Siyasa
Asiwaju Bola Tinubu Ne Ya Lashe Zaben Fidda Gwanin Jam’iyyar APC Da Kuri’u 1271
Daga; MUSTAPHA IMRANA ABDULLAHI.
JAM’IYYAR APC a tarayyar Najeriya ta bayyana sakamakon zaben da kowane dan takara ya samu daga cikin yan takara Goma 14 da suka tsaya neman Jam’iyyar ta tsayar da su takarar kujerar shugaban kasa a karkashin Jam’iyyar.
Kamar yadda aka sanar a filin wasa na Eagle Square a garin Abuja bayan kammala taron, an bayyana Asiwaju Bola Ahmed Tinubu a matsayin wanda ya yi nasarar lashe zaben fidda gwanin a Jam’iyyar ta APC.
Ga kuma yadda sakamakon zaben ta kasance:
Asiwaju Ahmad Bola Tinubu – 1271
Ahmad Lawal – 152
Rotimi Ameachi – 316
Gwamna Yahya Bello – 47
Farfesa Yemi Osinbajo – 235
Ahmad Rufa’I Sani Yarima – 4
Pastor Tunde Bakare – 0
Chukwumeka Nwajiba – 1
Engr David Omahy – 38
Sanata Farfesa Ben Ayade – 37
Sanata Rochas Okorocha – 0
T N Jackreach – 0
Dokta Christoper Onu – 1
Chief Eco Abalu Mukolu – 0
Siyasa
APC ta dakatar da ɗan Majalisa kan cin amana a Zamfara
![](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2024/05/aminu-san-jaji.jpeg)
APC ta dakatar da ɗan Majalisa kan cin amana a Zamfara
Jam’iyyar APC reshen Jihar Zamfara ta dakatar da Ɗan Majalisar Wakilai, Aminu Jaji bisa wasu zarge-zargen da ake yi masa na cin amanar jam’iyyar.
Sakataren Yaɗa Labarai na Jam’iyyar APC na Jihar, Malam Yusuf Idris ne ya sanar da dakatarwar a wani taron manema labarai a Gusau a ranar Juma’a.
Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa, Jaji yana wakiltar mazaɓar Ƙaura-Namoda/Birnin-Magaji a Majalisar Wakilai a ƙarƙashin jam’iyyar APC.
Idris ya ce wasu zarge-zargen da ake yi wa Ɗan Majalisar sun haɗa da aikata rashin gaskiya da rashin zuwa tarurrukan jam’iyyar da kuma sauran ayyuka.
KU KUMA KARANTA: Kotun Najeriya ta bayar da umarnin dakatar da asusun banki fiye da dubu 1
Ya ce, matakin ya biyo bayan sanarwar dakatarwar da aka yi wa Jaji daga shugabannin jam’iyyar APC na mazaɓar Birnin-Magaji bisa zargin cin amanar jam’iyyar da dai sauran abubuwan da suka saɓa wa jam’iyyar.
Idris ya ce, “Kwamitin zartaswa na jam’iyyar APC na ƙaramar hukumar Birnin Magaji ne ya miƙa sanarwar dakatarwar zuwa hedikwatar jam’iyyar APC ta jihar.
Bayanai sun ce kwamitin zartaswar jam’iyyar APC na jihar ya gudanar da taron gaggawa a sakatariyar jam’iyyar da ke Gusau a ranar Juma’a 17 ga watan Mayu, 2024, inda aka gabatar da batun dakatar da Jaji ga ‘yan majalisar zartarwar jihar.
Labarai
Tsohon gwamnan Katsina, Shema ya sauya sheƙa zuwa APC
![](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2024/05/IMG_8221.jpeg)
Tsohon gwamnan jihar Katsina, Ibrahim Shema, a hukumance ya koma jam’iyyar APC Mai mulki a jihar.
Shema, ya kasance gwamnan jihar a tsakanin shekarar 2007 zuwa 2015, a ƙarƙashin jam’iyyar PDP.
Tsohon gwamnan ya yi rajista ne a ofishin jam’iyyar na mazaɓar Shema, ƙaramar hukumar Dutsin-ma, inda shugaban jam’iyyar na jihar, Sani Aliyu-Daura ya ba shi katin zama ɗan jam’iyyar APC.
Lambar katin Shema ta zama ɗan jam’iyyar ita ce: 26551.
KU KUMA KARANTA:Gwamnatin Yobe za ta mayar da kwale-kwalen Dufuna mai shekaru 8,000 zuwa cibiyar yawon buɗe ido
Malam Aliyu-Daura ya yabawa Gwamna Dikko Raɗɗa da kuma tsohon gwamnan jihar Aminu Masari wanda ya gada, a bisa rawar da suka taka wajen ganin Shema ya sauya sheƙa.
Don haka ya tabbatar wa tsohon gwamnan cewa za a yi masa adalci kamar kowane ɗan jam’iyya.
Shugaban ma’aikata na Raɗɗa, Jabiru Abdullahi-Tasuri, shi ne ya miƙa katin zama ɗan jam’iyya ga Shema a madadin gwamnan a jiya Alhamis a Dutsin-ma.
Labarai
Fusatattun matasa sun lakaɗawa kwamishina duka a wajen zaɓen fidda gwani
![](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2024/04/IMG_8016.png)
Banji Ajaka, kwamishinan lafiya na jihar Ondo, ya gamu da fushin matasa a jiya Asabar yayin da ake gudanar da zaɓen fidda gwani na gwamna na jam’iyyar APC mai mulki a jihar.
Daily Trust ta gano cewa Dakta Ajaka, wanda ke Mazaɓar Ugbo 3, a ƙaramar hukumar, ana zarginsa da ɓoye takardar sakamakon zaɓen.
Shaidu sun tabbatar da faruwar lamarin a wata tattaunawa da suka yi da manema labarai, inda suka yi zargin cewa fusatattaun matasan ‘ya’yan jam’iyyar APC ne da ke adawa da tsarin da aka bi wajen gudanar da zaɓen.
Ɗaya daga cikin waɗanda suka shaida lamarin, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya bayyana cewa rikicin ya faro ne lokacin da ‘yan ɗaya ɓangaren na jam’iyyar suka buƙaci ganin takardar sakamakon zaɓen na fidda gwani.
KU KUMA KARANTA:An yi jana’izar tsohon gwamnan Ondo, Rotimi Akeredolu
“Sun fusata ne suka buƙaci jami’in zaɓe ya ba su takardar sakamakon zaɓen sai kuwa ya ce ta na wajen Ajaka.
“Don haka suka yi masa duka a wurin, inda kuma garinsu ne. Jama’a sun fusata sosai da lamarin, inda rigimar ta ƙare a wajen.”
Da yake tabbatar da faruwar lamarin, Dakta Ajaka ya ce an zarge shi ne da riƙe takardar sakamakon zaɓen.
Ya yi bayanin cewa a lokacin da yake ƙoƙarin bayyana kansa, ’yan daban sun auka masa inda suka yi masa mugun duka.
-
Kotu1 year ago
Kotu tayi watsi da ƙarar APC game da zaɓen Abba Gida Gida
-
Labarai9 months ago
Dalilin da ya sa na saka wa matata sasari – Wani magidanci a Potiskum
-
Ƙasashen Waje1 year ago
Ɗaliban Najeriya a Sudan sun nemi a kwaso su daga ƙasar
-
Labarai1 year ago
‘Yan banga sun kama wani mutum da ke yunƙurin sace yarinya a Kano
Pingback: INEC ta bayyana Tunibu a matsayin wanda ya lashe zaɓen shugaban ƙasa a 2023 | Neptune Prime Hausa