Connect with us

Siyasa

Na Samu Amincewar Kansiloli Bisa Kudirin Tsayawa Takarar Sanata A Kaduna – Hajiya Rabi Salisu

Published

on

Daga; USMAN NASIDI, Kaduna.

YAR takarar Kujerar Sanatan Shiyyar Kaduna ta tsakiya, Hajiya Rabi Salisu Ibrahim, Garkuwan Marayun Zazzau, ta bayyana cewa ta samu nasarar samun amincewar Kungiyar Kansilolin Jam’iyyar APC mai mulki a bisa kudirinta na tsayawa takarar Sanata a zaben fidda gwani da na kasa baki daya.

A zantawarta da manema labarai a garin Kaduna, Hajiya Rabi Salisu, ta kara da cewa babu gudu babu ja da baya a bisa wannan kudirin nata wanda ganin irin nasarar da ta ke samu tun a yanzu tare da samun goyon bayan wasu daga cikin iyayen Jam’iyyar musamman Kansiloli wanda su ne jagorori mafi kusa da al’umma, hakan ya kara mata kwarin gwiwa.

Acewarta, wannan shi ne karo na biyu da ta ke tsayawa takara kuma kamar yadda ta tsaya takarar tsayin daka a wancan lokacin zaben ba tare girgiza ba, haka a yanzu ma wannan karon za ta yi iya bakin kokarinta na ganin cewa hakarta ya cimma domin har sai ta ga abin da ya turewa buzu nadi ba tare da gajiyawa ba.

Ta ce “ina matukar bayyana farin cikina bisa ganin irin yadda ‘ya’yan Jam’iyyar suka nuna mun goyon bayansu a kan kudirina na tsayawa takara, domin na lura ma wasu sun nuna bacin ransu a kan jin cewa ance na janye daga takarar wanda hakan ba gaskiya ba ne, domin ina nan a kan bakata, kuma hakan yasa na riga kowa ma sayan Fom din bayyana sha’awa da ra’ayin tsaywa takarar.”

“Jam’iyyar APC a karkashin Jagorancin Malam Nasir El-Rufa’i na matukar ba da girma da girmama mata a karkashin mulkinsu wanda hakan ya sanya aka saka mata da dama a cikin tafiyar da al’amura a Gwamnatin Jihar, kuma muna alfari da ganin irin hakan ba tare da nuna banbancin Jinsi al’umma yayin gudanar da harkokin siyasar Jihar Kaduna ba.”

“Alal-hakikanin gaskiya, bayan kammala bayyana kudirorina a taron ganawa da wakilan Jam’iyyar wanda mataimakin Shugaban Kasa, kuma dan takarar Kujerar shugaban kasa, Farfesa Yemi Osinbajo ya yi, hakan ya kara harzuka ‘ya’yan Jam’iyyar ta mu na ganin cewa sun mara mun baya saboda jin irin kwarewata da Gwagwarmayar da nayi a fagen Siyasa da kuma cikin al’umma.”

“Ni mace ce wacce nake da kwarewa a fannin sasanci rikece-rikece da samar da zaman lafiya wanda hakan zai ba ni wata damar ganin cewa na tabbatar da samar da zaman lafiya da tsaro a yankin Shiyyar da nake wakilta, tare da kawar da duk wata matsala na rashin tsaro da al’ummar wannan yankin suke fuskanta, kana na tabbatar da samun zaman lafiya da kwanciyar hankali a Shiyyar.

“Kuma daga cikin kudirorina akwai batun inganta rayuwar mata da yara ta yadda zasu rika dogaro da Kansu, hakazalika da tallafawa al’umma masu fama da wata nakasa na musamman domin su ma suna da hakki da bukatar sumun Ingantacciyar rayuwa, don haka nake ganin nafi kowa cancanta.”

“Sannan game da zancen da ake na cewa ko Gwamnan Jihar ya tsayar da wani dan takara, wannan batu ne kawai domin babu wani dan takarar da Malam Nasir El-Rufa’i ya tsayar a matsayin zababbe a karkashin Jam’iyyar, illa kawai lokaci ne zai tabbatar mana da hakan, kuma ina fata da addu’ar Allah Yasa ni ce zababbiyar yar takarar da Jam’iyyar za ta tsayar. ” Inji Hajiya Rabi

A karshe, Yar takarar Sanatan ta Shiyyar Kaduna ta tsakiya, Hajiya Rabi Garkuwan Marayun Zazzau, ta roki yan Jam’iyyar ta APC da su tabbatar da sun ba mata duk wata damar da ake bukata a cikin wannan tafiyar tasu wanda hakan ne zai tabbatar da adalci a cikin al’umma da yanayin gudanar da harkokin siyasar Jihar.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Siyasa

APC ta dakatar da ɗan Majalisa kan cin amana a Zamfara

Published

on

APC ta dakatar da ɗan Majalisa kan cin amana a Zamfara

Jam’iyyar APC reshen Jihar Zamfara ta dakatar da Ɗan Majalisar Wakilai, Aminu Jaji bisa wasu zarge-zargen da ake yi masa na cin amanar jam’iyyar.

Sakataren Yaɗa Labarai na Jam’iyyar APC na Jihar, Malam Yusuf Idris ne ya sanar da dakatarwar a wani taron manema labarai a Gusau a ranar Juma’a.

Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa, Jaji yana wakiltar mazaɓar Ƙaura-Namoda/Birnin-Magaji a Majalisar Wakilai a ƙarƙashin jam’iyyar APC.

Idris ya ce wasu zarge-zargen da ake yi wa Ɗan Majalisar sun haɗa da aikata rashin gaskiya da rashin zuwa tarurrukan jam’iyyar da kuma sauran ayyuka.

KU KUMA KARANTA: Kotun Najeriya ta bayar da umarnin dakatar da asusun banki fiye da dubu 1

Ya ce, matakin ya biyo bayan sanarwar dakatarwar da aka yi wa Jaji daga shugabannin jam’iyyar APC na mazaɓar Birnin-Magaji bisa zargin cin amanar jam’iyyar da dai sauran abubuwan da suka saɓa wa jam’iyyar.
Idris ya ce, “Kwamitin zartaswa na jam’iyyar APC na ƙaramar hukumar Birnin Magaji ne ya miƙa sanarwar dakatarwar zuwa hedikwatar jam’iyyar APC ta jihar.

Bayanai sun ce kwamitin zartaswar jam’iyyar APC na jihar ya gudanar da taron gaggawa a sakatariyar jam’iyyar da ke Gusau a ranar Juma’a 17 ga watan Mayu, 2024, inda aka gabatar da batun dakatar da Jaji ga ‘yan majalisar zartarwar jihar.

Continue Reading

Labarai

Tsohon gwamnan Katsina, Shema ya sauya sheƙa zuwa APC

Published

on

Tsohon gwamnan jihar Katsina, Ibrahim Shema, a hukumance ya koma jam’iyyar APC Mai mulki a jihar.

Shema, ya kasance gwamnan jihar a tsakanin shekarar 2007 zuwa 2015, a ƙarƙashin jam’iyyar PDP.

Tsohon gwamnan ya yi rajista ne a ofishin jam’iyyar na mazaɓar Shema, ƙaramar hukumar Dutsin-ma, inda shugaban jam’iyyar na jihar, Sani Aliyu-Daura ya ba shi katin zama ɗan jam’iyyar APC.

Lambar katin Shema ta zama ɗan jam’iyyar ita ce: 26551.

KU KUMA KARANTA:Gwamnatin Yobe za ta mayar da kwale-kwalen Dufuna mai shekaru 8,000 zuwa cibiyar yawon buɗe ido

Malam Aliyu-Daura ya yabawa Gwamna Dikko Raɗɗa da kuma tsohon gwamnan jihar Aminu Masari wanda ya gada, a bisa rawar da suka taka wajen ganin Shema ya sauya sheƙa.

Don haka ya tabbatar wa tsohon gwamnan cewa za a yi masa adalci kamar kowane ɗan jam’iyya.

Shugaban ma’aikata na Raɗɗa, Jabiru Abdullahi-Tasuri, shi ne ya miƙa katin zama ɗan jam’iyya ga Shema a madadin gwamnan a jiya Alhamis a Dutsin-ma.

Continue Reading

Labarai

Fusatattun matasa sun lakaɗawa kwamishina duka a wajen zaɓen fidda gwani

Published

on

Banji Ajaka, kwamishinan lafiya na jihar Ondo, ya gamu da fushin matasa a jiya Asabar yayin da ake gudanar da zaɓen fidda gwani na gwamna na jam’iyyar APC mai mulki a jihar.

Daily Trust ta gano cewa Dakta Ajaka, wanda ke Mazaɓar Ugbo 3, a ƙaramar hukumar, ana zarginsa da ɓoye takardar sakamakon zaɓen.

Shaidu sun tabbatar da faruwar lamarin a wata tattaunawa da suka yi da manema labarai, inda suka yi zargin cewa fusatattaun matasan ‘ya’yan jam’iyyar APC ne da ke adawa da tsarin da aka bi wajen gudanar da zaɓen.

Ɗaya daga cikin waɗanda suka shaida lamarin, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya bayyana cewa rikicin ya faro ne lokacin da ‘yan ɗaya ɓangaren na jam’iyyar suka buƙaci ganin takardar sakamakon zaɓen na fidda gwani.

KU KUMA KARANTA:An yi jana’izar tsohon gwamnan Ondo, Rotimi Akeredolu

“Sun fusata ne suka buƙaci jami’in zaɓe ya ba su takardar sakamakon zaɓen sai kuwa ya ce ta na wajen Ajaka.

“Don haka suka yi masa duka a wurin, inda kuma garinsu ne. Jama’a sun fusata sosai da lamarin, inda rigimar ta ƙare a wajen.”

Da yake tabbatar da faruwar lamarin, Dakta Ajaka ya ce an zarge shi ne da riƙe takardar sakamakon zaɓen.

Ya yi bayanin cewa a lokacin da yake ƙoƙarin bayyana kansa, ’yan daban sun auka masa inda suka yi masa mugun duka.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like