Connect with us

Ilimi

Gwamna Buni ya ba da tallafin karatu ga ɗaliban koyon Shari’a kimanin 221 a Yobe

Published

on

Daga Sani Gazas Chinade, Damaturu

Gwamnan jihar Yobe, Mai Mala Buni ya ba da tallafin karatu ga ɗalibai 221 da suka kammala karatu a fannin shari’a daga Jami’o’i daban-daban a faɗin ƙasar nan a wani ɓangare na ƙoƙarin ƙarfafa ilimi.

Wannan taron ba da tallafin ya gudana ne a babban  ɗakin taro na Banquet da ke gidan gwamnati da ke Damaturu, wanda ya samu halartar manyan baƙi daga kowane lungu da saƙo na jihar.

A nasa jawabin, gwamnan jihar Yobe, Mai Mala Buni ya taya waɗanda suka ci gajiyar tallafin murna “bari in fara da taya ku murnar kammala karatun digiri a fannin shari’a a jihar Yobe tare da yi muku fatan alheri a lokacin da kuke shirin neman takardar shedar ƙwarewa a babbar Makarantar koyar da shari’a ta ƙasa (Nigerian Law School).

KU KUMA KARANTA: Gwamna Buni ya nemi haɗin kan jami’o’in Burtaniya uku, don bunƙasa harkar ilimi a jihar Yobe

Ya bayyana cewa, “Kamar yadda kuka sani, wannan gwamnatin ta ba da fifiko ga samar da ingantaccen ilimi tun daga tushe ta hanyar manyan makarantu, da kwasa-kwasa kamar fannin shari’a, fannin lissafi da kudaden, fannin koyon Likitanci da sauransu.”

“Wannan shi ne dalilin da ya sa gwamnatinmu ta tsaya tsayin daka wajen samar da yanayi mai kyau a makarantunmu ta hanyar sake gina makarantun da suka lalace  da kuma kafa sababbi.”

“Mun kuma ba da kayan koyo da  koyarwa ga manyan makarantunmu da cibiyoyin kiwon lafiya da su ma muke ƙoƙarin wadata su da kayan kiwon lafiya.”

“Na yi farin cikin bayyana irin  gamsuwa ta bisa ƙoƙarin wannan gwamnati na samun  daidaiton wajen inganta fannin ilimi ya kasance mai amfani kamar yadda aka nuna a irin hazaƙar dalibanmu gaba daya.”

“Abin farin ciki ne cewa jihar Yobe ta ci gaba da zama ta ɗaya da ba a doke ta ba a shiyyar Arewa maso Gabas, da kuma a cikin jihohin Nijeriya, inda Makarantar koyon shari’ar ta ba wa ɗalibanmu wannan damar don neman takardar shedar ƙwarewa cikin sauƙi.

“Ina so in tabbatar muku da cewa wannan gwamnatin za ta ci gaba da yin tsayin daka wajen bayar da guraben karatu ga ‘yan asalin Yobe da suka cancanta a manyan makarantu a gida da kuma cibiyoyin karatu a ƙasashen waje a faɗin duniya”.

Ya ƙara da cewa, “bikin bayar da tallafin karatu ga ɗaliban mu na Lauyoyin da za su halarci makarantar koyon aikin lauya ta Najeriya ya taimaka wa wannan gwamnati a cikin shekaru huɗun da suka gabata ga ɗaliban da ke karatun lauya ta wajen samun shaidar ƙwarewa a wannan fanni  ya yi dai-dai da tsarin da muke da shi na ci gaban ilimi ”.

“Saboda haka, ya kamata ku bi kwas ɗin ku na ƙwararru tare da sa  himma don mayar da jiharmu abin alfahari a kan wannan fanni na shari’a.”

“Ya kamata ku yi ƙoƙari ku zama jakadu nagari na jihar, kuma ku ci gaba da kasancewa wuraren nunin ƙwararrun ilimi da ɗabi’a.”

“Bari na kuma tabbatar muku da cewa gwamnati za ta sa ido sosai kan ayyukanku a yayin gudanar da karatun ku tare da ba ku tallafin da ya dace don samun nasara.

“Ina yi muku fatan samun nasara sosai kuma ina fatan halartar bikin yayewar ku a karshen karatun ku, kuma ina muku fatan alheri.” 

Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Ilimi

Gwamnatin Katsina ta jaddada manufarta na ci gaba da bayar da horo ga malaman makaranta

Published

on

Gwamnatin Katsina ta jaddada manufarta na ci gaba da bayar da horo ga malaman makaranta

Gwamnatin Katsina ta jaddada manufarta na ci gaba da bayar da horo ga malaman makaranta

Daga Idris Umar, Zariya

Kwamishinar kula da ilimin firamare da na Sakandire ne ta bayyana ƙudirin gwamnatin jihar mai ci yanzu na ci gaba da bayar da ƙarin horo ga malamai a faɗin jihar don samar da ƙwararrun malamai da suka iya sarrafa na’ura mai ƙwaƙwalwa da za su yi gogayya da takwarorinsu a faɗin duniya.

Hajiya Zainab Musa Musawa ta bayar da tabbacin hakan ne a lokacin da ta kai ziyarar duba yadda shirin horar da malamai 10,000 da suka haɗa da sabbin ɗauka 7,000 a kan dabarun koyarwa na ƙarni na 20 ke gudana.

Kwamishinar ta kai ziyarar ne a makarantar firamare ta Modoji inda ake gudanar da bayar da horon na yini 3 wanda Ma’aikatar kula da ilimin firamare da na Sakandire, hukumar ilimin bai ɗaya da kuma haɗin gwiwa da shirin bunƙasa ilimi matakin jiha (TESS) suka shirya.

KU KUMA KARANTA: Da ilimi ake samun kowace irin nasara a rayuwa – Dauda Lawal 

Hajiya Zainab Musa Musawa wanda ta zagaya azuzuwa ta kuma tattauna da masu bayar da horon da Kuma malaman, ta bukace su da suyi amfani da lokacin su fahimci Abunda aka koyamasu don bunkasa tsarin koyo da koyarwa a jihar.

A yayin ziyarar dai Kwamishinar ta samu rakiyar Babbar Sakatariya a Ma’aikatar Hajiya Mairo Mohamed Othman, Mai baiwa Gwamna shawarma akan ilimi Nura Sale Katsayal sauran Daraktocin Ma’aikatar.

Bayanin hakan na ƙunshe a cikin wata sanarwa wadda jami’in hudda da jama’a na Ma’aikatar Malam Sani Ɗanjuma Suleiman ya Sanyama hannu a katsina.

Continue Reading

Ilimi

Da ilimi ake samun kowace irin nasara a rayuwa – Dauda Lawal 

Published

on

Da ilimi ake samun kowace irin nasara a rayuwa - Dauda Lawal 

Da ilimi ake samun kowace irin nasara a rayuwa – Dauda Lawal

Daga Idris UMAR, Zariya

Gwamna Dauda Lawal ya halarci taron yaye ɗalibai karo na uku da na huɗu na Jami’ar tarayya, wanda ya gudana a filin taro na Jami’ar da ke Gusau a cikin satin da ya gabata

Mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris ne ya bayyana haka a cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Litinin a Gusau cewa, Gwamna Lawal ya shelanta bayar da gurbin karatu ga duk wanda ya zo na ɗaya a Jami’ar.

Cikin jawabinsa a wurin taron, Gwamnan ya yaba wa shugabannin Jami’ar game da yadda suka iya ririta ɗan abin da suke da shi, duk da ɗimbin ƙalubalen da suke fuskanta.

Ya ce, “Ina matuƙar farin cikin kasancewa da ku yau a wannan bikin yaye ɗalibai karo na uku da na huɗu a wannan jajirtacciyar Jami’a, Jami’ar gwamnatin tarayya ta Gusau.

Ina taya jami’ar nan murnar samun wannan nasara, duk kuwa da matsalolin da suke fuskanta tun lokacin da aka kafa ta. Ina kuma yaba wa iyaye da ɗalibai bisa sadaukarwar da suka nuna har zuwa wannan matsayi.

Muna sa ran samun makoma mai kyau kuma mai albarka duk da tarin ƙalubalen da muke fuskanta a matsayinmu na jiha kuma al’umma.

Muna yin addu’a kuma muna aiki ba dare ba rana don samar da makoma mai kyau. Duk waɗannan matsaloli za su wuce da izinin Allah Maɗaukakin Sarki.”

Gwamnan ya yi ƙarin haske kan ƙoƙarin gwamnatinsa na gyara harkar ilimi a Jihar Zamfara bayan kafa dokar ta-ɓaci a bara.

“A matsayinmu na gwamnati, mun ƙuduri aniyar ilimantar da duk ’ya’yan Zamfara. Ilimi shi ne ginshiƙin da ke haskaka ruyuwar ɗan adam.

“Mun ware maƙudan kuɗaɗe ga ɓangaren ilimi a cikin kasafin kuɗinmu na 2024 kuma muna fatan za mu kai ga babban matsayi a 2025, 2026, da 2027. Muna fatan cimma kashi 25 zuwa 30 na haɓaka tsarin ilimi.

Tare da samar da ingantaccen tsari a fannin da sarrafa albarkatun da ya ƙunsa, muna da ƙwarin gwiwar cewa za mu farfaɗo da ababen more rayuwa, ɗaukar ƙwararrun malamai, horarwa da sake horar da waɗanda ake da su.

“Za kuma mu ƙara yawan masu karatu a makarantun firamare da na gaba da firamare ta hanyar wayar da kan jama’a da samar da ingantattun wuraren koyo da koyarwa. Ilimi kyauta ne, kuma muna fatan ya zama wajibi ga kowa.

“Mun kuma yi wa manyan makarantunmu da ke jihar kason kuɗi mai yawa don fara aikin gyara su zuwa matakai masu inganci.

KU KUMA KARANTA:Gwamnan Kaduna zai ba da ilimi kyauta ga ɗaliban Kuriga

A karon farko Jami’ar Jihar Zamfara na shirye-shiryen amincewa da shirin Hukumar Kula da Jami’o’i ta Ƙasa.

Mun umurci ’yan kwangilar da gwamnatin da ta shuɗe ta tilastawa barin wuraren aiki da su koma bakin aiki, kuma muna fatan nan da watanni masu zuwa, rukunin dindindin na jami’ar zai fara aiki. A lokaci guda, NUC za ta amince ga duk kwasa-kwasai.

“Mun karɓi mulki a jihar da gwamnati ta ƙi biyan kuɗaɗen jarrabawar WEAC da NECO har na biliyoyin Naira fiye da shekaru uku.

Dole muka yi shiri na musamman da hukumomin, kuma tun daga lokacin an fara biyan kuɗi a kan kari kuma za a kammala su a kan lokaci.

“A cikin ƙarancin albarkatunmu, za mu ci gaba da bayar da taimako ga jami’a. Burinmu shi ne mu ƙara haɓaka ilimi a jiharmu ta yadda za a samu damarmaki ga ɗaukacin matasanmu da za a horar da su don kai ga ƙololuwar da ilimi ke samarwa.”

Continue Reading

Ilimi

Jami’o’in Birtaniya za su fara ɗaukar masu sakamakon jarabawar NECO

Published

on

Jami’o’in Birtaniya za su fara ɗaukar masu sakamakon jarabawar NECO

Jami’o’in ƙasar Birtaniya na shirin fara daukar daliban Najeriya masu shaidar jarabawar kammala sakandare ta NECO.

Shugaban hukumar shirya jarabawa ta kasa (NECO), Farfesa Ibrahim Wushishi, ya ce Jami’ar Lead da Jami’ar Birmingham City da ke kasar Birtaniya sun tuntubi hukumar  kan jarabawar da take shiryawa.

Ya ce  jami’o’in sun fara tunanin bai wa daliban Najeriya gurbin karatu da sakamakon jarabawarsu ta NECO.

KU KUMA KARANTA: JAMB zata duba yiwuwar amfani da wayoyin hanu a jarabawar UTME

A fahimtarsa, hakan na nuni da  amincewa da ingancin sakamakon jarabawar NECO ne a idanun manyan jami’o’in ciki da wajen Najeriya.

Farfesa Wushishi ya bayyana hakan ne yayin wani taron tattaunawa da ’yan jarida a Abuja ranar Laraba.

Ya ce NECO ta cika sharudan Jami’ar Birmingham City, kuma a halin yanzu suna aiki tukuru kan ganin sun sami cika sharudan jami’ar Lead.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like