Connect with us

Gobara

An rasa yara 2 da gidaje sama da dubu ɗaya a gobarar sansanin gudun hijira a Borno

Published

on

Ƙananan yara biyu sun rasu gidaje 1,113 sun ƙone a sakamakon gobarar da ta tashi a ranar Laraba a sansanin ’yan gudun hijira da ke yankin Muna Alamdari a ƙaramar hukumar Mafa ta jihar Borno.

Gobarar ta ranar Laraba ta tashi ne a yayin da ake cikin jimamin wadda ta tashi a a ƙarshen mako a Babbar kasuwar Gamborou da ke Maiduguri babban birnin jihar.

Kodinetan Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Jihar Borno a Karamar Hukumar Mafa, Surajo Garba, ya ce yara maza ’yan shekaru bakwai da 10 ne suka rasu a gobarar.

“Gidaje 1,113 sun kone, wasu 50 kuma an yi amfani da su wajen aikin agajin gaggawa,” in ji Surajo.

Ya ci gaba da cewa ba a kai ga gano musabbabin tashin gobarar ba tukuna, haka kuma ba a tantance yawan dabbobi da sauran ƙadarorin da gobarar ta lalata ba.

A jawabinsa bayan ziyarar gani da ido da ya kai sansanin ’yan gudun hijirar da aka samu gobarar, Darakta-Janar na hukumar, Barkindo Muhammad, ya ce wutar ta tashi ne da misalin karfe 6 na safe, sai bayan awanni ’yan kwana-kwana da taimakon sauran hukumomi da jama’ar gari suka shawo kanta.

KU KUMA KARANTA: Gobara ta tashi a kasuwar Gamboru da ke Maiduguri

“Muna jajantawa kuma za mu ba da tallafin gaggawa da suka haɗa da buhu 500 na shinkafa, da barguna da sauran kayayyaki nan take,” in ji shi.

Karo na biyu ke nan da aka samu tashin gobara a sansanin, bayan makamancinsa a watan Fabrairum wanda ya ƙone bukkoki 200.

Wancan lokaci hukumomi sun gobarar ta tashi ne da misalin karfe 11 na safe bayan yawancin mazauna sansanin sun shiga gonaki neman abninci.

Akasarin waɗanda abin ya shafa, babu abin da suka tsira da shi sai kayan jikinsu.

A watan Nuwamban 2022 an samu gobara a sansanin ’yan gudun hijirar da ke Ƙaramar Hukumar Mafa, mako uku bayan tashin watto gobarar a sansanin ’yan gudun hijira a Ƙaramar Hukumar Konduga da kuma wata gobarar a Maiduguri.

A watan Fabrairun 2022, wasu gidaje 100 suka ƙone a sansanin ’yan gudun hijira na Muna El-Badawi da ke Maiduguri a sakamakon fashewar tukunyar iskar gas.

A shekarun da suka wuce ne Hukumar Raya yankin Arewa maso Gabas (NEDC), da ƙungiyoyin agaji da attajirai suka gina dubban gidaje domin sake tsugunar da ’yan gudun hijira, ko da yake har yanzu wasu dubbai na zaman jiran tsammani a matsugunan wucin gadi da aka samar musu.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Boko Haram

An tabbatar da mutuwar masu juna biyu a cikin harin da aka kai a Borno

Published

on

An tabbatar da mutuwar masu juna biyu a cikin harin da aka kai a Borno

An tabbatar da mutuwar masu juna biyu a cikin harin da aka kai a Borno

An kasha aƙalla mutane 18, yayin da wasu 30 suka jikkata bayan wasu jerin hare-haren da ake zargin wasu mata ‘yan ƙunar baƙin wake ne suka kai a jihar Borno a jiya Asabar, in ji shugaban hukumar bayar da agajin gaggawa ta yankin.

Borno dai na cikin shekaru 15 na hare-haren masu iƙirarin kishin Islama wanda ya yi sanadiyar mutuwar dubban mutane tare da raba wasu miliyoyi da humallan su.

Duk da cewa sojojin Najeriya sun rage ƙarfin mayaƙan, amma har yanzu suna kai munanan hare-hare kan fararen hula da kuma wuraren tsaro.

KU KUMA KARANTA:Gobara ta tashi a matatar man Ɗangote

Barkindo Saidu, shine babban Daraktan Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Borno, ya ce wasu da ake zargin ‘yan ƙunar baƙin wake ne suka kai hari daban-daban a wajen bikin aure da jana’iza da kuma asibiti, inda suka kashe mutane tare da jikkata wasu da dama a garin Gwoza.

Saidu ya ce an tabbatar da mutuwar mutum 18, adadin da ya haɗa da ƙananan yara da manya da ma mata masu juna biyu.

Sai dai babu wata ƙungiyar ko wani mutun da ya ɗauki alhakin kai wannan harin.

Boko Haram da ISWAP da ta ɓalle kanta, su ne ƙungiyoyin ‘yan bindiga da suka fi yawan gudanar da ayyukan su a jihar Borno, wani babban yanki na karkara mai girman gaske.

Continue Reading

Gobara

Tinubu ya jajantawa mutanen da gobarar kasuwar Karu ta shafa

Published

on

Tinubu ya jajantawa mutanen da gobarar kasuwar Karu ta shafa

Tinubu ya jajantawa mutanen da gobarar kasuwar Karu ta shafa

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya miƙa saƙon jajensa ga ‘yan kasuwar da shaguna da dukiyoyinsu suka ƙone a gobarar da ta tashi a kasuwar Karu a daren Alhamis.

Sanarwar da hadimin shugaban ƙasar akan harkokin yaɗa labarai, Ajuri Ngilale ya fitar a ranar Juma’a ta ce, shugaban ƙasar ya yi takaicin samun labarin gobarar da ta shafi wani sashe na kasuwar.

Da yammacin ranar Alhamis, gobara ta laƙume wani yanki na kasuwar, inda ta lalata ɗimbim dukiya da sauran kayayyaki masu daraja.

KU KUMA KARANTA:Gobara ta tashi a matatar man Ɗangote

Sanarwar ta ƙara da cewar, shugaban ƙasa na miƙa saƙon jajensa ga ilahirin ‘yan kasuwar da wannan mummunan al’amari ya shafa, sannan yana ba su tabbacin samun tallafi daga gwamnatinsa.

Shugaban ƙasar ya kuma yi ƙira da a riƙa taka tsantsan da ɗaukar matakan kariya, domin kare afkuwar gobara da sauran bala’o’i a nan gaba.

Continue Reading

Gobara

Gobara ta tashi a matatar man Ɗangote

Published

on

Gobara ta tashi a matatar man Ɗangote

Gobara ta tashi a matatar man Ɗangote

Gobara ta tashi da yammacin yau a wani sashe na matatar man Ɗangote da ke kusa da Lekki a Legas.

Jami’an agajin gaggawa sun ɗauki matakin shawo kan lamarin, kuma a cewar rahotannin farko, ba a samu raunuka ba.

Kawo yanzu dai ba a san musabbabin tashin gobarar ba, kuma ana ci gaba da gudanar da bincike don gano girman barnar da aka yi da kuma abin da ya haddasa faruwar lamarin.

Da take mayar da martani kan gobarar a cikin wata sanarwa da Ɗangote ya fitar, mai ɗauke da sa hannun Anthony Chiejina, ƙungiyar ta ce, “Mun yi gaggawar shawo kan wata ‘yar karamar gobara a masana’antar sarrafa iska (ETP), a yau Laraba 26 ga watan Yuni.

KU KUMA KARANTA: Gobara ta kashe jarirai shida a Indiya

“Babu wani dalili na tashin hankali yayin da matatar ta ke aiki kuma babu wani rauni da aka samu ko lahani ga dukkan ma’aikatanmu da ke bakin aiki.”

Matatar dangote wani katafaren aiki ne da ake ginawa wanda ake hasashen zai iya tace ganga 650,000 a kowace rana.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like