Connect with us

Labari

Ramadan: El-Zakzaky Ya Tallafawa Yan Jaridu Da Kayan Abinci Da Kudi A Kaduna

Published

on

Daga; USMAN NASIDI Da Mustapha Imrana, Kaduna.

A KOKARIN da yake na ganin ya tallafawa al’umma musamman Mabukata daga halin kangin kuncin rayuwa da al’umma ke fuskanta, Fitatcen Malamin addinin musulunci da ke tarayyar Najeriya Sheikh Ibrahim Yakub El-zakzaky kuma Shugaban Kungiyar (IMN), ya tallafawa wasu yan Jaridu dake Jihar Kaduna da Kayan Abinci da Kudin cefane don rage radadin kuncin rayuwa da ake fama dashi.

Da yake mikawa manema labaran a Jihar Kaduna kayan abincin, Malamin addinin Kirista Fasto Yohanna Y. D Buru, ya shaidawa yan Jaridar cewa Malam Sheikh Ibrahim Yakubu El-Zakzaky ne ya bashi wannan kayan abincin domin ya rabawa yan Jaridun ta yadda za su samu damar yin walwala tare da farin ciki da iyalansu a wannan watan mai albarka na Azumin Ramadana da ake ciki.

Ya kara da cewa wannan aikin rabon Kayan Abincin na daya daga cikin irin karamcin da babban malamin ke yi wajen inganta rayuwar al’umma tare da nuna kauna a duk shekara, musamman a cikin irin wadannan lokutan.

Ya ce “Kuma hakan zai taimaka wajen samun zaman lafiya da walwalar rayuwar Jama’a don haka Malam Zazzaky ya aiko da wannan kayan abincin a ba yan Jaridu”.

“Ko a jiya da Sheikh Ibrahim Yakubu El- Zazzaky ya bayar da kayan abinci aba matan da mazajensu suka rasu ga marayu su na tare da su a yankin Kudancin Kaduna, hakazalika a bisa ga irin yadda labaran da yan jarida suka bayar hakika jama’a da dama duk sun yi murna da farin ciki da samun labarin taimakon da aka ba dimbin jama’a.

Acewarsa, a bisa irin kokarin da yan jarida ke yi ne ya sa a halin yanzu Malam Zazzaky da kansa ya ce a kawo musu wannan kayan abincin da suka hada da Shinkafa, Masara, Dawa da Gero domin kowa ya samu sukunin yin walwala tare da iyalansa”. Inji Fasto Buru.

Ya ci gaba da cewa hakika Malam Sheikh Ibrahim Yakubu El- Zazzaky ya na godiya da irin kokarin da yan Jaridu suke yi, juma kamar yadda aka ga wannan kayan abincin nasu haka aka aika da shi zuwa wadansu Jihohin a cikin kasar nan da nufin sama wa jama’a saukin rayuwa.

A karshe, Sheikh El-Zakzaky ya roki al’umma da yin amfani da damar lokacin da ake ciki wajen Addu’o’in samun karin zaman lafiya a kasar domin hakan zai taimaka wajen tabbatar da samun zaman lafiya da ciyar da al’umma gaba.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labari

EMAS69 • LINK ALTERNATIF SPORTBOOK SBOBET

Published

on

By

Emas69 adalah bandar taruhan sportbook sbobet terlengkap yang saat ini sangat dikenal seluruh masyarakat Indonesia dengan melalui link alternatif Emas69. Pada permainan taruhan sportbook, setiap pertandingan sepak bola yang dilangsungkan dapat dijadikan sebagai tempat bagi seluruh masyarakat Indonesia untuk melakukan taruhan dengan menggunakan uang asli. permainan taruhan bola online dapat dilakukan dengan bebas sesuai dengan pertandingan yang berlangsung dan juga team sepak bola yang disenangi untuk memperoleh kemenangan dan kepuasan dari setiap taruhan sportbook di situs Emas69.

Continue Reading

Labari

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Published

on

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi - TUC/NLC

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

Gamayyar ƙungiyar ƙwadagon Najeriya ta ce tayin Naira 70,000 da shugaba Tinubu ya yi a matsayin mafi ƙarancin albashi da babu ne gara ba daɗi.

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

KU KUMA KARANTA:NLC ta ƙira taron gaggawa bayan gwamnati ta jingine batun ƙarin albashi

Wannan dai na nuna a karo na farko tun neman mafi ƙarancin albashi mafi yawa a Najeriya Naira 615,00 ya sauƙo Naira 477,000, shugabannin ƙwadagon sun maida wuƙa kube ta hanyar yin na’am da tayin da gwamnati ta yi.

Bayan kammala ganawa babban sakataren ƙungiyar ƙwadagon ta TUC Komared Nuhu Toro ya ce sun amshi tayin da gabatar da hakan gaban majalisun su “mun kai majalisar ƙolinmu, tayin da shugaban ƙasa ya bayar sun kuma lamunta da shi da fatan Allah ya sa albarka…ai Naira 70,000 ɗin nan da babu ne gara ba daɗi.

Tuni ma’aikata na sassa daban-daban suka fara maida martani da mafi sauƙin shi ne na nuna ba abun da suka iya don jagorori sun miƙa wuya.

Malamin makaranta Muhammad Bello Nawaila ya ce ba wani tasiri da mafi ƙarancin albashin zai yi in an duba ɗan karen tsadar rayuwa.

Ita ma ƙungiyar gamayyar ƙungiyoyin arewa CNG da ke marawa gwagwarmayar ma’aikatan baya ta ce matuƙar shugaba Tinubu bai yi garambawul ga lamuran walwalar ma’aikata da matasa ba, za a iya fuskantar ƙalubale “mu na gujewa guguwar juyin juya hali a Najeriya matuƙar gwamnati ba ta farka ta ɗauki matakan gaskiya na zahiri ba.”

Alamu na nuna batun neman ƙarin mafi ƙarancin albashi zai dakata zuwa wani lokaci don ‘yan ƙwadagon sun yaɗa gora sai komawa kan batun tsadar rayuwa.

Continue Reading

Kasashen Waje

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Published

on

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump - Pennsylvania

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Sakataren tsaron cikin gida na Amurka, Alejandro N. Mayorkas ya fitar da wata sanarwa game da harbin da aka yi a wurin yaƙin neman zaɓen tsohon Shugaban ƙasar Donald Trump a jihar Pennsylvania da safiyar yau.

A cikin sanarwar, Sakataren tsaron cikin gidan na Amurka Mayorkas ya bayyana cewa, “Ni da Daraktan ma’aikatar leƙen asiri Cheatle mun yi wa Shugaba Biden bayani game da harbin da aka yi yau a Pennsylvania. Ma’aikatar tsaron cikin gida (DHS) da Ma’aikatar Leƙen Asiri suna aiki tare da abokan aikinmu, masu kula da kiyaye doka don gudanar da bincike kan harbin.

KU KUMA KARANTA:Kotun Ƙolin Amurka za ta yanke hukunci kan takarar Donald Trump

Sanarwar ta ƙara da cewa, “Muna Allah wadai da wannan tashin hankalin da kakkausar murya tare da yaba wa hukumar leƙen asiri bisa matakin gaggawar da ta ɗauka a yau. Muna tare da Shugaba Biden, tsohon Shugaba Trump, da yaƙin neman zaɓensu, kuma muna ɗaukar duk matakin da ya dace don tabbatar da tsaronsu. Kula da tsaron ’yan takarar Shugaban ƙasa da kuma taron yaƙin neman zaɓensu na ɗaya daga cikin muhimman abubuwan da sashenmu ke ba da fifik

Tun farko Mai magana da yawun ma’aikatar leƙen asiri Anthony Guglielmi ya fitar da sanarwa a dandalin sada zumunta X, cewa, “Ma’aikatar leken asiri ta aiwatar da matakan kariya kuma tsohon Shugaban ƙasar yana cikin ƙoshin lafiya. Yanzu haka Hukumar tana gudanar da bincike, ta kuma sanar da Hukumar Binciken manyan laifuka ta FBI.”

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like