Connect with us

Allah Ɗaya Gari Bam Bam

Habasha, tsarin kalandar su, da sauran al’adunsu na ban mamaki

Published

on

Yan Ethiopia na fara sabuwar shekarar su da cin abinci tare da iyalai daban-daban a lokaci guda, duk da matsananciyar rayuwar da ake fama da ita da tashin farashin kaya da yunwa da ta mamaye yankin arewacin Ƙasar.

  1. Wata 13 ne ke Yun shekara ɗaya

Ba wannan ba ma – kalandar ƙasar Habasha ta na bayan ta ƙasashen yamma da shekara Bakwai da wata Takwas, in da ranar 23 ga watan Satumbar 2022 ta zama farkon shekarar 2015 a ƙasar. Wannan ko ya biyo bayan ƙidayar shekarar haihuwar Annabi Isa da suke yi daban da na waɗannan ƙasashe.

Lokacin da Cocin Katolika ta sauya ƙirgenta a shekarar 500 AD (bayan wafatin Annabi Isa AS), amma a lokacin Cocin Katolika ta Habasha ba ta sauya tata kalandar ba. Don haka, shekarar ta faɗo a ranar 11 ga watan Satumba a kalandar ƙasashen Yamma, wannan daidai da lokacin bazara ke nan.

Yara a Habasha ba irin na ko ina ba ne, domin kuwa su da sun fara girma ake koya musu waƙe da za su riƙa tuna kwana nawa ne a kowanne wata. Abin ba shi da wuya sosai a Habasha; Wata 12 na farkon shekera duka su na da kwanaki 30, sai na 13 da ke yin kwana biyar ko shida, ya danganta da yanayi a shekarar.

Yadda ake duba lokaci shi ma na da bambanci – lokacin ana raba shi biyu ne, awa 12 da ke fara wa daga ƙarfe 6:00 wadda yake a matsayin maraice da kuma cikin dare, zuwa shidan safe.

2) Ita ce ƙasar Afrika tilo da ba a yi wa mulkin mallaka ba

Italiya ta so yi wa Habasha ko in ce Abyssinia kamar yadda ake kiranta a 1895 mulkin mallaka, lokacin da ƙasashen Turai ke ta hanƙoron kasafta ƙasashen nahiyar a tsakaninsu, sai dai mutanen Italiyan sun ƙare da jin kunyar gaza shiga ƙasar.

Italiya ta yi wa maƙociyar ƙasar Eritrea mulkin mallaka lokacin da wani kamfanin Italiyan ya sayi tashar jirgin ruwa da ke Assab.

Kuma an shiga ruɗani ne bayan mutuwar sarkin Habasha Yohannes IV a 1889, wadda ya ba su damar amfani da wani tudu da ke kusa da teku.

Shekaru kaɗan Italiya ta yi yunƙurin ƙara kutsawa Habasha, amma ta kwashi kashinta a hannu a yaƙin da aka kira da “Yaƙin Adwa.” Cikin ƴan sa’o’i aka murƙushe wasu manyan kwamandojin Italiya a ranar 1 ga watan Maris ɗin 1896 lokacin da mayaƙan sarki Menelik II suka afka musu.

An matsa wa Italiya ta sanya hannu kan wata yarjejeniya da za ta tabbatar da ƴancin kan Habasha, duk da dai bayan shekaru kusan Goma Shugaba Benito Mussolini ya yi watsi da ita, ya kuma mamaye ƙasar na kusan shekara Biyar. Ɗaya daga cikin waɗanda suka gajin Menelik, Sarki Haile Selassie ya ci gajiyar nasarar da ya samu a kan Italiya ta yadda ya ƙirƙiri ƙungiyar haɗin kan ƙasashen Afrika wadda a yanzu ake kiranta AU da ke da hedikwatarta a Addis-Ababa babban birnin Habasha.

Lokacin ƙaddamar da ƙungiyar a 1963 sarki Selassie ya ce “Yancin da muka samu ba shi da wata ma’ana har sai sauran ƙasashen Afrika sun samu ƴanci.” Lokacin da kuma mafi yawan ƙasashen nahiyar ba su samu yancin kai ba.

  1. Basarake Haile Selassie, wadda masu bin addinin Rastafarian ke bauta masa wannan ya faro ne lokacin da wani jagoran fafutukar yancin baƙar fata Marcus Garvey, ya yi bayani a 1920, wadda shi ne jagoran wata tafiya da aka yi wa take da “Mayar da baƙaƙen fata Afrika,” in da ya ce “Ku yi duba zuwa Afrika lokacin da za a naɗa wa wani sarki sarauta ranar yanci na kusa.”

Shekara 10 baya, lokacin da wani matashin mai shekara 38 Rastafari aka naɗa shi a matsayin Haile Selassie I, da yawa a Jamaica na kallon wannan tafiya kamar ta Annabta. A nan aka fara tafiyar Rastafari.

A nan Bob Marley, na ɗaya daga cikin mutanen suka riƙa yaɗa saƙon Rasta – a waƙoƙinsa.

Wannan fefen da Bob Marley ya yi, jaridar Time Magazine ta ayyana shi a matsayin fefen da ya fi ko wanne a a ƙarni na 20. wadda ya nuna buƙatar Rasta ta mayar da mutanen Afrika gida.

Waɗanda aka tilasta wa zuwa Turai lokacin mulkin mallaka
A yau masu bin addinin Rastafara ƙalilan ne ke rayuwa a wani yankin Habasha da ake kira Shashamene, mai nisan kilomita 225 daga kudancin Addis-Ababa, a wani lardi da Sarki Selassie ya bayar domin baƙaƙen fata da ke shirin dawowa daga ƙasashen yamma wadda ya goyi baya.

Sarki Selassie wadda mabiyin addinin Kirista ne ba mabiyin addinin Rasta ba ne, ya kuma jaddada cewa shi ma zai mutu, amma har yau masu bin addinin Rasta na kallonsa a matsayin “Zakin Judah.”

Wannan wata hujja ce a kan zargin cewa, abin bauta ne shi, wadda mabiya Rastafara da kuma ƴan Habasha suka yi amannar cewa, an yi bayaninsa a Injila Sarki Solomon.

4) Gidan akwatun alƙawari

A wajen da yawa daga cikin Habasha, akwai gidan wani akwati da suke da yaƙinin saƙon da za su yi amfani da shi ya na ciki.

Cocin Katolika da ke Habasha ta ce, wannan akwati na ƙarƙashin kulawa ta musamman a Cocin Lady Mary, in da ba a barin kowa ya shiga ya ganta.

A al’adance Cocin na da kayayyakin tarihin Sarauniya Sheba, wadda masu tarihi ke musanta samuwarta, amma dai ba ƴan Habasha ba ne da wannan aiki. Sun yi amannar cewa ta yi tafiya daga Aksum zuwa Birnin Ƙudus domin ta ziyarci Sarki Solomon da kuma ƙara sanin baiwar da yake da ita a shekara ta 950 kafin zuwan Annabi Isa AS.

Labarin tafiyarta da haɗuwarsu da Solomon ya na cikin Littafin Kebra Nagast – Littafin adabin Habasha da aka rubuta da yaren Ge’ez a ƙarni na 14.

An bayyana yadda Sarki Makeda da Sarauniya Sheba suka haifi ɗa, Menelik – da kuma yadda bayan shekaru ya tafi Birnin Ƙudus domin haɗuwa da mahaifinsa.

Solomon, ya so ya zauna tare da shi ya ci gaba da mulki bayan mutuwarsa, amma daga baya ya yarje masa ya koma gida, ya kuma tattara masa labaran Isra’ilawa – wadda aka sace na ainihin aka sauya shi da na bogi.

  1. Gidan musulman farko da ke wajen yankin larabawa

“Idan kuka je Absyssinia, za ku tarar da wani sarki da baya goyon bayan rashin gaskiya.” Annabi Muhammad SAW, Ya gaya wa sahabbansa lokacin da aka matsa masu a Makka, za su yi hijira a ƙarni na Bakwai, in da yanzu ake kira Saudiyya.

Wannan ya faru ne lokacin da Annabi SAW, Ya fara kiraye-kirayen zuwa ga Musulunci, wadda shugabannin da ba Musulmai ba na lokacin ke masa kallon wata barazana.

Bayan sun yi abin da ya ce, wasu daga cikin tsirarin Musulmai sun isa masarautar Aksum, wadda a baya ta haɗa da, Habasha ta yau da Eritrea, in da aka karɓe su hannu bibiyu ƙarƙashin wani sarkin Kirista na masarautar Amhara, wadda ake kira Nejjashi da Larabci.

In da Najjashi ya zauna nan ake kira Tigray a yau, nan ne waɗannan ƴan gudun hijirar suka zauna suka gina Masallacin da ake ganin ya fi kowane daɗewa a nahiyar Afrika.

A shekarar 2020 ne aka ruguza wannan Masallaci lokacin da ake rikicin yankin Tigray.

Musulmai da yawa sun yi amannar an binne Sahabbai da yawa a garin Nagesh. A tarihin Musulunci wannan tafiyar da sahabban suka yi zuwa Masarautar Aksum a matsayin hijirar farko a addinin.

A yau adadin Musulman da ke zaune a Habasha sun kai kashi 34 cikin 100 ko kuma sama da Musulmai miliyan 115 da ke zaune a ƙasar.

3 Comments

3 Comments

  1. Pingback: Wani mutum ya kashe zaki bayan sun shafe tsawon minti 90 suna kokawa | Neptune Prime Hausa

  2. Pingback: Francisco Domingo Joaquim ya fi kowa girman baki a duniya | Neptune Prime Hausa

  3. Pingback: Wani ɗan ƙasar Japan ya kashe dalar Amurka dubu 20 don a canza halittarsa zuwa ta kare | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Allah Ɗaya Gari Bam Bam

Na yi yunƙurin yin azumi irin na musulmai, na kusa mutuwa – Wata Kirista

Published

on

Wata matar aure mai suna Eniola Fagbemi Sisialagbo ta bayyana cewa ita Kirista ce, amma mijinta Musulmi ne, kuma tana sha’awar yadda musulmi ke azumi, domin kullum sai ta tashi lokacin sahur, ƙarfe 4:30am domin shirya wa mijin nata abincin da zai yi sahur, hakan ne ya sa ita ma wata rana ta ce za ta jaraba azumin.

Ta ce bayan ta yi sahur gari ya waye, “ƙarfe 10 na safe sai cikina ya fara amsawa, amma duk da haka na dage har zuwa ƙarfe 12 sai naga idanuna sun fara jujjuyawa, nan na ɗauki waya na ƙira mijina na sanar masa halin da nake ciki, ya ce na daure, ko da ƙarfe huɗu ta yi na suma sau biyu, sai ganin kai na na yi a asibitin SAANU da ke garin Makola a Ibadan, jihar Oyo, na rantse da Allah wannan azumi da Musulmi ke yi ba wasa ba ne, ina jinjinawa Musulmi masu Azumi.” In ji ta.

Me yasa kuke ganin ta ka sa yin azumin?

Continue Reading

Al'ajabi

Bishiyoyin da ke zubar da jini: Yadda kimiyya da gargajiya suka yarda su raba hanya

Published

on

Daga cikin abubuwa masu ban a’ajibi a hallittun tsirrai, shi ne wata bishiyar fure da aka bai wa sunan “Zuciya mai zubar da jini,” wadda ake amfani da kyawunta wajen bayyana yanayin halayyar ɗan’adam da ba a buƙata.

A yayin da wannan bishiya ba ta zubar da jini a zahiri, hotuna da bidiyo a faɗin duniya na nuna yadda wasu bishiyoyi suke fitar da wani jan ruwa kamar jini, abun da ke ci gaba da tayar da hazo kan fassararsa a gargajiyance da kimiyyance a tsakanin al’ummu.

A yankuna irin su Kudancin Amurka, ana kuskuren kallon wannan ruwa a matsayin jini, yayin da a Afirka, abin da aka fi imani da shi shi ne wai wasu mutanen ɓoye ne da ke rayuwa a cikin bishiyoyin ke fitar da jan ruwan.

A watan Oktoban 2017, masanin tsirrai ɗan ƙasar Faransa ya bayar da haske kan yadda Tepezcohuite ko “bishiya mai aman jini”, ta zama abar girmamawa a wajen jama’ar Mayas da ke kudanci Mexico zuwa Guatemala.

Wani bidiyo da aka yaɗa a yanar gizo ya tabbatar da wanzuwar irin waɗannan bishiyoyi masu zubar da ruwa kamar jini. Mene ne abin da ake muhawara a kai game da wannan jan ruwa da ke bulbulowa?

KU KUMA KARANTA: Abubuwan al’ajabi da ke tattare da dabbar ‘Batoyi’ (Hotuna)

Kimiyya ta yi watsi da wannan abi bisa cewa camfi ne kawai idan aka ce wai wannan ruwa d abishiyun ke fitarwa jini ne. Amma jama’ar Shaman da masu bin addinan gargajiya na yi wa wadannan bishiyu kallon masu tsarki.

Dr Djibril Diop, masanin muhalli kuma malami a Jami’ar Cheikh Anta Diop da ke Dakar babban birnin Senegal, ya bayyana cewa babu wata bishiya da ke aman jini ko take da wani ikon amfanarwa ko cutarwa saboda jan ruwan da take da fitarwa.

Ya nanata cewa wannan ruwa wani ɗanko ne ko ruwan cikin tsirrai danda ke taka muhimmiyar rawa wajen rayuwarsu.

Ɗankon cikin tsirrai wani ruwa ne da ke fita daga bishiya don tsaron kanta, inda ruwan cikin jijiyoyin bishiya kuma yake kasancewa fari, kuma yana fita da tsakanin gajye da reshe, wanda shi ke kai ruwa, gishiri, ko sukari ga tsirrai.

Dr Diop ya bayar da misali da bishiyar darbejiya a yankin Bandafassi take fitar da wani farin ruwa mai yawa saboda harin ciwon fungal.

“Mazauna yankin na fassara wannan da wani abin a’ajibi kan bishiyar, ba tare da sun san cewa yanayin bishiyar, yankin da take, ƙasar data fito daga ciki da kuma yanayin ciwon da za ta yi na taka rawa wajen fitar ruwan da kalarsa.

Masanin muhallin ya kuma yi nuni da cewa babu wata bishiya da ke da jini, a saboda haka a hankalce, ba za a taɓa tsammanin ta fitar da jini ba.

Ya bayar da misali da bishiyar da ake ƙira Socotra don nuni ga yadda ɗanko a reshan bishiya yake, tare da kalar jan da wasu ke tunanin ko jini ne.

Wannan bishiya da za ta iya tsayin har mita 20, na fitar da ruwa ja daya sanya har aka rubuta wasu makalolin kimiyya don bayyana ta a matsayin “bishiya mai aman jini”.

Wannan jan ruwa ya haɗa da sukari, ruwa da wasu sinadaran gina jiki, kuma a wasu al’adu ana amfani da shi wajen rini. Ana yawan alaƙanta wannan ruwa ja ga ƙarfin tace sinadarai da bishiya ke yi.

Baya ga amfani da su wajen yin rini, masana tsirrai irin su Dr Diop da masu maganin gargajiya irin su Romaric Moussounde Moussounda na da ra’ayin cewa wadannan bishiyoyi na yin magani.

Moussounda, wanda ke da fahimta kan bambance-bambancen dazukan Gabon, na da ra’ayin cewa halittu da yawa, ko nau’ikan bishiyoyi Pterocarpusda ke Afirka ko na Abitibi da ke Quebec, duk sun cancanci a yi musu kallon masu matsayi na musamman ko yin camfi game da su.

Moussounda ya na cewa “Waɗannan bishiyoyi kyauta ce daga Ubangiji da bai kamata su faɗa wani rukunin rashin tabbas ba.”

“Wannan ruwa da ke fitowa daga cikin waɗannan bishiyoyi na jini ba ne, amma kuma na da muhimmanci da matsayi irin na jini.”

Moussounda wanda ke cakuɗa gargajiyanci da zamananci a fannin kula da lafiyar zuciya da sauran ayyukan gaggawa na kula da lafiya, ya rawaito marubuci dan asalin Senegal Birago Diop, wanda a 1960 ya yi rubutu game da “Tsarkin wasu bishiyoyi”.

Moussounda ya ce “Ana yawan amfani da waɗannan bishiyu masu tsarki wajen bukukuwa da magani. Duk suna da wata alaƙa ruhaniyya ga ɗan adam.”

A yayin da masana tsirrai ke ta fashin baki kan waɗannan bishiyu masu aman jini, su kuma mabiya addinan gargajiya irin su Mayan da ke Mexico da ‘yan asalin Indiya na Barazil ko Kudancin Amurka na da ra’ayin lallai a kalli waɗannan bishiyoyi a matsayin masu tsarki ababan girmamawa.

Duk da waɗannan bambance-bambance na ra’ayi, akwai ijma’i tsakanin masana kan lallai a kare wadannan bishiyoyi, ko suna da tsarki ko babu, don kare muhalli.

Continue Reading

Allah Ɗaya Gari Bam Bam

Wani matashi ya auri mata bakwai rana ɗaya a Uganda

Published

on

Wani ɗan kasuwa, Ssaalongo Nsikonenne Habib Ssezzigu, ya auri mata bakwai a rana guda a ƙasar Uganda.

An yi bikin auren ne a ƙauyen Bugereka, a gundumar Mukono  ranar Lahadi, 10 ga Satumba, 2023.

Biyu daga cikin mata bakwai da ya aura ’yan’uwan juna ne.

An fara gudanar da aikin ne da misalin ƙarfe 8 na safe, inda aka kai Amaren ɗakin gyaran jiki domin yin salon gashi, kafin a sanya su a cikin motocin dakon kaya na Super Custom, ɗauke da faranti na musamman wanda ke ɗauke da sunayen kowace Amarya.

KU KUMA KARANTA: Mutumin da ya auri kada, ya ce zai riƙe ta cikin aminci babu cutarwa

Bayan sun yi musabaha na aure, Nsikonnene da matansa guda bakwai sun gudanar da gagarumin jerin gwano ƙarɓashin jagorancin masu tuƙa keke babura da ake ƙira “boda”, suka bi ta garuruwan Kalagi, Kasana, da Nakifuma, kafin su isa gidansu da ƙarfe shida na yamma.

An fara bikin ɗaurin auren ne da kaɗe-kaɗe a yayin da ma’auratan ke tafiya a cikin ayarin motoci, yayin da jama’a suka yi ɗafifi a bakin titi domin shaida bikin.

Wasu mutane sun ka sa gaskata cewa gaskiya ne wannan abu yana faruwa, wasu sun ce wannan shi ne karo na farko da za su halarci irin wannan taron ɗaurin aure.

Matan sun haɗa da Mariam, Madina, Aisha, Zainabu, Fatuma, Rashida, da Musanyusa, wacce ita ce matar Habib ta farko kuma tana tare da shi tsawon shekaru bakwai.

Haka Habib ya sayo sabbin motocin a matsayin kyauta ga kowane daga cikin matansa.

A wajen liyafar, an shirya kujerun angonta, kowane da sunayensu.

Nsikonnene a jawabinsa a wajen liyafar, ya yabawa matansa bisa yadda suke yi masa biyayya.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like