Connect with us

Labarai

Adadin marasa aikin yi ya ƙaru matuƙa a Najeriya – NBS

Published

on

Hukumar Ƙididdiga ta Najeriya, (NBS), ta bayyana cewar, an samu gagarumar ƙaruwa a mizanin rashin aikin yi a Najeriya a zango na 3 na shekarar 2023.

A rahoton wani bincike data gudanar game da yawan ma’aikatan Najeriya a zango na 3 na shekarar 2023 wanda aka wallafa a Litinin ɗin da ta gabata, hukumar NBS ta bayyana cewar mizanin rashin aikin yi a Najeriya ya yi tashin gwauron zabi daga kaso 4.2 cikin 100 a zango na 2 na shekarar 2023 zuwa kaso 5.0 cikin 100 a zango na 3 na shekarar.

A cewar NBS an samu ragowar ma’aikatan da suka shiga cikin bincike tsakanin mutanen da ke da shekarun yin aiki daga kaso 80.4 cikin 100 a zango na zuwa kaso 79. 5 cikin 100 a zango na 3 na shekarar 2023.

A sharhin da tayi game da ƙididdiga, NBS tace, mizanin auna yawan masu aikin yi da adadin yawan al’umma ya kasance akan kaso 75.6 cikin 100 a zango na 3 na shekarar 2023 inda ya ragu da kaso 1.5% idan aka kwatanta shi dana zango na 2 na wannan shekarar.

“Gamayyar mizanin rashin aikin yi da na ƙarancin guraben aikin yi dake da nasaba da lokaci a matsayin wani kaso na adadin masu aikin yin dake cikin al’umma (lu2) ya karu da kaso 17.3 cikin 100 a zango na 3 na shekarar daga kaso 15.5 cikin 100 na yadda yake a zango na 2 na shekarar.

“Kimanin kaso 87.3 na ma’aikatan da aka gudanar da ƙididdigar akansu a zango na 3 na shekarar 2023 masu sana’ar kansu ne.

“Kason ma’aikatan dake aikin albashi a zango na 3 na shekarar 2023 ya kai kaso 12.7 cikin 100.

Mizanin rashin aikin yin yayi gagarumar karuwa a zango na 3 na shekarar 2023 da kaso 5 cikin 100. An samu karuwar kaso 0.8 cikin 100 daga yadda yake a zango na 2 na shekarar ta 2023.

“Mizanin rashin aikin yin tsakanin mutanen da suka kammala karatun sakandare ya kai kaso 7.8 cikin 100 a zango na 3 na shekarar 2023.”

A cewar Hukumar Kididdigar Najeriya ta NBS, mizanin rashin aikin yi tsakanin matasan dake tsakanin shekara 15 zuwa 24 ya kai kaso 8.6 cikin 100 a zango na 3 na shekarar 2023, inda aka samu karuwar kaso 1.4 cikin 100 akan yadda al’amarin yake a zango na 2 na shekarar.

Mizanin rashin aikin yin a birane ya kai kaso 6.0 cikin 100 a zango na 3 na shekarar 2023, inda aka samu ‘yar karuwa da kaso 0.1 cikin 100 akan yadda yake a zango na 2 na shekarar.

KU KUMA KARANTA:Ƙungiyar NARTO ta dakatar da yajin aikin gamagari, ta umarci ma’aikatan ta su koma bakin aiki

Kididdigar karancin guraben aikin me nasaba da lokaci ta kasance akan kaso 12.3 cikin 100 a zango na 3 na shekarar 2023, inda aka samu ‘yar karuwa da kaso 0.5 cikin 100 yadda yake a zango na 2 na shekarar. hakan na nuni da samun karuwar kaso 1.4 cikin 100 idan aka kwatanta da yadda yake a zangon na 4 na shekarar 2022.

“Kaso 4.1 cikin 100 na wadanda ke tsakanin shekarun yin aiki duk a harkar noman ci da karfi suke a zango na 3 na shekarar 2023.

Kididdigar mutanen dake aikin da ba na hukuma ba a zango na 3 na shekarar 2023 ya kai kaso 92.3 cikin, yayin da a zango na 3 na shekarar ya kasance akan kaso 92.7 cikin 100.

Rahoton ya kara da cewar, adadin matasan da basa aiki ko karatu ko koyon wata sana’a (neet rate) a zango na 3 na shekarar 2023 ya kai kaso 13.7 cikin 100.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Sarkin Gwandu ya naɗa ɗan Buran ɗin Gwandu babba

Published

on

Sarkin Gwandu ya naɗa ɗan Buran ɗin Gwandu babba

Sarkin Gwandu ya naɗa ɗan Buran ɗin Gwandu babba

Daga Haruna Abdulrashid

Shugaban majalisar sarakuna ta jihar Kebbi, Mai martaba Sarkin Gwandu, Manjo-Janar Muhammadu Ilyasu Bashar Mni, ya karrama Shugaban hukumar jin daɗi da walwalar Alhazzai ta ƙasa, Malam Jalal Muhammad Arabi da sarautar (ƊAN BURAN GWANDU BABBA) inda mai martaba sarki ya aike da tawaga zuwa birnin tarayya Abuja domin gabatar da wannan karramawa zuwa ga Malam Jalal Arabi.

Da ya ke jawabi a madadin mai martaba sarkin Gwandu Alhaji Aminu Ahmad, Sarkin Fadan Gwandu ya bayyana cewa mai martaba sarkin Gwandu ya amince da bayar da wannan karramawa ga Malam Jalal ne a bisa jajircewa da kuma taimako da yake yiwa Alhazzan Najeriya tare da haɗin kai da yake bawa shugabanni a kan abin da ya shafi harkar aikin Hajji mussaman a bana.

Shi ma shugaban hukumar jin daɗin da walwalar Alhazai ta jihar Kebbi, Alhaji Faruƙu Musa Yaro Enabo, Jagaban Gwandu, ya bayyana jin daɗin shi matuƙa a kan wannan karramawar da aka yi wa maigidan shi.

Ya kuma yabawa mai martaba Sarkin Gwandu Manjo-Janar Muhammadu Ilyasu Bashar akan yadda yake gabatar da kyakkyawan jagoranci zuwa ga Al’ummar Gwandu.

Wannan bayar da takardar karramawa ta sarautar (ƊAN BURAN GWANDU) Sun haɗa da Alh Aminu Ahmed Sarkin Fadan Gwandu, Alh Aminu Abubakar Gulumbe Uban ƙasar Gulumbe, Alh. Mustapha Ka’oje Sarkin Bargun Ka’oje, Alh Lamiru Shehu Sakataren Sarakunan jihar Kebbi, Alh Faruƙu Musa Yaro Enabo Jagaban Gwandu, Alh Usman Osho da Alh Rilwanu Awwal.

Mai girma Shugaban hukumar Jin daɗi da walwalar Alhazzai ta jihar Kebbi, Malam Jalal Arabi, ya bayyana jin daɗin shi sosai ganin wanan karramawa da ya samu daga masarautar Gwandu.

Ya kuma ce jihar Kebbi ta zama gida a gareshi ganin yadda yake samun karramawa da mutuntawa a jihar ya kuma bayyana mana irin mutunci da zumunci dake tsakanin shi da shugaban hukumar Jin daɗi da walwalar Alhazzai ta jihar Kebbi.

Alh Faruku Musa Yaro Enabo Jagaban Gwandu ya kuma yi godiya da jinjina zuwa ga Maigirma Gwamnan jihar Kebbi His Excellency Comrd Dr. Nasir Idris Ƙauran Gwandu akan irin yadda yayi ɗawainiya ga Alhazzan jihar shi.

Continue Reading

Labarai

Mun gana da shugaba Tinubu mun isar masa saƙon al’umma – Shaikh Bala Lau

Published

on

Mun gana da shugaba Tinubu mun isar masa saƙon al'umma - Shaikh Bala Lau

Mun gana da shugaba Tinubu mun isar masa saƙon al’umma – Shaikh Bala Lau

Daga Idris Umar, Zariya

A ranar Alhamis tawagar malaman Najeriya ta gana da shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu dangane da halin da ƙasa ta ke ciki kan batun zanga-zanga da wasu ke ƙiran a yi dalilin halin matsi da tsadar rayuwa.

Rahoton sun nuna cewa jim kaɗanne bayan kammala ganawar, shugaban ƙungiyar Izala na ƙasa, Shaikh Abdullahi Bala Lau ya shaidawa manema labarai cewa shugaban ƙasa ya karɓi koken da suka je masa da shi.

“Mun faɗa mar halin da al’umma suke ciki na tsadar rayuwa, taɓarɓarewar tsaro da wahalar rayuwa, ya kuma ce dan Allah a ja hankalin al’umma a ba su haƙuri nan gaba kaɗan za a ga sauyi da gyara kan ƙorafe-ƙorafen da ake yi”. In ji Bala Lau.

KU KUMA KARANTA: Zanga-zanga ba gudu ba ja da baya – ‘Yan Najeriya

Daga nan kuma, Shaikh ɗin ya ja hankalin al’umma da su yi haƙuri su cigaba da addu’a, “ba mu da ƙasar da ta fi Najeriya kar mu rusa ƙasarmu da kanmu”. Inji Shaikh Bala Lau.

Continue Reading

Ilimi

Gwamnatin Katsina ta jaddada manufarta na ci gaba da bayar da horo ga malaman makaranta

Published

on

Gwamnatin Katsina ta jaddada manufarta na ci gaba da bayar da horo ga malaman makaranta

Gwamnatin Katsina ta jaddada manufarta na ci gaba da bayar da horo ga malaman makaranta

Daga Idris Umar, Zariya

Kwamishinar kula da ilimin firamare da na Sakandire ne ta bayyana ƙudirin gwamnatin jihar mai ci yanzu na ci gaba da bayar da ƙarin horo ga malamai a faɗin jihar don samar da ƙwararrun malamai da suka iya sarrafa na’ura mai ƙwaƙwalwa da za su yi gogayya da takwarorinsu a faɗin duniya.

Hajiya Zainab Musa Musawa ta bayar da tabbacin hakan ne a lokacin da ta kai ziyarar duba yadda shirin horar da malamai 10,000 da suka haɗa da sabbin ɗauka 7,000 a kan dabarun koyarwa na ƙarni na 20 ke gudana.

Kwamishinar ta kai ziyarar ne a makarantar firamare ta Modoji inda ake gudanar da bayar da horon na yini 3 wanda Ma’aikatar kula da ilimin firamare da na Sakandire, hukumar ilimin bai ɗaya da kuma haɗin gwiwa da shirin bunƙasa ilimi matakin jiha (TESS) suka shirya.

KU KUMA KARANTA: Da ilimi ake samun kowace irin nasara a rayuwa – Dauda Lawal 

Hajiya Zainab Musa Musawa wanda ta zagaya azuzuwa ta kuma tattauna da masu bayar da horon da Kuma malaman, ta bukace su da suyi amfani da lokacin su fahimci Abunda aka koyamasu don bunkasa tsarin koyo da koyarwa a jihar.

A yayin ziyarar dai Kwamishinar ta samu rakiyar Babbar Sakatariya a Ma’aikatar Hajiya Mairo Mohamed Othman, Mai baiwa Gwamna shawarma akan ilimi Nura Sale Katsayal sauran Daraktocin Ma’aikatar.

Bayanin hakan na ƙunshe a cikin wata sanarwa wadda jami’in hudda da jama’a na Ma’aikatar Malam Sani Ɗanjuma Suleiman ya Sanyama hannu a katsina.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like