Connect with us

'Yansanda

Yadda aka min dukan mutuwa ina tsaka da ɗaukan rohoton ambaliyar ruwa a Ganuwar Kuka.

Published

on

Daga Abubakar TAHIR, Hadejia

Labarin cike yake da ban tausayi, dalilin rashin gaggauta ɗaukan matakin gaggawa daga mahukunta kan lamarin ambaliyar ruwa dayake cima mutane tuwo a kwarya tsawon shekaru babu kuma wani shiri na musamman daga gwamnatoci wajen daƙile wannan matsalar.

Dayake lamarin ambaliya ya ƙazanta a garin Hadejia dama garuruwa kamar Ganuwar Kuka, Auyo, Hago, Kadime, Kubayau dss. Wannan tasa gidajen radio da jaridu suka rinƙa tuntuɓata domin sanin halin da kuma matakin da gwamnati ke ɗauka kai tsaye.

Bayan shigata garin Ganuwar Kuka, na lura da cewa cikin mintuna sha biyar ruwa ya kusa gamawa da garin. A take na gabatar da ID Card ɗina na aiki inda wasu matasa danakega sun waye suka biyo ni domin yin hirasa dasu.

Bayan na ɗora musu kyamara don na naɗi abun da suke da bukata haka tasa matasan suka faɗi irin halin da suke ciki tare da neman agajin ƙungiyoyi. Bayan mun kammala na ɗan gusa gaba kaɗan domin cigaba da daukan bayanai.

Katsam sai naji an taho da gudu inda aka bugeni da ƙarfi a kaina, a take wayoyin dake hannuna ƙirar Infinix da Itel suka zuge cikin ruwa. Ɗagowar da zanyi domin naga wanne dalili sai naji an cigaba da dukana ta koina aka dannan kaina cikin wani rafi da suke Kira ruwan Makasa. A haka sukayi ta dilmiya kaina suna dukana wasu suna cewa ku dake shi Nikwa inata kokarin nusar dasu ID card dina ina ce musu aiki nake.

Bayan Ɗan wani lokaci na fiddar rai daga cigaba da nunfashi nan take wasu mutane sukayi ta maza suka hanasu wanda daba dan an kawomin ɗaukin ba da tuni sun kasheni tunda a take wasu sun zare wuqaqe.
Wasu suna ku kasheshi, ɓarawone, Ina ce musu kuduba ID card dina.

Haka aka kaini gidan Maigari ya bani ruwa nayi wanka ya bani sabin Kaya na saka Inda ya buƙaci na dawo na cigaba da aiki nace masa A’a. Najefar da kuɗaɗena inda aka kawomin ɗan abinda yarage naira 2500.

A haka Maigari Ya bada babura aka kawoni Haɗejia inda a take na tafi babban asibitin Hadejia domin jinya. Na ɗauki tsawon kwanaki uku a asibitin banma san a Ina nake ba. An sallameni ranar juma’a zuwa gida domin cigaba da karɓan magani.

Abokanen aiki Yan jaridu sun ji halin da nake ciki inda labarin ya chanja daga jin halin danake ciki.

Mutanen Garin sun buƙaci a cigaba da kawo musu ɗaukin tare da SAWABA Fm, suna nuna rashin jin ɗadinsu Kan abinda ya faru dani. Ya zuwa yanzu jikina na daɗa samun sauƙi, saidai Ina fama da matsananci ciwon wuya da baya sakamakon harin.

Haka Kuma na sanar da jamian tsaron farin kaya,Yan sanda, Civil defence, Ƙungiyar Yan jaridu, domin zaƙulo waɗannan ɓatagari wanda suka yi ƙoƙarin hallakani, Allah yayi da sauran kwana a gaba.

Jamian tsaro sun gayyaci Mai garin inda ya tabbatar da faruwar lamarin Wanda yake da alaqa da sakacin gwamnati wajen shigowa cikin lamarin ambaliyar, wanda suka huce haushinsu a kaina danaje ɗaukan rohoton.

Haka shima Shugaban ƙaramar hukumar Auyo, Baffa shinge, ya tabbatar da faruwar lamarin. Ya zuwa yanzu dai, jami’an tsaro na ciga da bincike wajen ganosu inda ni
kuma nake cigaba da jinyar harin, nake sa rai kan samun adalci daga garesu.

1 Comment

1 Comment

  1. Pingback: Yadda aka min dukan mutuwa ina tsaka da ɗaukan rohoton ambaliyar ruwa a Ganuwar Kuka. – LEGEND FM DAURA

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

'Yansanda

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

Published

on

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

Rundunar ’yan sandan Najeriya ta tube wa wasu jami’an ta biyar kaki sakamakon zargin su da karɓar cin hancin kuɗi kimanin Naira miliyan uku.

Mataimakin Shugaban ’yan Sanda mai kula da Shiyya ta shida ta da ke Jihar Kuros Riba, Jonathan Towuru, ya sanar a Kalaba cewa ’yan sandan sun kwace kuɗin ne da bakin bindiga a hannun wani mai abin hawa.

A makon jiya ne aka zargi jami’an da ƙwayar kuɗin da bakin bindiga a hannun wani mutum da rundunar ta sakaya sunansa.

Yanzu haka waɗanda ake zargin an tuɓe masu kaki amma ana tsare da su ana bincike, da zarar an same su da laifi kotu za a turasu ta yanke masu hukuncin da ya dace.

KU KUMA KARANTA: ’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe

Mataimakin shugaban ’yan sandan ya ce waɗanda ake zargin su da karɓar cin hancin kuɗi Naira milyan uku daga wannun wani.

Ko a kwanan baya irin haka ta taba faruwa a kan babbar hanyar Kalaba zuwa Ikom inda aka kama wasu ’yan sanda kan karbar na goro.

Tafiya a kan hanyar na yawan zargin ’yan sanda da kula da shingen bincike a kan hanyar da yawan tatsar su kuɗi.

Continue Reading

'Yansanda

‘Yan sanda sun kama mutum 2 da ake zargin sace mahaifiyar Rarara

Published

on

Yan sanda sun kama mutum 2 da ake zargin sace mahaifiyar Rarara

‘Yan sanda sun kama mutum 2 da ake zargin sace mahaifiyar Rarara

Rundunar ’yan sandan Jihar Katsina ta sanar da cafke wasu mutum biyu bisa zargin hannu a garkuwa da mahaifiyar fitaccen mawaƙin siyasar nan, Dauda Kahutu Rarara.

Mai magana da yawun rundunar a Katsina, ASP Abubakar Sadiq Aliyu ya ce “muna tsare da mutum biyu kan lamarin, muna ci gaba da bincike.”

Tun farko, Kwamishinan tsaro na Jihar Katsina, Nasiru Mu’azu ya ce an sace dattijuwar ce a daren Juma’a a ƙauyen Kahutu da ke Karamar Hukumar Ɗanja.

Mu’azu ya ce waɗanda suka sace matar sun yi hakan ta hanyar bi ta bayan gida, inda suka sace ta ba tare da jami’an da ke tsaron gidan sun sani ba.

Ya kuma bayyana cewa tuni aka tura jami’an tsaro waɗanda suka bazama cikin dazuka domin bin sawun ’yan bindigar.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan bindiga sun yi garkuwa da mahaifiyar mawaƙi Rarara

Neptune Prime Hausa ta ruwaito shaidu a kauyen sun ce da misalin karfe daya na dare ne dandazon ’yan bindiga suka kutsa gidan dattijuwar suka yi awon gaba da ita.

“A kafa suka zo, ba su yi harbi ba a lokacin da suka ka yi awon gaba da ita cikin ’yan mintoci.

“Dattijuwar ba ta bijire musu ba a lokacin da suka memi ta biyo su.

“Duk da cewa ’yan bindigar sun samu wasu mutane a gidan, amma mahaifiyar Rarara kaɗai suka ɗauka.

“Babu wani yunƙuri da aka yi na tunkarar ’yan bindigar a lokacin da suke tafiya da ita saboda bindigogin da suke ɗauke da su,” in ji wani mazaunin ƙauyen na Kahutu.
Ya ce, “Watakila maharan sun bar baburansu ne daga nesa suka tako zuwa cikin ƙauyen a kafa.

“Muna rokon Allah Ya kuɓutar da ita cikin koshin lafiya domin tana taimaka mana sosai a wannan ƙauyen.

“Danta Rarara mai yawan taimakon al’umma ne, kuma ya kawo mana abubuwan ci gaba sosai a garinmu,” in ji shi.

Continue Reading

'Yansanda

‘Yan sanda sun kama kawali na ’yan bindiga

Published

on

'Yan sanda sun kama kawali na ’yan bindiga

‘Yan sanda sun kama kawali na ’yan bindiga

Daga Muhammad Kukuri 

Wani wanda yake kai wa ’yan bindiga karuwai domin yin lalata da su ya shiga hannun jami’an tsaro.

’Yan sanda sun bayyana cewa kawalin ya kuma ƙware wajen yin safarar makamai ga ƙungiyar jagoran ’yan bindiga mai suna Arɗo, wanda ake nema ruwa a jallo a yankin Kagarko da ke Jihar Kaduna.

An kuma gano cewa mutumin wanda yake harkar hada-hadar tura kuɗi ta PoS, shi ke kai wa iyalan ’yan bindiga kuɗaɗe a yankin na Kagarko.

Dubun kawalin ta cika ne a yayin wani samamen haɗin gwiwa da ’yan sanda suka gudanar a yankin.

Kwamishinan ’Yan Sandan Birnin Tarayya, ya sanar ranar Talata cewa wanda ake zargin ya shaida musu cewa shi ke tsara yadda ake kai wa ’yan bindiga karuwai da miyagun ƙwayoyi da ma’aikatan lafiya a duk lokacin da suke buƙata.

KU KUMA KARANTA: Ƴan sanda a Kano sun kai mutanen da ake zargi da sayar da dala ba bisa ƙa’ida ba kotu

“Ya kuma amsa cewa yana yin dakon kuɗi tare da rabawa ga iyalan ’yan bindiga.

“A cewarsa, kuɗaɗen da ya raba wa iyalan ’yan bindiga sun haura Naira miliyan ashirin,” in ji kwamishinan ’yan sandan.

Igwe ya ce wanda ake zargin ya tabbatar musu cewa ’yan bindigar da ke ƙarƙashin Ardo sun kai 15 kowannensu da bindiga ƙirar AK-47.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like