Al'ajabi
Yadda miji ya guji matarsa saboda gemu ya fito a fuskarta
Wani magidanci yayi watsi da matarsa saboda gashi ya fito mata a haɓarta.
Mandeep Kaur ta yi aure ne a shekara ta 2012 kuma ta yi imanin cewa ta sami abokin rayuwa na har abada.
Shikam mijin Kaur tsaf ya guje wa matarsa a daidai lokacin da ta fara gashin gemu a fuska, kammaninta ya fara sauyawa izuwa irin na maza, inda ya watsar da aurensu cikin ‘yan shekaru.
KU KUMA KARANTA:Dalilai 7 masu Haɗari da zai sa mu guji cin gandar fatar dabbobi
Matar mai shekaru 33 ta shiga tashin hankali bayan aurenta ya mutu, ta ji kamar rayuwarta tazo ƙarshe saboda wannan cutar halitta da ke kira Hirsutism.
Menene hirsutism?
A cewar wani masani ta fuskar lafiya Mayo, hirsutism wani yanayi ne a cikin mata wanda ke haifar da tsayi da yawa na gashin a cikin fuska, ƙirji da baya.
A cutar hirsutism, ƙarin gashi yakan taso daga haddi na hormones na maza (androgens) testosterone.
An ba da rahoton cewa Kaur taƙi karbar lalurar, amma daga baya, ta yanke shawarar neman taimako, inda ta fara halartar Gurdwara – wurin ibadar mabiya addinin Sikh.
Kuma a hankali Kaur ta rungumi ƙaddararta, ta bar gemunta. Ta ke ɗaura rawani, ta dena aske gemunta da gashin baki.
Takan hau babur ta zagaya ƙauyensu tana noma tare da yayyenta, wani lokaci mutane kan yi mata kallon namiji, amma muryarta na tona mata asiri cewa mace.
Ta ce ta ɗauki lokaci kafin ta saduda, amma a ƙarshe ta haqura, don haka ta daina jin kunyar gemun nata.
Al'ajabi
Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas
Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas
Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.
Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.
Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.
An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.
KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja
Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.
Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.
Al'ajabi
An ƙona mutane suna Sallar Asuba a masallaci a Kano
An ƙona mutane suna Sallar Asuba a masallaci a Kano
Rundunar ‘yan sandan jihar Kano a arewacin Najeriya ta ce ta kama wani mutum da ake zargi da cinna wa wani masallaci wuta yayin da mutane ke Sallar Asuba ranar Laraba.
Lamarin ya faru ne a ƙauyen Gadan da ke Ƙaramar Hukumar Gezawa a jihar ta Kano, da misalin karfe 5:20 lokacin da ake sallah, a cewar sanarwa ‘yan sanda.
Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Kano, Abdullahi Haruna Kiyawa ya tabbatar wa da TRT Afrika Hausa faruwar lamarin da kama mutumin da ake zargi, sai dai ya ce ana ci gaba da gudanar da bincike.
Abdullahi Kiyawa ya ce bincike ya nuna cewa mutumin da ake zargi da cinna wutar Shafi’u Abubakar mai kimanin shekaru 38 ya jefa wata roba ne ɗauke da fetur cikin masallacin, sannan ya cinna wuta.
KU KUMA KARANTA: Mahara a Anambara sun ƙona fadar babban Basarake ƙurmus
Kakakin ‘yan sandan ya ce mutum 24 ne suka ƙone a masallacin, da suka haɗar da manya 20, yara huɗu.
An garzaya da duka waɗanda suka jikkata zuwa asibiti don ba su kulawa, amma babu wanda ya mutu a haɗarin, a cewar sanarwar ‘yan sandan.
Al'ajabi
An tsinci gawar wata ɗaliba a cikin ɗaki a Kano
An tsinci gawar wata ɗaliba mai suna Aisha Yahaya ta Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Aliko Ɗangote da ke Wudil, a wani gida da ke wajen jami’ar.
Aisha, ɗaliba ce da ke matakin karatu na uku wato ‘level 300’ a sashen nazarin Kimiyya da Fasahar Abinci na jami’ar wadda aka tsinci gawarta bayan ta koma ɗakinta.
An ce ɗalibar ta rubuta jarrabawarta ta farko a zangon karatun na farko da ake yi a jami’ar.
Wasu daga cikin abokan karatunta sun danganta mutuwarta da shiga cikin matsi da damuwa a dalilin karatu da kuma zana jarrabawar.
A cikin wasiƙar ta’aziyyar, hukumar jami’ar ta bayyana matuƙar baƙin cikinta dangane da rasuwar Aisha Yahaya.
KU KUMA KARANTA: An tsinci gawar wani mutum a kan titi a Kano
Sanarwar ta ce, “Aisha ɗaliba ce mai hazaƙa wadda ta rasu a dalilin bugun zuciya. Za a riƙa tunawa da ita a kan sha’awarta na karatu da jajircewarta kan harkokin karatunta.”
Jami’ar ta ƙara da cewa, ba a iya gano wata da ke tattare da ita ba gabanin mutuwarta saboda ba ta nuna alamun rashin lafiya ko fama da wata cuta ba.
-
Kotu1 year ago
Kotu tayi watsi da ƙarar APC game da zaɓen Abba Gida Gida
-
Labarai9 months ago
Dalilin da ya sa na saka wa matata sasari – Wani magidanci a Potiskum
-
Ƙasashen Waje1 year ago
Ɗaliban Najeriya a Sudan sun nemi a kwaso su daga ƙasar
-
Labarai1 year ago
‘Yan banga sun kama wani mutum da ke yunƙurin sace yarinya a Kano