Connect with us

Wasanni

Makon Wasanni: SWAN Kaduna, Ta Karrama Kwamishinan Wasanni, Shugaban AYCF Da Sauran Su

Published

on

Daga; USMAN NASIDI, Kaduna.

A BISA Kokarin da suke na ganin an inganta sashen wasannin motsa jiki a Kasar Najeriya, Kungiyar Marubutan Wasanni ta Kasa (SWAN), reshen Jihar Kaduna ta gudanar da makon wasannin tare da karrama wasu al’umma da lambar yabo na girmamawa ciki har da Kwamishinan Wasanni na Jihar Kaduna Honarabul Idris Nyam da Shugaban Kungiyar Tuntuba Ta Matasan Arewa (AYCF) Kwamared Shettima Yarima.

Taron karramawar da bada lambar yabon wanda ya gudana a dakin taro na gidan Sardauna dake Jihar Kaduna a ranar Asabar din daya gabata, ya biyo bayan kammala shirin makon wasannin motsa jikin da aka gudanar tun daga ranar 20 ga watan Maris izuwa ranar 25 ga watan Maris ta shekarar 2022.

An shirya wadannan wasannin ne da zummar kara inganta sashen wasannin da kulla kyakkyawar alaka a tsakanin al’umma wadanda suka hada da yin wasanni tsakanin makarantu, ma’aikatun Kafafen Yada Labarai, kana da kokarin nuna bajintar da ke tsakanin kowace al’umma kamar yadda ma’aikatan Gidan Talabijin na DITV suka lashe gasar kwallon Kafa na Kafafen Yada Labarai.

Da yake jawabi a wajen taron, Honarabul Idris Nyam, ya bayyana farin cikinsa bisa irin Kokarin da Kungiyar ta ke yi na ganin cewa ta samar da kyakkyawar yanayi da fahimta a tsakanin al’ummar Jihar ta hanyar ware mako guda na shirya wasannin motsa jiki daban-daban.

Kwamishinan Wasannin, ya kara da cewa ko shakka babu ma’aikatar wasannin ta Jihar Kaduna karkashin Jagorancin shi a shirye ta ke domin ta marawa duk wata Kungiyar wasanni baya domin tabbatar da an samu duk wata nasarar da ake bukata, wanda hakan yasa karsashin hubbasan da Kungiyar Marubutan Wasanni ta (SWAN) ta ke yi yake matukar birge shi.

Ya ce “tun bayan dana kama aiki a karkashin wannan ma’aikata kuma na ci karo da Shugaban wannan Kungiyar ta (SWAN), na yi maka alkawarin za mu yi aiki tare kuma bayan hakan duk inda naje taro na kan ci karo da shi, wanda hakan ya sanya ya tabbatar mun da shi Jakadan ma’aikatar wasannin ta Jihar Kaduna amma a karkashin Kungiyar ta (SWAN).

A nashi jawabin, Shugaban Kungiyar Tuntuba Ta Matasan Arewa (AYCF), Kwamared Shettima Yarima, ya bayyana cewa wasannin motsa jiki wani abu ne wanda zai taimaka wajen inganta rayuwar al’umma musamman a mutane da shekarun suka dan ja baya bayan ga zaman ta wata hanya ta sada zumunta da kulla kyakkyawar mu’amala a tsakanin al’umma baki daya.

Acewar Shettima, wannan shi ne karo na farko da yake halartar wannan taron na Kungiyar (SWAN), amma ya yi alkawarin ci gaba halarta tare da tallafawa harkokin Kungiyar ta duk fuskar da ta dace, kana ya yaba da irin yunkurin da Kungiyar ta ke na ganin cewa ta hada kan al’umma baki daya musamman a Jihar ta Kaduna.

Hakazalika, wasu daga cikin manyan mutanen da aka karrama da lambar yabo na girmamawar a wajen taron a bisa irin kokarin da suke ba sashen wasannin, sun hada da Makarantar Kadwel, Alhaji Abdulfatai Aremu (Mayekun), Bishop Ademola Idowu Tinuoye, Honarabul Ibrahim Yusuf Zailani, Alhaji Shehu Aliyu ( Dan Malikin Kasar Hausa), da sauran wasu al’umma.

Ni ɗan jarida ne mai zaman kansa. Mawallafi kuma mai sharhi a lamarin yau da kullum.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Wasanni

Messi ya jagoranci Argentina zuwa wasan ƙarshe na Copa America

Published

on

Messi ya jagoranci Argentina zuwa wasan ƙarshe na Copa America

Messi ya jagoranci Argentina zuwa wasan ƙarshe na Copa America

Ɗan wasan gaba na Inter Miami Lionel Messi ya jagoranci ƙasarsa Argentina zuwa wasan ƙarshe na Copa America inda ta doke Canada da ci 2-0.

Messi mai shekaru 37 ya zura ƙwallo a minti shida da komawa daga hutun rabin lokaci.

Ɗan wasan Manchester City Julian Alvarez ne ya baiwa ƙasar wadda ke rike da kofin duniya damar samun wannan nasara bayan ƙwallon kusa da Rodrigo de Paul na Atletico Madrid ya buga.

Wannan dai shi ne karo na shida a karawa takwas da Argentina wacce ta lashe kofin Copa America sau 15 ta kai matakin wasan ƙarshe.

Wasan ƙarshen da Argentina za ta kara da Uruguay ko Colombia, zai kasance wasa na ƙarshe da Angel di Maria zai buga wa ƙasar kafin ya yi ritaya daga buga wasa sannan kuma akwai shakku kan makomar Messi.

”Za mu ji daɗin yanayin da muke ciki a matsayinmu na ƙasa kuma ƙungiya. Ba abu ba ne mai sauƙi kasancewarmu a matakin wasan ƙarshe domin sake fafatawa don zama zakara,” kamar yadda Messi ya shaida wa kafar TYC Sports.

Manajan Argentina Lionel Scaloni ya ce zai yi aiki don shawo kan Di Maria da Messi su ci gaba da buga wasannin ƙasa da ƙasa.

KU KUMA KARANTA: Farin cikina ya dawo bayan komawa Inter Miami – Messi

“Yanayin Leo (Messi), yana kama da Angel,” in ji Scaloni.

”Dole ne mu bar shi ya yi abin da yake so, don ba za mu taɓa zama waɗanda za su rufe masa ƙofa ba, zai iya zama tare da tawagarmu har tsawon lokacin da yake so. kuma idan yana so ya yi ritaya kuma ya dawo ya kasancewa tare da mu, za mu yi farin cikin hakan.”

Jacob Shaffelburg, ɗan wasan ƙungiyar MLS Nashville ne ya ɓarar da mafi kyawun damar da Canada ta samu a farkon wasanta da Argentina.

Kasar Canada wacce ke matsayi na 48 a duniya, ta yi waje da ƙwallon da Alvarez ya zura a ragarta kana ya bai wa Argentina damar samun gurbi na gaba a wasan.

Duk da shan kayen Canada, tawagar ta yi rawar gani fiye da yadda ake zato a fafatawar da suka yi a gasar Copa America.

A ranar Lahadi ne tawagar Jesse Marsch wacce za ta ɗauki nauyin gasar cin kofin duniya ta 2026 tare da Mexico da Amurka, za su kara da wadanda suka sha kashi daga sauran wasan kusa da na ƙarshe a wasan neman matsayi na uku.

Continue Reading

Nishadi

Sadiya Haruna ta sake aure karo na 10

Published

on

Sadiya Haruna ta sake aure karo na 10

Sadiya Haruna ta sake aure karo na 10

Jarumar TikTok, Sayyada Sadiya Haruna ta sake amarcewa a ranar Juma’a watanni kaɗan da mutuwar aurenta da jarumin TikTok Al Ameen G-Fresh.

A wani kati da ta wallafa a shafinta na Instagram, Sadiya ta bayyana sunan angon nata a matsayin Hon. Babagana Audu Grema.

An daura auren ne da misalin ƙarfe ɗaya bayan sallar Juma’a kamar yadda katin ya nuna a birnin Maiduguri da ke jihar Borno a arewa maso gabashin Najeriya.

KU KUMA KARANTA:Gwamnatin tarayya ta bai wa Rahama Sadau muƙami

Auren na zuwa mako guda bayan da jarumar ta TikTok ta bayyana a shirin tattaunawa na jarumar Kannywood Hadiza Gabon “Gabon Talk Show” inda Sadiya ta caccaki G-Fresh tare da bayyana matsalolin da suka kai ga mutuwar aurenta da shi.

Auren har ila yau na zuwa ne kwana guda bayan da shirin na Gabon ya watsa tattaunawar mayar da martani da G-Fresh inda shi ma ya yi ta sukar tsohuwar matar tasa – mafi aksarin lokuta a kaikaice.

Continue Reading

Kasashen Waje

COPA America: Panama ta yi nasara kan Amurka

Published

on

COPA America: Panama ta yi nasara kan Amurka

COPA America: Panama ta yi nasara kan Amurka

Hukumar ƙwallon ƙafa ta Amurka ta yi Allah wadai da kalaman nuna wariyar launin fata ga ‘yan wasanta a ranar Alhamis, bayan da Panama ta yi nasara a kan Amurka da ci 2-1 a gasar cin kofin Copa America.

A wani saƙo da ta wallafa a shafin X, hukumar ƙwallon ƙafa ta Amurka ta ce “Babu shakka, babu wuri a cikin wasa na irin wannan halayya ta nuna ƙiyayya da wariya.”

Sanarwar ta ƙara da cewa “Waɗannan ayyukan ba kawai ba za’a amince da su ba ne, amma kuma sun saɓa wa kimar mutuntawa da haɗa kai da muka ɗauka a matsayin hukuma.”

KU KUMA KARANTA:Manchester City ta lashe Firimiyar Ingila sau huɗu a jere

Timothy Weah, wanda baƙar fata ne, yana ɗaya daga cikin ‘yan wasan da aka ci zarafin su. An bai wa ɗan wasan gaba na Amurka jan kati kai tsaye a minti na 18 da fara wasa, saboda hannu da ya sa ya bugi ɗan wasan Panama a bayan kan sa a lokacin da ƙwallon ta fita wajen filin wasa.

Ɗan wasan Amurka Folarin Balogun ya zura ƙwallo a minti na 22 da fara wasan bayan an bai wa Weah jan kati kafin ɗan wasan Panama Blackman ya farke a minti na 26.

Fajardo ya zura ƙwallo da ta bai wa Panama nasara da ci 2-1 a minti na 83.

Weah ya fitar da wata sanarwa ta kafafan sada zumunta, inda ya bayar da haƙuri tare da neman gafarar waɗanda ya ɓata wa rai.

Yanzu haka dai Amurka, wacce ita ce ke karɓar baƙuncin gasar cin kofin na Copa America, muddin tana son zuwa zagaye na gaba to dole ne ta yi nasara a wasanta da Uruguay da zura ƙwallaye wanda ko da Panama ta yi nasara kan Bolivia za ta samu tsallake wa.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like