Connect with us

Ƙasashen Waje

Sojojin Amurka za su kammala ficewa daga Nijar 15 ga Satumba

Published

on

Sojojin Amurka za su kammala ficewa daga Nijar 15 ga Satumba

Sojojin Amurka da ke zaune a Nijar sun soma ficewa daga ƙasar kuma za su kammala ficewa daga ƙasar a ranar 15 ga watan Satumbar 2024, kamar yadda wata sanarwar haɗin-gwiwa ta bayyana wadda Amurka da Nijar ɗin suka fitar a ranar Lahadi.

Duka ɓangarorin biyu sun sanar da cewa sun cimma matsaya ta wareware dangantaka inda sojojin na Amurka suka soma ficewa bayan Nijar ɗin ta yi iƙirarin suna zaune ne ba bisa ƙa’ida ba.
Akwai sojojin Amurka kusan 1,100 a Nijar da ke zaune waɗanda Amurkar ta ce suna taimakawa domin yaƙi da ta’addanci.

A watan Maris, sojojin da ke mulki a Nijar suka bayyana cewa wata yarjejeniyar tsaro da aka cimmawa a 2012 tsakanin Nijar da Amurka an yi ta ne “ba tare da izinin” Nijar ba.

KU KUMA KARANTA: Rundunar sojin Najeriya ta nemi Nijar ta kama shugaban ‘yan bindiga da take nema

An kori sojojin Faransa

Nijar ta bayyana cewa Amurka ta yi ta ƙoƙarin hana ta dangantaka da Rasha, wadda tuni ta tura masu horar da sojoji da kayayyakin yaƙi domin su cike gurbin na Faransa waɗanda Nijar ɗin ta kora a kwanakin baya.

Nijar ɗin ta kori dakarun na Faransa 1,500 daga ƙasarta.

A watan Satumbar 2023, shugabannin sojin Nijar sun ce sojojin Faransa sun gaza yaki da ‘yan tada kayar baya duk da cewa sun shafe fiye da shekaru goma a ƙasar.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Ƙasashen Waje

Wani harin haɗin-gwiwa na Amurka da Birtaniya ya kashe mutum biyu a Yemen

Published

on

Wani harin haɗin-gwiwa na Amurka da Birtaniya ya kashe mutum biyu a Yemen

Wani harin haɗin-gwiwa na Amurka da Birtaniya ya kashe mutum biyu a Yemen

Sojojin Amurka da na Birtaniya sun sanar cewa sun kai hare-hare kan mayaƙan Houthi da ke Yemen.

Ranar Alhamis kafar watsa labarai ta Houthi ta tabbatar da kisan aƙalla mutum biyu a hare-haren.

Ma’aikatar tsaron Birtaniya ta ce an kai hare-haren na haɗin-gwiwa ne a wurare uku a birnin Hodeidah da ke gaɓar Bahar Maliya.

KU KUMA KARANTA: Sojojin Amurka za su kammala ficewa daga Nijar 15 ga Satumba

Gidan talbijin na Al Masirah wanda ƙungiyar Houthi take gudanar da shi ya ruwaito cewa an kashe aƙalla mutum biyu sannan aka jikkata mutum 10 a hare-haren da aka kai a wani gini na gidan rediyo a lardin Al-Hawk na birnin Hodeidah.

Continue Reading

Ƙasashen Waje

Kenya ta soma sauraron ƙararraki kan zargin cin zarafi da sojojin Birtaniya suka yi

Published

on

Kenya ta soma sauraron ƙararraki kan zargin cin zarafi da sojojin Birtaniya suka yi

Kenya ta soma sauraron ƙararraki kan zargin cin zarafi da sojojin Birtaniya suka yi

Kenya za ta soma zaman sauraren ƙararrakin jama’a a ranar Talata kan zargin take hakkin ɗan’adam da kuma cin zarafi da sojojin Birtaniya suka yi a kasar wadda ta taba yi wa mulkin mallaka.

Sashen horar da sojojin Birtaniya a Kenya (BATUK) wuri ne na tafiyar da ayyukan da suka shafi tattalin arzikin mutane da dama a tsakiyar garin Nanyuki, inda aka kafa sansanin soji na dindindin, amma kuma ana zargin sojojin da ke wurin da aikata laifuka ciki har da kisan kai.

Ɗaya daga cikin manyan laifuka da suka fi ɗaukar hankali a shekarar 2012, shi ne na tsintar gawar wata mata ‘yar ƙasar Kenya a cikin wata rijiya a Nanyuki, inda ganinta da rai na ƙarshe da aka yi tare da wani Sojan Birtaniya ne.

Iyalan Agnes Wanjiru sun shigar da ƙara a Kenya kan mutuwar matashiyar mai shekaru 21, amma babu wani ci gaba da suka samu kan shari’ar, inda aka yi ta ɗage sauraron ƙarar.

Yanzu dai ana sa ran sake sauraron ƙarar a ranar 10 ga watan Yuli kamar yadda kafafen yada labarai na ƙasar suka rawaito.

A makon jiya ne majalisar dokokin Kenya ta sanar da cewa za ta gudanar da zaman sauraron ƙararrakin jama’a har guda hudu ciki har da na Nanyuki kan cin zarafin da ake zargin sojojin Birtaniya da aikatawa a ƙasar.

Za a yi zaman sauraron ƙararrakin ne tsakanin ranakun Talata da Alhamis na wannan makon inda za gudanar da ”bincike kan zarge-zargen take hakkin bil’adama da suka haɗa cin zarafi da azabtarwa da tsare mutane ba bisa ka’ida ba da kuma kashe- kashe,” a cewar wata sanarwar da majalisar ta fitar.

KU KUMA KARANTA: Ana fargabar zaftarewar ƙasa ta rutsa da mutane da dama a Kenya

Kazalika zaman zai yi duba kan “zargin take hakkokin ɗa’ar aiki da suka haɗa da cin hanci da rashawa da aikata zamba da kuma nuna wariya da cin zarafi da sauran munanan dabi’u.”

Birnin Landan da Nairobi suna takun-saƙa kan batun hukunta sojojin Birtaniya da suka take dokokin Kenya, inda a baya gwamnatin Birtaniya ta ce ba ta amince da hurumin kotun Kenya na bincike kan kisan Wanjiru ba.

Da yake amsa tambayoyi kan sauraron karar na wannan makon, mai magana da yawun hukumar Biritaniya ya shaida wa kamfanin dillacin labarai AFP cewa: “Hukumar Birtaniya a Nairobi da BATUK suna da niyyar ba da hadin kai ga binciken.

“Haɗin gwiwar ayyukan tsaro na Birtaniya da Kenya na ɗaya daga cikin manyan ginshiƙan dangantakarmu kuma horon da muke samarwa ta haɗin gwiwa da ayyukan da muke yi tare suna taimakawa wajen samar da tsaro ga al’ummar Kenya da Birtaniya,” in ji shi.

A ranar Alhamis din da ta gabata ne tawagar Birtaniya ta ce babban kwamishinanta Neil Wigan ya gana da iyalan Wanjiru, waɗanda suka dade suna neman a yi musu adalci kan kashe ta da aka yi.

“Taron ya ba da dama ga Babban Kwamishinan ya saurari ‘yan’uwan marigayiyar tare da yi musu ta’aziyya. Kazalika ya samu damar jaddada matsayar Birtaniya na ci gaba da bayar da cikakken haɗin kanta ga binciken da Kenya ke yi kan (mutuwar Misis Wanjiru),” in ji sanarwar.

A watan Oktoban 2021 ne, Jaridar ‘The Sunday Times’ ta Biritaniya ta ruwaito cewa wani soja ya shaida wa abokansa cewa sun kashe Wanjiru kuma ya nuna musu gawarta.

Rahoton ya yi zargin kan cewa an sanar da manyan jami’an soji game da kisan, amma ba a dauki wani mataki akai ba.

An ƙaddamar da bincike kan batun ne a shekarar 2019 amma ba a bayyana sakamakon ba ga al’ummar.

‘Yan sandan Kenya sun sanar da cewa za a sake buɗe binciken bayan rahoton da Jaridar Sunday Times ta fitar.

Iyalan Wanjiru sun shigar da karar sojojin Birtaniya a Kenya da kuma ‘yan sanda da jami’an shari’a da na siyasa na Kenya kan batun mutuwarta.

Continue Reading

Ƙasashen Waje

Ana lalata mutuncin bil’adama a Gaza – Ministan Turkiyya

Published

on

Ana lalata mutuncin bil'adama a Gaza - Ministan Turkiyya

Ana lalata mutuncin bil’adama a Gaza – Ministan Turkiyya

Ministan Lafiya na Turkiyya ya ce ana lalata mutuncin bil’adama a Gaza a yayin da ake ci gaba da kai hare-hare ba kan fararen hula ba har ma da cibiyoyin kiwon lafiya.

A wani taron Majalisar Lafiya ta Duniya (WHA) a Geneva, Fahrettin Koca ya ce “A Gaza, ana lalata mutuncin bil’adama a gaban dukkan idanunmu, ana yi mata rugu-rugu.”

KU KUMA KARANTA: An yi zanga-zangar neman ƙasashen Musulmai su tura sojoji don taimaka wa Falasɗinawa a Gaza

“An ga cewa ƙasashen da ke iƙirarin ci gaba su ne a baya sosai a fannin darajta dan’adam, sun gwammace su yi shiru yayin da ake kashe yara da jarirai da hanyoyin a salon da ake tunanin ya gushe a duniya,” in ji shi. Ya ƙara da cewa:

“Wadanda ake kiran sun fi kowa ci gaba a fannin dimokuradiyya su ne masu ƙin mayar da hankali kan kukan al’umma”.

“Dukkanmu mun kasance fursunonin wannan baƙin tarihi” ya ce.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like