Connect with us

Labari

Hukumar Kula Da Yan Gudun Hijira Ta Kasa Za Ta Horas Da Mutane 10,000

Published

on

Daga; MUSTAPHA IMRANA ABDULLAHI.

HUKUMAR kula da yan gudun hijira a tarayyar Najeriya ta bayyana cewa za ta horas da mutane yan gudun hijira na cikin gida Dubu goma (10,000) tare da hadin Gwiwar hukumar da ke Koyar da kimiyyar sarrafa bayanai ta kasa wato (NITDA) a Abuja.

Za a fara ne da mutane dari biyu a da za su halarci horon a bangaren kimiyyar zamani ta yanar Gizo, za kuma a ba su Kwamfutar hannu domin kara inganta basira da ilimin da suka samu.

Da yake gabatar da bayani, Kwamishinan hukumar kula da yan gudun hijirar wadan da aka tsugunnar, Honarabul Imaan Suleiman Ibrahim cewa ta yi tsarin horaswar zai taimaka wajen kara Sanya su hulda a cikin al’umma, ta yadda za su ci gaba da gudanar da al’amuran rayuwa kamar kowa.

A cikin wata takardar da sashen yada bayanai na hukumar ya fitar ya ce babban dalilin da ya sa za a koyawa yan gudun hijirar wannan aikin yin amfani da yanar Gizo shi ne domin su samu dama kamar sauran jama’a na jerawa da zamani kuma ya taimaka masu ta fuskar dogaro da kansu har wasu ma su ci moriyar abin daga gare su kuma su fita daga cikin matsayin da suke ciki a halin yanzu.

Hajiya Suleiman Ibrahim ta kara da cewa hukumar za ta ci gaba da aikin bunkasa ayyukan da za su inganta harkokin dogaro da kai musamman daga bangaren yan gudun hijira da komai zai dace da kokarin Gwamnatin shugaba Muhammadu Buhari da sauran shirye shiryen bunkasa tattalin arzikin kasa musamman ga marasa karfi a cikin al’umma.

Sai ta godewa Darakta Janar na hukumar NITDA Inuwa Kashifu Abdullahi da yake kokarin fadada ayyukan hukumarsa domin horas da wadannan mutane yan gudun hijira.

A nasa jawabin Abdullahi cewa ya yi hukumarsa an Dora mata alhakin kokarin bunkasa fasahar sadarwar zamani domin samar da bayanai a Najerita baki daya.

Da kuma dokar da ta ba su damar samar da tsarin shiryawa,bincike, binkasawa da kuma kara ingantawa a dukkan lamuran baki daya da ya hada da yin aikin hadin Gwiwa Gwiwa sauran hukumomi wajen aikin horaswa da nufin kara bunkasa ayyukan ma’aikatansu.

A dai kokarin samun ci gaban rayuwa an yaba wa hukumar yan gudun hijirar saboda aikin horas da mutane Hamsin (50) a unguwar Jabi cikin babban birnin tarayya Abuja.

Babban aikin horaswar zai fara ne da aikin koyawa wasu aikin yin takalma, Walda,sana’ar Tela,Aikin Girke – Girke, aikin sarrafa bidiyo, aikin gyaran gashi,kirkirar dandalin shafukan tamar Gizo, sana’ar Aski da ba su kayan fara aiki bayan kammala samun horon.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labari

EMAS69 • LINK ALTERNATIF SPORTBOOK SBOBET

Published

on

By

Emas69 adalah bandar taruhan sportbook sbobet terlengkap yang saat ini sangat dikenal seluruh masyarakat Indonesia dengan melalui link alternatif Emas69. Pada permainan taruhan sportbook, setiap pertandingan sepak bola yang dilangsungkan dapat dijadikan sebagai tempat bagi seluruh masyarakat Indonesia untuk melakukan taruhan dengan menggunakan uang asli. permainan taruhan bola online dapat dilakukan dengan bebas sesuai dengan pertandingan yang berlangsung dan juga team sepak bola yang disenangi untuk memperoleh kemenangan dan kepuasan dari setiap taruhan sportbook di situs Emas69.

Continue Reading

Labari

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Published

on

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi - TUC/NLC

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

Gamayyar ƙungiyar ƙwadagon Najeriya ta ce tayin Naira 70,000 da shugaba Tinubu ya yi a matsayin mafi ƙarancin albashi da babu ne gara ba daɗi.

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

KU KUMA KARANTA:NLC ta ƙira taron gaggawa bayan gwamnati ta jingine batun ƙarin albashi

Wannan dai na nuna a karo na farko tun neman mafi ƙarancin albashi mafi yawa a Najeriya Naira 615,00 ya sauƙo Naira 477,000, shugabannin ƙwadagon sun maida wuƙa kube ta hanyar yin na’am da tayin da gwamnati ta yi.

Bayan kammala ganawa babban sakataren ƙungiyar ƙwadagon ta TUC Komared Nuhu Toro ya ce sun amshi tayin da gabatar da hakan gaban majalisun su “mun kai majalisar ƙolinmu, tayin da shugaban ƙasa ya bayar sun kuma lamunta da shi da fatan Allah ya sa albarka…ai Naira 70,000 ɗin nan da babu ne gara ba daɗi.

Tuni ma’aikata na sassa daban-daban suka fara maida martani da mafi sauƙin shi ne na nuna ba abun da suka iya don jagorori sun miƙa wuya.

Malamin makaranta Muhammad Bello Nawaila ya ce ba wani tasiri da mafi ƙarancin albashin zai yi in an duba ɗan karen tsadar rayuwa.

Ita ma ƙungiyar gamayyar ƙungiyoyin arewa CNG da ke marawa gwagwarmayar ma’aikatan baya ta ce matuƙar shugaba Tinubu bai yi garambawul ga lamuran walwalar ma’aikata da matasa ba, za a iya fuskantar ƙalubale “mu na gujewa guguwar juyin juya hali a Najeriya matuƙar gwamnati ba ta farka ta ɗauki matakan gaskiya na zahiri ba.”

Alamu na nuna batun neman ƙarin mafi ƙarancin albashi zai dakata zuwa wani lokaci don ‘yan ƙwadagon sun yaɗa gora sai komawa kan batun tsadar rayuwa.

Continue Reading

Kasashen Waje

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Published

on

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump - Pennsylvania

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Sakataren tsaron cikin gida na Amurka, Alejandro N. Mayorkas ya fitar da wata sanarwa game da harbin da aka yi a wurin yaƙin neman zaɓen tsohon Shugaban ƙasar Donald Trump a jihar Pennsylvania da safiyar yau.

A cikin sanarwar, Sakataren tsaron cikin gidan na Amurka Mayorkas ya bayyana cewa, “Ni da Daraktan ma’aikatar leƙen asiri Cheatle mun yi wa Shugaba Biden bayani game da harbin da aka yi yau a Pennsylvania. Ma’aikatar tsaron cikin gida (DHS) da Ma’aikatar Leƙen Asiri suna aiki tare da abokan aikinmu, masu kula da kiyaye doka don gudanar da bincike kan harbin.

KU KUMA KARANTA:Kotun Ƙolin Amurka za ta yanke hukunci kan takarar Donald Trump

Sanarwar ta ƙara da cewa, “Muna Allah wadai da wannan tashin hankalin da kakkausar murya tare da yaba wa hukumar leƙen asiri bisa matakin gaggawar da ta ɗauka a yau. Muna tare da Shugaba Biden, tsohon Shugaba Trump, da yaƙin neman zaɓensu, kuma muna ɗaukar duk matakin da ya dace don tabbatar da tsaronsu. Kula da tsaron ’yan takarar Shugaban ƙasa da kuma taron yaƙin neman zaɓensu na ɗaya daga cikin muhimman abubuwan da sashenmu ke ba da fifik

Tun farko Mai magana da yawun ma’aikatar leƙen asiri Anthony Guglielmi ya fitar da sanarwa a dandalin sada zumunta X, cewa, “Ma’aikatar leken asiri ta aiwatar da matakan kariya kuma tsohon Shugaban ƙasar yana cikin ƙoshin lafiya. Yanzu haka Hukumar tana gudanar da bincike, ta kuma sanar da Hukumar Binciken manyan laifuka ta FBI.”

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like