Connect with us

Labari

Maniyyatan Aikin Umrah Sun Zargi Azman Air Da Zubar Da Su A Kano

Published

on

Daga; Rabo Haladu.

WASU maniyyata aikin Umrah sun zargi kamfanin sufurin jiragen sama na Azman Air da zubar da su a Kano, suna watangaririya bayan ya gaza kai su ƙasa mai tsarki.

Maniyyatan, waɗanda suka ce sun kai ɗaruruwa, sun koka kan rashin ba su ko da makwanci bayan sun baro gidajensu daga Jihohi daban-daban.

Wasu maniyyatan sun shaida cewa sun shiga mawuyacin hali bayan Azman Air ta zubar da su a Kano ba tare da yi musu bayani a kan tsaikon da aka samu na jigilarsu zuwa kasa mai tsarki ba.

Daya daga cikin fasinjojin, ya shaida cewa, kusan kwanansu biyu jibge a Kano, kuma akwai wadanda daga cikinsu suka je Kanon daga Jihohi kamar Sokoto da Kebbi da Zamfara da Borno har ma Abuja, babban birnin tarayya.

Yace “Da muka je Kano cikin dare mun zauna filin jirgin saman Kano har zuwa 11:30 na dare, ba wanda ya ce mana uffan, haka muka yi ta zaman jira har muka gaji, daga nan ne muka shiga gari muka nemo otel don mu kwanta.”

Fasinjan ya ce sun je ofishin Azman Air da ke Zaria Road sun tarar an kulle, haka suka kasance babu wanda ya ce musu komai har sun gaji da biyan kudin otel.

Sai dai mataimakin babban manajan kamfanin na Azman Air, Nuradden Aliyu, ya shaida cewa jinkirin da aka samu ya samu asali ne sanadin fashewar tayar jirginsu a makon da ya wuce a kasa mai tsarki lamarin da ya haddasa tashin wuta amma an yi nasarar kashe ta.

Yace wannan hatsari ne ya shafi lafiyar jirginsu na jigilar aikin Umrah ko da yake tuni aka kammala gyaransa a ranar Litinin 18 ga watan Afrilun, 2022.

Mataimakin babban manajan kamfanin na Azman Air, ya ce ana sa ran tasowar jirgin zuwa Najeriya don ci gaba da aikin jigilar a ranar Talata 19 ga watan Afrilun, 2022.

Ya ce sai da suka tuntubi wasu kamfanonin jiragen amma saboda yanayin da ake ciki na jigilar zuwa Umrah, ba su samu jirgin da zai taimaka musu ba, shi ya sa suka tsaya tsayin daka wajen ganin an gyara na su.

Nuradden Aliyu ya ce,” Duk wani matsayi da muke ciki mu kan sanar da fasinjoji cewa mun daga jirginsu kada suje filin jirgin sama.”

Ya ce an samu rashin fahimta tsakaninsu da maniyyatan, saboda shi aikin Umrah, kamfanonin da ke shirya tafiye-tafiye ne ke sayen tikitin tafiya, su kuma a nasu bangaren sun sanar da duk wadanda suka kamata.

Fasinjojin da aka ta tattaunawa da su, sun bukaci kamfanin Azman Air da ya biya su kudaden da suka kashe kamar na wajen kwana da suka kama a Kano tare da sauran wahalhalun da ya janyo musu.

To amma kamfanin ya ce ba bu wani hakkin fasinja da zai salwanta a hannunsa.

1 Comment

1 Comment

  1. Pingback: Katsina ta fara rijistar maniyyata hajji, ta soma ƙarban naira miliyan daya da rabi kuɗin ajiya. | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labari

EMAS69 • LINK ALTERNATIF SPORTBOOK SBOBET

Published

on

By

Emas69 adalah bandar taruhan sportbook sbobet terlengkap yang saat ini sangat dikenal seluruh masyarakat Indonesia dengan melalui link alternatif Emas69. Pada permainan taruhan sportbook, setiap pertandingan sepak bola yang dilangsungkan dapat dijadikan sebagai tempat bagi seluruh masyarakat Indonesia untuk melakukan taruhan dengan menggunakan uang asli. permainan taruhan bola online dapat dilakukan dengan bebas sesuai dengan pertandingan yang berlangsung dan juga team sepak bola yang disenangi untuk memperoleh kemenangan dan kepuasan dari setiap taruhan sportbook di situs Emas69.

Continue Reading

Labari

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Published

on

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi - TUC/NLC

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

Gamayyar ƙungiyar ƙwadagon Najeriya ta ce tayin Naira 70,000 da shugaba Tinubu ya yi a matsayin mafi ƙarancin albashi da babu ne gara ba daɗi.

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

KU KUMA KARANTA:NLC ta ƙira taron gaggawa bayan gwamnati ta jingine batun ƙarin albashi

Wannan dai na nuna a karo na farko tun neman mafi ƙarancin albashi mafi yawa a Najeriya Naira 615,00 ya sauƙo Naira 477,000, shugabannin ƙwadagon sun maida wuƙa kube ta hanyar yin na’am da tayin da gwamnati ta yi.

Bayan kammala ganawa babban sakataren ƙungiyar ƙwadagon ta TUC Komared Nuhu Toro ya ce sun amshi tayin da gabatar da hakan gaban majalisun su “mun kai majalisar ƙolinmu, tayin da shugaban ƙasa ya bayar sun kuma lamunta da shi da fatan Allah ya sa albarka…ai Naira 70,000 ɗin nan da babu ne gara ba daɗi.

Tuni ma’aikata na sassa daban-daban suka fara maida martani da mafi sauƙin shi ne na nuna ba abun da suka iya don jagorori sun miƙa wuya.

Malamin makaranta Muhammad Bello Nawaila ya ce ba wani tasiri da mafi ƙarancin albashin zai yi in an duba ɗan karen tsadar rayuwa.

Ita ma ƙungiyar gamayyar ƙungiyoyin arewa CNG da ke marawa gwagwarmayar ma’aikatan baya ta ce matuƙar shugaba Tinubu bai yi garambawul ga lamuran walwalar ma’aikata da matasa ba, za a iya fuskantar ƙalubale “mu na gujewa guguwar juyin juya hali a Najeriya matuƙar gwamnati ba ta farka ta ɗauki matakan gaskiya na zahiri ba.”

Alamu na nuna batun neman ƙarin mafi ƙarancin albashi zai dakata zuwa wani lokaci don ‘yan ƙwadagon sun yaɗa gora sai komawa kan batun tsadar rayuwa.

Continue Reading

Kasashen Waje

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Published

on

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump - Pennsylvania

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Sakataren tsaron cikin gida na Amurka, Alejandro N. Mayorkas ya fitar da wata sanarwa game da harbin da aka yi a wurin yaƙin neman zaɓen tsohon Shugaban ƙasar Donald Trump a jihar Pennsylvania da safiyar yau.

A cikin sanarwar, Sakataren tsaron cikin gidan na Amurka Mayorkas ya bayyana cewa, “Ni da Daraktan ma’aikatar leƙen asiri Cheatle mun yi wa Shugaba Biden bayani game da harbin da aka yi yau a Pennsylvania. Ma’aikatar tsaron cikin gida (DHS) da Ma’aikatar Leƙen Asiri suna aiki tare da abokan aikinmu, masu kula da kiyaye doka don gudanar da bincike kan harbin.

KU KUMA KARANTA:Kotun Ƙolin Amurka za ta yanke hukunci kan takarar Donald Trump

Sanarwar ta ƙara da cewa, “Muna Allah wadai da wannan tashin hankalin da kakkausar murya tare da yaba wa hukumar leƙen asiri bisa matakin gaggawar da ta ɗauka a yau. Muna tare da Shugaba Biden, tsohon Shugaba Trump, da yaƙin neman zaɓensu, kuma muna ɗaukar duk matakin da ya dace don tabbatar da tsaronsu. Kula da tsaron ’yan takarar Shugaban ƙasa da kuma taron yaƙin neman zaɓensu na ɗaya daga cikin muhimman abubuwan da sashenmu ke ba da fifik

Tun farko Mai magana da yawun ma’aikatar leƙen asiri Anthony Guglielmi ya fitar da sanarwa a dandalin sada zumunta X, cewa, “Ma’aikatar leken asiri ta aiwatar da matakan kariya kuma tsohon Shugaban ƙasar yana cikin ƙoshin lafiya. Yanzu haka Hukumar tana gudanar da bincike, ta kuma sanar da Hukumar Binciken manyan laifuka ta FBI.”

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like