Kotu a Kano ta yanke wa Amarya hukuncin kisa kan kashe Angonta bayan kwana 9 da aure
Babbar kotun jihar Kano da ke zamanta a Miller Road, ƙarƙashin jagorancin Mai Shari’a Maryam Sabo, ta yanke wa Saudat Idris hukuncin kisa ta hanyar rataya bayan an same ta da laifin kashe mijinta, Salisu Idris, kwanaki tara kacal da ɗaura aurensu.
A lokcin yanke hukuncin, Mai Shari’a Maryam Sabo ta bayyana cewa kotun ta gamsu da hujjoji da shaidun da masu gabatar da ƙara suka gabatar. Ta ce lauyan gwamnati, Barista Lamido Abba Soran Ɗinki, ya gabatar da gamsassun hujjoji tare da shaidu biyu da suka tabbatar da aikata laifin, lamarin da ya sa kotun ta same ta da laifin kisan kai tare da yanke mata hukuncin kisa ta hanyar rataya.
Bayan kammala shari’ar, lauyan gwamnati, Barista Lamido Abba Soran Ɗinki, ya bayyana gamsuwarsa da hukuncin da kotun ta yanke, yana mai cewa an yi adalci bisa hujjojin da aka gabatar.
Sai dai lauyan da ke kare Saudat Idris ya bayyana cewa ba su gamsu da hukuncin ba, yana mai cewa za su ɗaukaka ƙara zuwa Kotun Ɗaukaka Ƙara domin neman a sake duba hukuncin da aka yanke.


