Labarai
El-Rufai ya bar wa jihar Kaduna ɗimbim bashi – Gwamnan Uba Sani
Daga Idris Umar, Zariya
Gwamna Uba Sani ya bayyana haka ne a Kaduna a ranar Asabar yayin da yake jawabi a wajen wani babban taron ji daga jama’a, inda ya ce ɗimbim bashin da ake bin jihar Kaduna shi ke laƙume ɗan abin da ta ke samu.
Gwamnan ya kuma bayyana cewa gwamnatin sa ta gaji bashin Dalar Amurka Miliyan 587 da bashin Naira Biliyan 85 da kuma ayyukan kwangila 115 daga gwamnatin Nasir El-Rufai.
Ya bayyana cewa gwamnatin jihar ta ware Naira Biliyan 7 daga cikin Naira Billiyan 10 da Gwamnatin Tarayya ta ware mata a watan Maris, domin biyan bashi.
Gwamnan ya kuma koka kan tashin farashin canji, wanda ya ce jihar na biyan kusan ninki uku na bashin da gwamnatin baya ta karɓo.
KU KUMA KARANTA: Nijar ta gaza biyan bashin da ya kai dala miliyan ɗari biyar – WAEMU
Ya Kuma koka da yadda gwamnatin El-Rufai ta bar wa jihar Biliyan uku kacal a asusun, wanda ya gaza biyan albashin ma’aikata da ake biya na Naira Biliyan 5.2 a duk wata.
Gwamnan ya ƙara da cewa muhimman abubuwan da gwamnatin sa ta sa a gaba sun haɗa da tsaro, samar da gidaje, ilimi, kiwon lafiya da tallafa wa masu ƙananan sana’o’i.
Ya ce gwamnatin sa za ta kuma mayar da hankali wajen samar da ci gaba ta hanyar saka hannun jari, inganta tattalin arziƙi da samar da gidaje masu sauƙi.
Ya ka bayyana wasu muhimman abubuwan da gwamnatin tasa ta sa a gaba a 2024 da suka haɗa da tsaro, samar da ababen more rayuwa, bunƙasa ilimi, samar da gidaje da ci gaban birane da dai sauransu.
Labarai
‘Yan sanda sun sha alwashin daƙile tashe-tashen hankula a lokacin zanga-zanga
‘Yan sanda sun sha alwashin daƙile tashe-tashen hankula a lokacin zanga-zanga
Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta sha alwashin magance tashe-tashen hankula yayin zanga-zangar gama garin da ake shirin gudanarwa a ranar 1 ga watan Agusta mai kamawa.
Sanarwar da kakakin rundunar ‘yan sandan birnin tarayya Abuja, SP Josephine Adeh, ta fitar a yau Juma’a tace, rundunar ta tura jami’anta dubu 4 da 200 domin shawo kan duk wani nau’in tashin hankalin da ka iya tasowa yayin zanga-zangar.
Manufar tura ‘yan sandan ita ce tabbatar da tsaron al’umma da ba da kariya ga masu zanga-zangar.
KU KUMA KARANTA:Ba za mu bari a wargaza ƙasa ta hanyar zanga-zanga ba – Rundunar Sojin Najeriya
Da ya ke tabbatar da hakkin mazauna birnin na gudanar da zanga-zanga, kwamishinan ‘yan sanda Abuja, Benneth Igweh, ya ba da shawarar cewa kamata ya yi a yi ta cikin lumana.
Ya ce, “kwamishinan ‘yan sanda ya sha alwashin daƙile dukkanin wani nau’i na tashin hankali da rashin bin doka da oda, kasancewar ‘yan sanda ba zasu kyalle suna kallo a lalata dukiyoyin hukuma da na daidaikun mutane ko kuma a samu asarar rayuka ba.
Labarai
Sarkin Gwandu ya naɗa ɗan Buran ɗin Gwandu babba
Sarkin Gwandu ya naɗa ɗan Buran ɗin Gwandu babba
Daga Haruna Abdulrashid
Shugaban majalisar sarakuna ta jihar Kebbi, Mai martaba Sarkin Gwandu, Manjo-Janar Muhammadu Ilyasu Bashar Mni, ya karrama Shugaban hukumar jin daɗi da walwalar Alhazzai ta ƙasa, Malam Jalal Muhammad Arabi da sarautar (ƊAN BURAN GWANDU BABBA) inda mai martaba sarki ya aike da tawaga zuwa birnin tarayya Abuja domin gabatar da wannan karramawa zuwa ga Malam Jalal Arabi.
Da ya ke jawabi a madadin mai martaba sarkin Gwandu Alhaji Aminu Ahmad, Sarkin Fadan Gwandu ya bayyana cewa mai martaba sarkin Gwandu ya amince da bayar da wannan karramawa ga Malam Jalal ne a bisa jajircewa da kuma taimako da yake yiwa Alhazzan Najeriya tare da haɗin kai da yake bawa shugabanni a kan abin da ya shafi harkar aikin Hajji mussaman a bana.
Shi ma shugaban hukumar jin daɗin da walwalar Alhazai ta jihar Kebbi, Alhaji Faruƙu Musa Yaro Enabo, Jagaban Gwandu, ya bayyana jin daɗin shi matuƙa a kan wannan karramawar da aka yi wa maigidan shi.
Ya kuma yabawa mai martaba Sarkin Gwandu Manjo-Janar Muhammadu Ilyasu Bashar akan yadda yake gabatar da kyakkyawan jagoranci zuwa ga Al’ummar Gwandu.
Wannan bayar da takardar karramawa ta sarautar (ƊAN BURAN GWANDU) Sun haɗa da Alh Aminu Ahmed Sarkin Fadan Gwandu, Alh Aminu Abubakar Gulumbe Uban ƙasar Gulumbe, Alh. Mustapha Ka’oje Sarkin Bargun Ka’oje, Alh Lamiru Shehu Sakataren Sarakunan jihar Kebbi, Alh Faruƙu Musa Yaro Enabo Jagaban Gwandu, Alh Usman Osho da Alh Rilwanu Awwal.
Mai girma Shugaban hukumar Jin daɗi da walwalar Alhazzai ta jihar Kebbi, Malam Jalal Arabi, ya bayyana jin daɗin shi sosai ganin wanan karramawa da ya samu daga masarautar Gwandu.
Ya kuma ce jihar Kebbi ta zama gida a gareshi ganin yadda yake samun karramawa da mutuntawa a jihar ya kuma bayyana mana irin mutunci da zumunci dake tsakanin shi da shugaban hukumar Jin daɗi da walwalar Alhazzai ta jihar Kebbi.
Alh Faruku Musa Yaro Enabo Jagaban Gwandu ya kuma yi godiya da jinjina zuwa ga Maigirma Gwamnan jihar Kebbi His Excellency Comrd Dr. Nasir Idris Ƙauran Gwandu akan irin yadda yayi ɗawainiya ga Alhazzan jihar shi.
Labarai
Mun gana da shugaba Tinubu mun isar masa saƙon al’umma – Shaikh Bala Lau
Mun gana da shugaba Tinubu mun isar masa saƙon al’umma – Shaikh Bala Lau
Daga Idris Umar, Zariya
A ranar Alhamis tawagar malaman Najeriya ta gana da shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu dangane da halin da ƙasa ta ke ciki kan batun zanga-zanga da wasu ke ƙiran a yi dalilin halin matsi da tsadar rayuwa.
Rahoton sun nuna cewa jim kaɗanne bayan kammala ganawar, shugaban ƙungiyar Izala na ƙasa, Shaikh Abdullahi Bala Lau ya shaidawa manema labarai cewa shugaban ƙasa ya karɓi koken da suka je masa da shi.
“Mun faɗa mar halin da al’umma suke ciki na tsadar rayuwa, taɓarɓarewar tsaro da wahalar rayuwa, ya kuma ce dan Allah a ja hankalin al’umma a ba su haƙuri nan gaba kaɗan za a ga sauyi da gyara kan ƙorafe-ƙorafen da ake yi”. In ji Bala Lau.
KU KUMA KARANTA: Zanga-zanga ba gudu ba ja da baya – ‘Yan Najeriya
Daga nan kuma, Shaikh ɗin ya ja hankalin al’umma da su yi haƙuri su cigaba da addu’a, “ba mu da ƙasar da ta fi Najeriya kar mu rusa ƙasarmu da kanmu”. Inji Shaikh Bala Lau.
-
Kotu1 year ago
Kotu tayi watsi da ƙarar APC game da zaɓen Abba Gida Gida
-
Labarai10 months ago
Dalilin da ya sa na saka wa matata sasari – Wani magidanci a Potiskum
-
Ƙasashen Waje1 year ago
Ɗaliban Najeriya a Sudan sun nemi a kwaso su daga ƙasar
-
Labarai1 year ago
‘Yan banga sun kama wani mutum da ke yunƙurin sace yarinya a Kano