashin zai yi in an duba ɗan karen tsadar rayuwa.

Ita ma ƙungiyar gamayyar ƙungiyoyin arewa CNG da ke marawa gwagwarmayar ma’aikatan baya ta ce matuƙar shugaba Tinubu bai yi garambawul ga lamuran walwalar ma’aikata da matasa ba, za a iya fuskantar ƙalubale “mu na gujewa guguwar juyin juya hali a Najeriya matuƙar gwamnati ba ta farka ta ɗauki matakan gaskiya na zahiri ba.”

Alamu na nuna batun neman ƙarin mafi ƙarancin albashi zai dakata zuwa wani lokaci don ‘yan ƙwadagon sun yaɗa gora sai komawa kan batun tsadar rayuwa.

Continue Reading

Kasashen Waje

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Published

on

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump - Pennsylvania

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Sakataren tsaron cikin gida na Amurka, Alejandro N. Mayorkas ya fitar da wata sanarwa game da harbin da aka yi a wurin yaƙin neman zaɓen tsohon Shugaban ƙasar Donald Trump a jihar Pennsylvania da safiyar yau.

A cikin sanarwar, Sakataren tsaron cikin gidan na Amurka Mayorkas ya bayyana cewa, “Ni da Daraktan ma’aikatar leƙen asiri Cheatle mun yi wa Shugaba Biden bayani game da harbin da aka yi yau a Pennsylvania. Ma’aikatar tsaron cikin gida (DHS) da Ma’aikatar Leƙen Asiri suna aiki tare da abokan aikinmu, masu kula da kiyaye doka don gudanar da bincike kan harbin.

KU KUMA KARANTA:Kotun Ƙolin Amurka za ta yanke hukunci kan takarar Donald Trump

Sanarwar ta ƙara da cewa, “Muna Allah wadai da wannan tashin hankalin da kakkausar murya tare da yaba wa hukumar leƙen asiri bisa matakin gaggawar da ta ɗauka a yau. Muna tare da Shugaba Biden, tsohon Shugaba Trump, da yaƙin neman zaɓensu, kuma muna ɗaukar duk matakin da ya dace don tabbatar da tsaronsu. Kula da tsaron ’yan takarar Shugaban ƙasa da kuma taron yaƙin neman zaɓensu na ɗaya daga cikin muhimman abubuwan da sashenmu ke ba da fifik

Tun farko Mai magana da yawun ma’aikatar leƙen asiri Anthony Guglielmi ya fitar da sanarwa a dandalin sada zumunta X, cewa, “Ma’aikatar leken asiri ta aiwatar da matakan kariya kuma tsohon Shugaban ƙasar yana cikin ƙoshin lafiya. Yanzu haka Hukumar tana gudanar da bincike, ta kuma sanar da Hukumar Binciken manyan laifuka ta FBI.”

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like