Connect with us

Ilimi

Gwamnan Kano ya biya wa ɗalibai 6,500 kuɗin JAMB ‘yan asalin jihar Kano

Published

on

Daga Idris Umar, Zariya

Gwamna Abba Kabir Yusuf na jihar Kano ya biya wa Ɗalibai maza da mata, da suka gama sakandire ‘yan asalin jihar Kano kuɗin jarabawar share fagen shiga Jami’a kimanin 6,500 don ci gaba da karatun su a kwalejoji da jami’o’i a ƙasar nan dama duniya gaba ɗaya.

Gwamnan wanda ya fara da godiya ga iyayen yara bisa jajircewar su wajen bawa yaran su tarbiyya da tsayawa don ci gaban su ta hanyar ilimi.

Mai girma Gwamna yace daga lokacin da aka zaɓi wannan gwamnati sun gudanar da ayyuka da dama ya zuwa yanzu, inda ya ce lokacin yaƙin neman zaɓe sun yi wa al’umma da dama alƙawarin farfaɗo da harkar ilimi idan an samu nasara.

“Ba na mantawa wata shida da suka wuce mun ƙirƙiro da ɗaukar nauyin yaran mu da sukayi ƙwazo tare da ɗaukar su da biya masu kuɗin makaranta da sauran abubuwan da ba’a rasa ba.”

“Samun labarin wasu ɗaliban da muka tura ƙasashen ƙetare ba su samu kuɗin su ba ta fuskan matsalar canjin dala, ba mu yi ƙasa a gwuiwa ba ko bacci sai da muka tabbatar ya zuwa yanzu a sallame su babu mai bin wani abu.

KU KUMA KARANTA: Gwamnan Kaduna zai ba da ilimi kyauta ga ɗaliban Kuriga

Gwamna Abba Kabir yace batun BESDA kuwa ya zuwa yanzu ya sa kwamiti da za su tantance su, wanda ya zuwa yanzu kuma an kammala tantance su, sai abin da ya yi saura.

”Kasancewar mun baiwa ilimi fifiko a jihar Kano ya sa wajen gabatar da kasafin kuɗin wannan shekara ya sa muka baiwa ilimi kaso mafi tsoka.”

Gwamnan ya kuma buƙaci Ɗalibai Maza da su ƙara ƙaimi wajen ganin sun samu dama kamar yadda mata suka yi ƙwazo don haka suma Maza ana buƙatar ƙara ƙaimin su.

Batun dawo da tsarin samar da kayan aiki kuwa gwamnan ya ba da umarnin ci gaba da samar da kayan aikin da suka haɗar da Tebura da kayan koyarwa da nan da bayan sallah za’a tabbatar da tura wa kowace makaranta a jihar Kano.

“Suma Malamai mun yi shirin ganin sun samu horo mai kyau tare da ba su haƙƙoƙinsu na alawus-alawus ɗin su da gwamnatin baya ba ta biya su ba.”

A jawabin sa mai girma kwamishinan ilimi na jihar Kano Hon Haruna Doguwa yace mai girma gwamna yana tuntuɓar sa a ko da yaushe yadda za’a tabbatar ɗaliban jihar Kano sun samu damar rubuta Jarabawar Jamb.

Doguwa ya kuma ce a lokuta da yawa yana mamakin yadda mai girma Gwamna ya ke fin sauran gwamnonin jihohin Najeriya ƙoƙari wajen gudanar da aiki tuƙuru.

Kwamishinan ya ce da irin aikin alherin da ya kema al’ummar jihar Kano zai ba shi damar yin aikin sa na tsawon shekaru takwas tare da wucewa mataki na gaba.

Sannan Haruna Umar Doguwa ya kuma ƙara da cewa a yanzu haka gwamnan Kano cikin ƙudurinsa na ciyar da ilimi gaba a kano ya ƙara wa ɗaliban makarantun kwana yawan harkar ciyarwa a faɗin jihar Kano.

Hajiya Rabi Inuwa Hussain wadda ta fara da godewa mai girma Gwamna Abba Kabir Yusuf bisa ƙoƙarin sa na tallafawa tsarin ilimi a wannan jiha don al’ummar sa su samu ilimi mai kyau.

Abba Kabir Yusuf ya kuma jinjina wa sauran ma’aikatan hukumar ilimi ta jihar Kano wajen ƙoƙarin da suka yi.

Bilala muhammad Abubuakr, Nahayatu Isah Garba, sun nuna godiyar su bisa yadda mai girma Gwamna ya taimaka Ɗaliban Kano 6,500 kuɗin Jarabawar JAMB da kowane Form ya kai Naira 6,200.

Ɗaya daga cikin iyayen yara Sada Muhammad Idris ya wakilci sauran iyayen yaran shi ma ya fara da godewa mai girma Gwamna bisa wannan ƙoƙari nasa.

Haka kuma yace a matsayin su na Iyayen yara za su ci gaba goyan baya ga duk wanda ke goyan bayan harkar ilmi a jihar Kano da yardar Allah.

Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Ilimi

Gwamnatin Katsina ta jaddada manufarta na ci gaba da bayar da horo ga malaman makaranta

Published

on

Gwamnatin Katsina ta jaddada manufarta na ci gaba da bayar da horo ga malaman makaranta

Gwamnatin Katsina ta jaddada manufarta na ci gaba da bayar da horo ga malaman makaranta

Daga Idris Umar, Zariya

Kwamishinar kula da ilimin firamare da na Sakandire ne ta bayyana ƙudirin gwamnatin jihar mai ci yanzu na ci gaba da bayar da ƙarin horo ga malamai a faɗin jihar don samar da ƙwararrun malamai da suka iya sarrafa na’ura mai ƙwaƙwalwa da za su yi gogayya da takwarorinsu a faɗin duniya.

Hajiya Zainab Musa Musawa ta bayar da tabbacin hakan ne a lokacin da ta kai ziyarar duba yadda shirin horar da malamai 10,000 da suka haɗa da sabbin ɗauka 7,000 a kan dabarun koyarwa na ƙarni na 20 ke gudana.

Kwamishinar ta kai ziyarar ne a makarantar firamare ta Modoji inda ake gudanar da bayar da horon na yini 3 wanda Ma’aikatar kula da ilimin firamare da na Sakandire, hukumar ilimin bai ɗaya da kuma haɗin gwiwa da shirin bunƙasa ilimi matakin jiha (TESS) suka shirya.

KU KUMA KARANTA: Da ilimi ake samun kowace irin nasara a rayuwa – Dauda Lawal 

Hajiya Zainab Musa Musawa wanda ta zagaya azuzuwa ta kuma tattauna da masu bayar da horon da Kuma malaman, ta bukace su da suyi amfani da lokacin su fahimci Abunda aka koyamasu don bunkasa tsarin koyo da koyarwa a jihar.

A yayin ziyarar dai Kwamishinar ta samu rakiyar Babbar Sakatariya a Ma’aikatar Hajiya Mairo Mohamed Othman, Mai baiwa Gwamna shawarma akan ilimi Nura Sale Katsayal sauran Daraktocin Ma’aikatar.

Bayanin hakan na ƙunshe a cikin wata sanarwa wadda jami’in hudda da jama’a na Ma’aikatar Malam Sani Ɗanjuma Suleiman ya Sanyama hannu a katsina.

Continue Reading

Ilimi

Da ilimi ake samun kowace irin nasara a rayuwa – Dauda Lawal 

Published

on

Da ilimi ake samun kowace irin nasara a rayuwa - Dauda Lawal 

Da ilimi ake samun kowace irin nasara a rayuwa – Dauda Lawal

Daga Idris UMAR, Zariya

Gwamna Dauda Lawal ya halarci taron yaye ɗalibai karo na uku da na huɗu na Jami’ar tarayya, wanda ya gudana a filin taro na Jami’ar da ke Gusau a cikin satin da ya gabata

Mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris ne ya bayyana haka a cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Litinin a Gusau cewa, Gwamna Lawal ya shelanta bayar da gurbin karatu ga duk wanda ya zo na ɗaya a Jami’ar.

Cikin jawabinsa a wurin taron, Gwamnan ya yaba wa shugabannin Jami’ar game da yadda suka iya ririta ɗan abin da suke da shi, duk da ɗimbin ƙalubalen da suke fuskanta.

Ya ce, “Ina matuƙar farin cikin kasancewa da ku yau a wannan bikin yaye ɗalibai karo na uku da na huɗu a wannan jajirtacciyar Jami’a, Jami’ar gwamnatin tarayya ta Gusau.

Ina taya jami’ar nan murnar samun wannan nasara, duk kuwa da matsalolin da suke fuskanta tun lokacin da aka kafa ta. Ina kuma yaba wa iyaye da ɗalibai bisa sadaukarwar da suka nuna har zuwa wannan matsayi.

Muna sa ran samun makoma mai kyau kuma mai albarka duk da tarin ƙalubalen da muke fuskanta a matsayinmu na jiha kuma al’umma.

Muna yin addu’a kuma muna aiki ba dare ba rana don samar da makoma mai kyau. Duk waɗannan matsaloli za su wuce da izinin Allah Maɗaukakin Sarki.”

Gwamnan ya yi ƙarin haske kan ƙoƙarin gwamnatinsa na gyara harkar ilimi a Jihar Zamfara bayan kafa dokar ta-ɓaci a bara.

“A matsayinmu na gwamnati, mun ƙuduri aniyar ilimantar da duk ’ya’yan Zamfara. Ilimi shi ne ginshiƙin da ke haskaka ruyuwar ɗan adam.

“Mun ware maƙudan kuɗaɗe ga ɓangaren ilimi a cikin kasafin kuɗinmu na 2024 kuma muna fatan za mu kai ga babban matsayi a 2025, 2026, da 2027. Muna fatan cimma kashi 25 zuwa 30 na haɓaka tsarin ilimi.

Tare da samar da ingantaccen tsari a fannin da sarrafa albarkatun da ya ƙunsa, muna da ƙwarin gwiwar cewa za mu farfaɗo da ababen more rayuwa, ɗaukar ƙwararrun malamai, horarwa da sake horar da waɗanda ake da su.

“Za kuma mu ƙara yawan masu karatu a makarantun firamare da na gaba da firamare ta hanyar wayar da kan jama’a da samar da ingantattun wuraren koyo da koyarwa. Ilimi kyauta ne, kuma muna fatan ya zama wajibi ga kowa.

“Mun kuma yi wa manyan makarantunmu da ke jihar kason kuɗi mai yawa don fara aikin gyara su zuwa matakai masu inganci.

KU KUMA KARANTA:Gwamnan Kaduna zai ba da ilimi kyauta ga ɗaliban Kuriga

A karon farko Jami’ar Jihar Zamfara na shirye-shiryen amincewa da shirin Hukumar Kula da Jami’o’i ta Ƙasa.

Mun umurci ’yan kwangilar da gwamnatin da ta shuɗe ta tilastawa barin wuraren aiki da su koma bakin aiki, kuma muna fatan nan da watanni masu zuwa, rukunin dindindin na jami’ar zai fara aiki. A lokaci guda, NUC za ta amince ga duk kwasa-kwasai.

“Mun karɓi mulki a jihar da gwamnati ta ƙi biyan kuɗaɗen jarrabawar WEAC da NECO har na biliyoyin Naira fiye da shekaru uku.

Dole muka yi shiri na musamman da hukumomin, kuma tun daga lokacin an fara biyan kuɗi a kan kari kuma za a kammala su a kan lokaci.

“A cikin ƙarancin albarkatunmu, za mu ci gaba da bayar da taimako ga jami’a. Burinmu shi ne mu ƙara haɓaka ilimi a jiharmu ta yadda za a samu damarmaki ga ɗaukacin matasanmu da za a horar da su don kai ga ƙololuwar da ilimi ke samarwa.”

Continue Reading

Ilimi

Jami’o’in Birtaniya za su fara ɗaukar masu sakamakon jarabawar NECO

Published

on

Jami’o’in Birtaniya za su fara ɗaukar masu sakamakon jarabawar NECO

Jami’o’in ƙasar Birtaniya na shirin fara daukar daliban Najeriya masu shaidar jarabawar kammala sakandare ta NECO.

Shugaban hukumar shirya jarabawa ta kasa (NECO), Farfesa Ibrahim Wushishi, ya ce Jami’ar Lead da Jami’ar Birmingham City da ke kasar Birtaniya sun tuntubi hukumar  kan jarabawar da take shiryawa.

Ya ce  jami’o’in sun fara tunanin bai wa daliban Najeriya gurbin karatu da sakamakon jarabawarsu ta NECO.

KU KUMA KARANTA: JAMB zata duba yiwuwar amfani da wayoyin hanu a jarabawar UTME

A fahimtarsa, hakan na nuni da  amincewa da ingancin sakamakon jarabawar NECO ne a idanun manyan jami’o’in ciki da wajen Najeriya.

Farfesa Wushishi ya bayyana hakan ne yayin wani taron tattaunawa da ’yan jarida a Abuja ranar Laraba.

Ya ce NECO ta cika sharudan Jami’ar Birmingham City, kuma a halin yanzu suna aiki tukuru kan ganin sun sami cika sharudan jami’ar Lead.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like