Connect with us

Kasashen Waje

Amurka Ta Gargadi Amurkawa Kan Bulaguro Zuwa Najeriya

Published

on

Daga Wakilinmu

Yayin da ake samun karuwar satar mutane da sauran laifuka a Najeriya, Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka tana kira ga Amurkawa da ‘yan kasa biyu da sauran su da su “sake yin shawarar balaguro” zuwa kasar da ke yammacin Afirka.

Shawarwarin Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka kan masu tafiye-tafiye, wanda aka fitar a ranar 4 ga watan Janairun nan, ya yi gargadin cewa “laifuka na tashin hankali – kamar fashi da makami da kai hare-hare da satar motoci da garkuwa da kuma fyade – ya zama ruwan dare a duk fadin kasar.

Satar mutane don neman kudin fansa na faruwa akai-akai, galibi ana kai hari ga ’yan kasa biyu da suka koma Najeriya ziyara, da kuma ‘yan kasar Amurka da ake da masaniyar suna da arziki.

A wannan nan ranar ne kuma, gwamnatin tarayyar Najeriya ta ayyana masu dauke da makamai a matsayin ‘yan ta’adda a hukumance, kamar yadda kamfanin dillancin labaran Faransa ya ruwaito. Ayyanawar ta ba da karin takunkumi da hukunci ga masu laifi da wadanda suka taimaka aka aikata laifin.

Shawarar da Amurka ta bayar ta hada da gargadin “kada ayi tafiya” zuwa jihohin Borno da Yobe da kuma arewacin Adamawa saboda ta’addanci da matsalar garkuwa da mutane, da kuma irin wannan gargadi ga jihohin Bauchi da Gombe da Kaduna da KanodaKatsina da Zamfara saboda sace-sacen mutane.

Yankunan bakin teku kamar jihohin Akwa Ibom da Bayelsa da Kuros Riba da Delta da Ribas – ban da Fatakwal – su ma suna duk cikin jerin “kada ku yi tafiya”.

Kasar da ta fi kowacce yawan al’umma a Afirka ta fuskanci matsalar rashin tsaro, ciki har da yawaitar sace-sacen mutane domin neman kudin fansa. A jihar Kaduna kadai, gwamnati ta ce an yi garkuwa da mutane 1,723 a cikin watanni shida na farkon shekarar 2021, idan aka kwatanta da kusan 2,000 a duk shekarar da ta gabata.

Ni ɗan jarida ne mai zaman kansa. Mawallafi kuma mai sharhi a lamarin yau da kullum.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Kasashen Waje

Trump da Harris sun yi tir da zanga-zangar ƙin jinin Isra’ila

Published

on

Trump da Harris sun yi tir da zanga-zangar ƙin jinin Isra'ila

Trump da Harris sun yi tir da zanga-zangar ƙin jinin Isra’ila

Zanga-zangar na zuwa ne a daidai lokacin da Firai ministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya ke ƙare yaƙin da ƙasar ke yi a Gaza, a yayin jawabi da ya yi a zauren Majalisar dokokin Amurka.

Manyan ‘yan takarar shugabancin Amurka biyu, mataimakiyar shugaban ƙasa Kamala Harris da tsohon shugaban ƙasa Donald Trump, sun ya yi Allah-wadai da zanga-zangar nuna adawa da Isra’ila wacce aka fara ranar Laraba a kusa da ginin majalisar dokokin Amurka.

Zanga-zangar na zuwa ne a daidai lokacin da Firai ministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya ke kare yaƙin da ƙasar ke yi a Gaza, a yayin jawabi da ya yi a zauren Majalisar dokokin Amurka.

Harris, wacce ta yiwu ita ce ‘yar takarar shugaban ƙasa ta jam’iyyar Democrat a zaɓen shekarar nan ta 2024, a cikin wata Sanarwa ta ce “Mun ga ayyukan Allah-wadai daga marasa kishin ƙasa masu zanga-zanga da munanan kalaman ƙiyayya a tashar jirgin ƙasa ta Union Station da ke kusa da ginin majalisar dokoki.”

KU KUMA KARANTA:Joe Biden ya janye daga takarar shugaban Amurka

A gaban tashar, masu zanga-zangar sun cire tutocin Amurka suka sanya Tutocin Falasɗinawa, sannan wani mutum ya yi amfani da jan fenti ya rubuta “Hamas na nan tafe” da manyan harrufa a kan wani babban sassaƙe. Bayan haka Masu zanga-zangar sun ƙona wani mutum-mutumi na Netanyahu da tutar Amurka.

Shi ma Trump, ya rubuta a shafin sa na sada zumunta na Truth cewa “Idan da waɗanda suka ta da tarzoma jiya a Washington ‘yan Republican ne, da yanzu dukkansu na tsare a gidan yari, suna fuskantar hukuncin ɗauri na shekaru 10 zuwa 20. Amma a ƙarƙashin wannan Gwamnatin, babu abin da zai same su.”

A jiya Alhamis Shugaban Amurka Joe Biden ya karɓi baƙuncin Firai Minista Benjamin Netanyahu a fadar White House, don tattaunawa da nufin ganin an cimma yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza da kuma sakin sauran mutanen da Hamas ta yi garkuwa da su, tun bayan harin da ta kai kan Isra’ila ranar 7 ga watan Oktoban bara.

Shugabannin biyu sun gana a Ofishin shugaban kasa, kwana daya bayan da dukkansu sun gabatar da muhimman jawabai. A ranar Laraba Netanyahu ya yi magana a gaban Majalisar Dokokin Amurka, inda ya kare yaƙin da ƙasarsa ke yi da mayaƙan Hamas.

Shi kuwa shugaba Biden ya yi jawabi game da dalilin da ya sa ya yanke shawarar janyewa daga takarar shugaban ƙasa a ranar Lahadin da ta gabata, tare da bayyana goyon bayansa ga mataimakiyarsa.

 

Dukkan shugabannin biyu sun gabatar muhimman jawabai a taƙaice kafin ganawar da suka yi ta sirri.

To sai dai gabanin ganawar, wani babban jami’in gwamnatin ƙasar ya shaidawa manema labarai cewa shugabannin biyun suna aiki kan cikakkun bayanai game da yarjejeniyar tsagaita wuta da kuma sakin waɗanda aka yi garkuwa da su, “wadda suka ce sun yi imani ana a matakin ƙarshe.”

Continue Reading

Kasashen Waje

An ceto wani jariri da aka kashe mahaifiyarsa a wani mummunan farmaki ta sama a Gaza

Published

on

An ceto wani jariri da aka kashe mahaifiyarsa a wani mummunan farmaki ta sama a Gaza

An ceto wani jariri da aka kashe mahaifiyarsa a wani mummunan farmaki ta sama a Gaza

An kashe aƙalla mutane 13 a wasu hare-hare uku da Isra’ila ta kai kan sansanonin ‘yan gudun hijira da ke tsakiyar Gaza cikin daren Juma’a zuwa jiya Asabar, a cewar jami’an kiwon lafiyar Falasɗinu, yayin da ake ganin ana samun ci gaba a tattaunawar tsagaita buɗe wuta a birnin Alkahira.

Daga cikin waɗanda suka mutu a sansanin ‘yan gudun hijiran Nuseirat da kuma sansanin ‘yan gudun hijiran Bureij, akwai yara uku da mace guda, a cewar ƙungiyoyin agajin gaggawa na Falasɗinawa da suka kai gawarwakin zuwa asibitin Al-Aqsa Martyrs da ke kusa. ‘Yan jaridan AP sun kirga gawarwakin mutane 13 a asibitin.

Mace macen baya-bayan nan na zuwa ne adaidai wani lokaci da ake bege gani a yakin da ya addabi Gaza, bayan da tawagar likitocin suka ceto jariri da rai daga wata mace Bafalasdina mai juna biyu da aka kashe a harin na jirgin sama da ya fada kan gidanta da ke Nuseirat da yammacin ranar Alhamis.

An kashe Ola al-Kurd mai tsohon ciki mai shekaru 25 tare da wasu mutane 6 a tashin bam ɗin, amma jami’an agajin gaggawa suka garzaya da su asibitin Al-Awda da ke arewacin Gaza da fatan ceto yaron da ke cikinta. Sa’o’i kaɗan bayan haka, likitoci sun shaida wa kamfanin dillancin labarai na Associated Press cewa an haifi yaron.

Jaririn da har yanzu ba a raɗa masa suna ba yana cikin koshin lafiya, sai dai yana fama da ƙarancin iskar oxygen kuma an sanya shi a cikin na’urar incubator, in ji Dr. Khalil Dajran. Mahaifin yaron ya samu rauni a wannan harin, amma ya tsira da ransa.

KU KUMA KARANTA:Isra’ila ta kashe Falasɗinawa 48 a Gaza a ƙasa da awa ɗaya

Yakin na Gaza, wanda ya ɓarke sanadiyar hari da Hamas ta kai wa kudancin Isra’ila a ranar 7 ga watan Oktoba, ya yi sanadin mutuwar mutane fiye da 38,900, a cewar ma’aikatar lafiyar yankin, wadda ba ta banbance tsakanin mayaka da fararen hula a kidayar ta.
Yakin ya haifar da bala’in jin kai a yankin Falasɗinawa da ke gabar teku, inda aka raba mafi yawan al’ummarta miliyan 2.3 da muhallansu tare da janyo yunwa mai yawa.

Harin na Hamas a watan Oktoba ya kashe mutane 1,200, galibi fararen hula, sannan mayaƙan sun yi garkuwa da kusan mutane 250.
Kimanin mutane 120 ne suka rage a hannu ake garkuwa da su, inda aka yi imanin kusan kashi uku daga cikinsu sun mutu, a cewar hukumomin Isra’ila.

Continue Reading

Kasashen Waje

Babban sakatare na jami’ar Gurguzu a Vietnam, Nguyen Phu Trong, ya rasu

Published

on

Babban sakatare na jami'ar Gurguzu a Vietnam, Nguyen Phu Trong, ya rasu

Babban sakatare na jami’ar Gurguzu a Vietnam, Nguyen Phu Trong, ya rasu

Nguyen Phu Trong, babban sakatare na jam’iyyar gurguzu mai mulki a Vietnam, kuma ɗan siyasa mafi ƙarfi a ƙasar, ya rasu sakamakon rashin lafiya na tsawon watanni, kamar yadda kafafen yaɗa labarai suka faɗa a ranar Juma’a.

KU KUMA KARANTA:Jam’iyar Republican ta tsayar da Donald Trump takarar shugaban ƙasa karo na uku
Ya rasu yana da shekaru 80 a duniya.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like