Connect with us

Labarai

An sace ɗalibai ‘yan makaranta 1,683 cikin shekaru 8 a Najeriya – Rahoto

Published

on

Wani rahoto da ƙungiyar ‘Save the Children International’ (SCI) ta fitar, ya bayyana cewa an kai hari kusan makarantu 70 tare da yin garkuwa da yara ‘yan makaranta 1,683 a faɗin Najeriya tsakanin watan Fabrairun 2014 zuwa Disamba 2022.

Rahoton mai taken, “Ilimin da ake kai wa hari: Bita da nazari kan hare-haren da aka kaiwa Makarantu, Malamai, da Almajirai daga sace ‘yan matan Chiɓok, a jihar Borno, Nigeria a 2014.”

Mashawarcin wanda ya ƙirƙiro rahoton, Augustine Mamedu, yayin da yake gabatar da sakamakon a Abuja ranar Alhamis, ya kuma ce an kashe ɗalibai 184 yayin da wasu 88 suka jikkata a cikin wannan lokaci.

Mista Mamedu ya ƙara da cewa an kuma yi garkuwa da malamai kusan 60 da wasu ma’aikatan makarantar; An kashe 14, yayin da aka lalata gine-ginen makarantu 25.

Ya yi nuni da cewa, tun bayan aukuwar lamarin na Chiɓok a watan Fabrairun 2014 da aka yi garkuwa da ‘yan mata kimanin 276, ana samun ƙaruwar satar mutane.

KU KUMA KARANTA: Bayan Shekaru tara, Sojoji sun sake kuɓutar da ‘yar makarantar Chiɓok guda ɗaya

Ya ƙara da cewa rahotannin sun kuma bayyana cewa an samu sauyin yanayi na sace ɗalibai daga Arewa maso Gabas zuwa shiyyar Arewa maso Yamma da Arewa ta Tsakiya.

Ya ce a tsakanin shekarar 2014 zuwa 2022 an kai hari a makarantu biyar a Arewa maso Gabas, 49 a Arewa maso Yamma, 11 a Arewa ta Tsakiya, uku a Kudu maso Kudu, biyu a Kudu maso Yamma.

“Rahoton ya kuma nuna cewa an kai hare-hare kan makarantu 28 a jihar Kaduna a cikin wannan lokaci, inda aka kai wa makarantu 17 hari a ƙaramar hukumar Kajuru kaɗai.

“A jihar Katsina, an rufe makarantu 99, wanda ya shafi ɗalibai 30,870,” in ji shi.

Mashawarcin ya ce rahoton ya ba da shawarar ƙara zuba jari a makarantu masu aminci da aiwatar da tsarin SSD a duk faɗin ƙasar da kuma rufe wuraren kwana da ke cikin al’ummomin da ba su da wuraren tsaro.

Daraktan ƙasar, SCI, Famari Barro, ya yi ƙira ga cikakken aiwatar da sanarwar ‘Safe Schools’, SSD, da aka sanya wa hannu a cikin 2015 don kare yara ‘yan makaranta daga sacewa da sauran munanan ɗabi’u.

Mista Barro ya bayyana cewa SSD wani alƙawari ne na siyasa da Gwamnatin Tarayya ta amince da shi don kare yara, malamai da wuraren makaranta daga hare-hare da amfani da kayan makaranta a lokacin rikici na makamai.

Ya ce a duniya ana ci gaba da kai hare-hare kan ilimi, makarantu, yara, da malamansu da kuma yadda jami’an tsaro ke amfani da kayayyakin makaranta a lokacin rikici.

Ya tunatar da cewa gwamnatin Najeriya ta ɗauki matakai ta hanyar shigar da SSD a cikin gida kuma ta yi alƙawarin aiwatar da ƙa’idodin sanarwar.

Daraktan na ƙasar, ya ce duk da ƙoƙarin da ake yi, hare-haren da ake kai wa harkokin ilimi ya kasance ƙalubale a ƙasar.

Ya bayyana cewa SCI ta ƙaddamar da binciken ne domin duba hare-haren da ake kaiwa makarantu, malamai, da ɗalibai a Najeriya tun bayan harin da aka kai garin Chiɓok a shekarar 2014.

Ya ce an ɗauki matakin ne domin nemo hanyoyin da za a bi wajen ganin an shawo kan al’ummar da abin ya shafa, malamai, da ɗaliban.

Mista Barro ya yaba da kafa cibiyar ba da amsa ga makarantu ta ƙasa, NSSRCC. “Shirin wani mataki ne mai kyau na samar da ingantaccen yanayin koyo ga ‘yan mata, maza da yara masu naƙasa a cikin yanayi na tashin hankali.

“Duk da haka, har sai yaran da ke ƙauyuka masu nisa, waɗanda ke jin barazanar yawan tashin hankali za su iya zuwa makaranta ba tare da tsoro ba, har yanzu da sauran rina a kaba.

“Akwai buƙatar a ƙara yin aiki don hana kai hare-hare, amma kuma a tallafa wa yara da iyalansu, musamman tare da kula da raunuka,” in ji shi.

Da yake mayar da martani, babban sakatare na ma’aikatar ilimi, Andrew Adejo ya bayyana ƙudurin ma’aikatar na tabbatar da tsaro ga kowane yaro ta hanyar aiwatar da SSD.

Mista Adejo, wanda ya samu wakilcin Joseph Achede, mataimakin darakta a fannin ilimin sakandare, ya ce ma’aikatar tana bakin ƙoƙarinta wajen ganin an shawo kan matsalar.

1 Comment

1 Comment

  1. Pingback: Yarinyar da aka sace a Kogi mai shekaru 16 an same ta a Imo | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like