Connect with us

Labarai

Gasar AFCON: Najeriya ta ja hankalin ‘yan ƙasarta da ke Afirka ta Kudu

Published

on

Gwamnatin Najeriya ta shawarci ƴan ƙasar da ke zaune a Afirka ta Kudu kan su kula da kansu kafin da kuma bayan wasan da ƙasar za ta yi da Afirka ta Kudu a Gasar AFCON.

Ofishin jakadancin Najeriya da ke birnin Pretoria na Afirka ta Kudu ne ya fitar da wannan sanarwar inda ya ce ya kula da wasu maganganu da ake yi a shafukan sada zumunta waɗanda ka iya tayar da hargitsi bayan wasan.

“Galibin kalaman sun ƙunshi barazanar da ake yi wa “’ƴan Najeriya kan dafa dukar shinkafa” kafin wasan, da kuma “saka wa ƴan Nijeriya barkono idan Bafana Bafana ta sha kashi a hannun Super Eagles a ranar Laraba 7 ga watan Fabrairun 2024,” in ji sanarwar.

“Sakamakon haka, ofishin jakadancin ke bayar da shawara ga ƴan Najeriya da su lura da abubuwan da za su furta da kuma wurin da za su je kallon wasan musamman a bainar jama’a, da kuma guje wa ɗaga murya a lokacin murna ko tayar da rikici ko murna cikin tsokana idan Super Eagles ɗin ta yi nasara a wasan.

KU KUMA KARANTA: Dalilin da ya sa Ahmed Musa bai buga wasa ko ɗaya ba, a wasan cin kofin Afirka

“Haka kuma, ƴan Najeriya su ci gaba da nuna kyakkyawar ɗabi’ar da aka san su da ita, su kuma bi doka kafin da kuma bayan wasan. Ko da an harzuƙa, kada su mayar da martani, su kai koke wurin hukumomin da suka dace,” kamar yadda sanarwar ta ƙara da cewa.

Duka wannan na zuwa ne a daidai lokacin da Najeriya ke shirin buga wasan daf da ƙarshe da Afirka ta Kudu a Gasar AFCON a ranar Laraba.

A ɗayan ɓangaren kuwa Ivory Coast wadda ke karɓar baƙuncin gasar za ta fafata da Jamhuriyar Dimokuradiyyar Kongo a ranar Larabar.

Duk waɗanda suka yi nasara a cikin rukunan biyu za su fafata a wasan ƙarshe a ranar Lahadi 11 ga watan Fabrairun 2024.

Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

‘Yan sanda sun sha alwashin daƙile tashe-tashen hankula a lokacin zanga-zanga

Published

on

‘Yan sanda sun sha alwashin daƙile tashe-tashen hankula a lokacin zanga-zanga

‘Yan sanda sun sha alwashin daƙile tashe-tashen hankula a lokacin zanga-zanga

Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta sha alwashin magance tashe-tashen hankula yayin zanga-zangar gama garin da ake shirin gudanarwa a ranar 1 ga watan Agusta mai kamawa.

Sanarwar da kakakin rundunar ‘yan sandan birnin tarayya Abuja, SP Josephine Adeh, ta fitar a yau Juma’a tace, rundunar ta tura jami’anta dubu 4 da 200 domin shawo kan duk wani nau’in tashin hankalin da ka iya tasowa yayin zanga-zangar.

Manufar tura ‘yan sandan ita ce tabbatar da tsaron al’umma da ba da kariya ga masu zanga-zangar.

KU KUMA KARANTA:Ba za mu bari a wargaza ƙasa ta hanyar zanga-zanga ba – Rundunar Sojin Najeriya

Da ya ke tabbatar da hakkin mazauna birnin na gudanar da zanga-zanga, kwamishinan ‘yan sanda Abuja, Benneth Igweh, ya ba da shawarar cewa kamata ya yi a yi ta cikin lumana.

Ya ce, “kwamishinan ‘yan sanda ya sha alwashin daƙile dukkanin wani nau’i na tashin hankali da rashin bin doka da oda, kasancewar ‘yan sanda ba zasu kyalle suna kallo a lalata dukiyoyin hukuma da na daidaikun mutane ko kuma a samu asarar rayuka ba.

Continue Reading

Labarai

Sarkin Gwandu ya naɗa ɗan Buran ɗin Gwandu babba

Published

on

Sarkin Gwandu ya naɗa ɗan Buran ɗin Gwandu babba

Sarkin Gwandu ya naɗa ɗan Buran ɗin Gwandu babba

Daga Haruna Abdulrashid

Shugaban majalisar sarakuna ta jihar Kebbi, Mai martaba Sarkin Gwandu, Manjo-Janar Muhammadu Ilyasu Bashar Mni, ya karrama Shugaban hukumar jin daɗi da walwalar Alhazzai ta ƙasa, Malam Jalal Muhammad Arabi da sarautar (ƊAN BURAN GWANDU BABBA) inda mai martaba sarki ya aike da tawaga zuwa birnin tarayya Abuja domin gabatar da wannan karramawa zuwa ga Malam Jalal Arabi.

Da ya ke jawabi a madadin mai martaba sarkin Gwandu Alhaji Aminu Ahmad, Sarkin Fadan Gwandu ya bayyana cewa mai martaba sarkin Gwandu ya amince da bayar da wannan karramawa ga Malam Jalal ne a bisa jajircewa da kuma taimako da yake yiwa Alhazzan Najeriya tare da haɗin kai da yake bawa shugabanni a kan abin da ya shafi harkar aikin Hajji mussaman a bana.

Shi ma shugaban hukumar jin daɗin da walwalar Alhazai ta jihar Kebbi, Alhaji Faruƙu Musa Yaro Enabo, Jagaban Gwandu, ya bayyana jin daɗin shi matuƙa a kan wannan karramawar da aka yi wa maigidan shi.

Ya kuma yabawa mai martaba Sarkin Gwandu Manjo-Janar Muhammadu Ilyasu Bashar akan yadda yake gabatar da kyakkyawan jagoranci zuwa ga Al’ummar Gwandu.

Wannan bayar da takardar karramawa ta sarautar (ƊAN BURAN GWANDU) Sun haɗa da Alh Aminu Ahmed Sarkin Fadan Gwandu, Alh Aminu Abubakar Gulumbe Uban ƙasar Gulumbe, Alh. Mustapha Ka’oje Sarkin Bargun Ka’oje, Alh Lamiru Shehu Sakataren Sarakunan jihar Kebbi, Alh Faruƙu Musa Yaro Enabo Jagaban Gwandu, Alh Usman Osho da Alh Rilwanu Awwal.

Mai girma Shugaban hukumar Jin daɗi da walwalar Alhazzai ta jihar Kebbi, Malam Jalal Arabi, ya bayyana jin daɗin shi sosai ganin wanan karramawa da ya samu daga masarautar Gwandu.

Ya kuma ce jihar Kebbi ta zama gida a gareshi ganin yadda yake samun karramawa da mutuntawa a jihar ya kuma bayyana mana irin mutunci da zumunci dake tsakanin shi da shugaban hukumar Jin daɗi da walwalar Alhazzai ta jihar Kebbi.

Alh Faruku Musa Yaro Enabo Jagaban Gwandu ya kuma yi godiya da jinjina zuwa ga Maigirma Gwamnan jihar Kebbi His Excellency Comrd Dr. Nasir Idris Ƙauran Gwandu akan irin yadda yayi ɗawainiya ga Alhazzan jihar shi.

Continue Reading

Labarai

Mun gana da shugaba Tinubu mun isar masa saƙon al’umma – Shaikh Bala Lau

Published

on

Mun gana da shugaba Tinubu mun isar masa saƙon al'umma - Shaikh Bala Lau

Mun gana da shugaba Tinubu mun isar masa saƙon al’umma – Shaikh Bala Lau

Daga Idris Umar, Zariya

A ranar Alhamis tawagar malaman Najeriya ta gana da shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu dangane da halin da ƙasa ta ke ciki kan batun zanga-zanga da wasu ke ƙiran a yi dalilin halin matsi da tsadar rayuwa.

Rahoton sun nuna cewa jim kaɗanne bayan kammala ganawar, shugaban ƙungiyar Izala na ƙasa, Shaikh Abdullahi Bala Lau ya shaidawa manema labarai cewa shugaban ƙasa ya karɓi koken da suka je masa da shi.

“Mun faɗa mar halin da al’umma suke ciki na tsadar rayuwa, taɓarɓarewar tsaro da wahalar rayuwa, ya kuma ce dan Allah a ja hankalin al’umma a ba su haƙuri nan gaba kaɗan za a ga sauyi da gyara kan ƙorafe-ƙorafen da ake yi”. In ji Bala Lau.

KU KUMA KARANTA: Zanga-zanga ba gudu ba ja da baya – ‘Yan Najeriya

Daga nan kuma, Shaikh ɗin ya ja hankalin al’umma da su yi haƙuri su cigaba da addu’a, “ba mu da ƙasar da ta fi Najeriya kar mu rusa ƙasarmu da kanmu”. Inji Shaikh Bala Lau.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like