Connect with us

Labari

Na Shiga Hadarin Mutuwa Saboda Buhari – Nastura Ashiru Sharif

Published

on

Mustapha Imrana Abdullahi
Shugaban kwamitin Amintattun gamayyar kungiyoyin matasan arewacin Nijeriya Dokta Nastura Ashiru Sherif, ya bayyana cewa a can baya ya shiga munanan hadurran mutuwa saboda ganin Buhari ya zama shugaban kasa da zaton za a gyara kasar baki daya.
Nastura Ashiru Sharif ya bayyana hakan ne a lokacin da yake tattaunawa da kafar Talbijin ta “Tambarin hausa” da ke da mazauninta a cikin garin Kano.
Nastura ya ci gaba da cewa a kokarin ganin Muhammadu Buhari ya zama shugaban Nijeriya a can baya “akwai lokacin da an kira ni a Kaduna mun gama tattaunawar da zamu yi ni da abokina muka kama hanyar Kano mun je garin Kwanar Dan Gora, sai muka ga ana yin fashi sai muka tsaya kamar yadda kowa ya tsaya wanda daga baya sai muka ga motoci na aron hanya suna tafiya ta bangare daya,mums sai muka bi kar yadda sauran jama’a suke yi, ashe canza wuri suka yi ta yadda da kazo sai kawar ka gansu a dai dai wani hawa a kan hanya, to,  Nike tuki sai kawai na canza na juya motar baki daya”, inji Nastura.
“Nan take kawai sai suka biyo mu da gudu muna tafiya sai kawai na taka motar da gudu na shiga wata hanya a lokacin marar kwalta da ta nufi wani kauye ashe su mutanen garin sun san yadda lamarin yake domin ana yawan tare hanyar, ni kuma sai na rufe fitilar motar nan da nan mutanen garin suka ce in shiga in ajiye motar a wani wuri sai muka fito muna kallon barayin nan suka yi harbe harbensu muka shiga wani masallaci wannan kenan”.
Sai kuma zamu je wayar wa da jama’a kai a dai dai garin Toro, muna cikin mota kirar Bus mai jan fenti Kawai sai muka ga jama’a suna yin taron wata jam’iyya daban da ta mu kafin ka ce me dukkan gilashin motar an zubar da su nan da nan aka fitar da mu daga cikin motar amma sai Allah ya rufa mana asiri da akwai wani dan Jihar Bauchi da jama’ar duk sun san shi sai dattawa suka taso suka ce muma hakika Buhari zamu zaba, wannan ne ya cece mu domin motarmu mun saki wakar Buhari rikon Najeriya sai mai gaskiya.
Akwai kuma wani misalin guda daya ” in da muka je wani taro a gidan Arewa cikin Kaduna muna wani taro amma aka turo wasu yan dabar siyasa suka tayar da mu,malaman addini da Limamai suka rika cika rigunansu da Iska su na rugawa domin yan dabar siyasa sun kawo hari a dakin taron da dai misalai da yawa duk a kan Buhari muka samu wadannan tsallake rijiyar da baya”.

Nastura ya kuma ce shi a matsayinsa na mutum daman can bai amince da batun karba karba ba domin da ka ce kada wasu su tsaya takara domin sun fito daga wani bangare na kasar nan to hakika an taka tsarin Dimokuradiyya domin ya ba kowa dama a tsarin tsayawa da zaben wanda mutum ke bukata.

Ni ɗan jarida ne mai zaman kansa. Mawallafi kuma mai sharhi a lamarin yau da kullum.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labari

EMAS69 • LINK ALTERNATIF SPORTBOOK SBOBET

Published

on

By

Emas69 adalah bandar taruhan sportbook sbobet terlengkap yang saat ini sangat dikenal seluruh masyarakat Indonesia dengan melalui link alternatif Emas69. Pada permainan taruhan sportbook, setiap pertandingan sepak bola yang dilangsungkan dapat dijadikan sebagai tempat bagi seluruh masyarakat Indonesia untuk melakukan taruhan dengan menggunakan uang asli. permainan taruhan bola online dapat dilakukan dengan bebas sesuai dengan pertandingan yang berlangsung dan juga team sepak bola yang disenangi untuk memperoleh kemenangan dan kepuasan dari setiap taruhan sportbook di situs Emas69.

Continue Reading

Labari

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Published

on

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi - TUC/NLC

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

Gamayyar ƙungiyar ƙwadagon Najeriya ta ce tayin Naira 70,000 da shugaba Tinubu ya yi a matsayin mafi ƙarancin albashi da babu ne gara ba daɗi.

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

KU KUMA KARANTA:NLC ta ƙira taron gaggawa bayan gwamnati ta jingine batun ƙarin albashi

Wannan dai na nuna a karo na farko tun neman mafi ƙarancin albashi mafi yawa a Najeriya Naira 615,00 ya sauƙo Naira 477,000, shugabannin ƙwadagon sun maida wuƙa kube ta hanyar yin na’am da tayin da gwamnati ta yi.

Bayan kammala ganawa babban sakataren ƙungiyar ƙwadagon ta TUC Komared Nuhu Toro ya ce sun amshi tayin da gabatar da hakan gaban majalisun su “mun kai majalisar ƙolinmu, tayin da shugaban ƙasa ya bayar sun kuma lamunta da shi da fatan Allah ya sa albarka…ai Naira 70,000 ɗin nan da babu ne gara ba daɗi.

Tuni ma’aikata na sassa daban-daban suka fara maida martani da mafi sauƙin shi ne na nuna ba abun da suka iya don jagorori sun miƙa wuya.

Malamin makaranta Muhammad Bello Nawaila ya ce ba wani tasiri da mafi ƙarancin albashin zai yi in an duba ɗan karen tsadar rayuwa.

Ita ma ƙungiyar gamayyar ƙungiyoyin arewa CNG da ke marawa gwagwarmayar ma’aikatan baya ta ce matuƙar shugaba Tinubu bai yi garambawul ga lamuran walwalar ma’aikata da matasa ba, za a iya fuskantar ƙalubale “mu na gujewa guguwar juyin juya hali a Najeriya matuƙar gwamnati ba ta farka ta ɗauki matakan gaskiya na zahiri ba.”

Alamu na nuna batun neman ƙarin mafi ƙarancin albashi zai dakata zuwa wani lokaci don ‘yan ƙwadagon sun yaɗa gora sai komawa kan batun tsadar rayuwa.

Continue Reading

Kasashen Waje

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Published

on

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump - Pennsylvania

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Sakataren tsaron cikin gida na Amurka, Alejandro N. Mayorkas ya fitar da wata sanarwa game da harbin da aka yi a wurin yaƙin neman zaɓen tsohon Shugaban ƙasar Donald Trump a jihar Pennsylvania da safiyar yau.

A cikin sanarwar, Sakataren tsaron cikin gidan na Amurka Mayorkas ya bayyana cewa, “Ni da Daraktan ma’aikatar leƙen asiri Cheatle mun yi wa Shugaba Biden bayani game da harbin da aka yi yau a Pennsylvania. Ma’aikatar tsaron cikin gida (DHS) da Ma’aikatar Leƙen Asiri suna aiki tare da abokan aikinmu, masu kula da kiyaye doka don gudanar da bincike kan harbin.

KU KUMA KARANTA:Kotun Ƙolin Amurka za ta yanke hukunci kan takarar Donald Trump

Sanarwar ta ƙara da cewa, “Muna Allah wadai da wannan tashin hankalin da kakkausar murya tare da yaba wa hukumar leƙen asiri bisa matakin gaggawar da ta ɗauka a yau. Muna tare da Shugaba Biden, tsohon Shugaba Trump, da yaƙin neman zaɓensu, kuma muna ɗaukar duk matakin da ya dace don tabbatar da tsaronsu. Kula da tsaron ’yan takarar Shugaban ƙasa da kuma taron yaƙin neman zaɓensu na ɗaya daga cikin muhimman abubuwan da sashenmu ke ba da fifik

Tun farko Mai magana da yawun ma’aikatar leƙen asiri Anthony Guglielmi ya fitar da sanarwa a dandalin sada zumunta X, cewa, “Ma’aikatar leken asiri ta aiwatar da matakan kariya kuma tsohon Shugaban ƙasar yana cikin ƙoshin lafiya. Yanzu haka Hukumar tana gudanar da bincike, ta kuma sanar da Hukumar Binciken manyan laifuka ta FBI.”

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like