HomeAddiniFarfesa Mansur Yelwa...

Farfesa Mansur Yelwa ya sauka daga limancin masallacin jami’ar ATBU

Tsohon babban limamin Jami’ar Abubakar Tafawa Balewa (ATBU) da ke Bauchi, Farfesa Mansur Isa Yelwa, ya bayyana cewa amincewar da mahukuntan jami’ar suka bai wa ƙungiyar ɗaliban Tijjaniyya (TIMSAN) domin gina masallaci a harabar jami’ar ce ta sa ya yi murabus daga mukaminsa.

Farfesa Yelwa ya ce amincewa da gina masallacin na iya haifar da rarrabuwar kawuna tsakanin ɗalibai da mabiya ƙungiyoyi daban-daban a jami’ar.

Ya bayyana cewa idan aka bai wa Tijjaniyya damar gina masallaci, sauran ƙungiyoyi irin su Ƙadiriyya, Izala, Salafiyya da Shi’a ma za su nemi irin wannan dama, lamarin da ka iya kawo rashin jituwa a jami’ar.

Ku kuma karanta: A kan wayar Android, Matashi a Yobe, ya yi tafiyar kilomita 4, ɗauke da buhun shinkafa a kansa

Tsohon limamin ya ce tun lokacin da ya zama babban limami shekaru 17 da suka gabata, ya yi aiki wajen haɗa kan musulman jami’ar ba tare da nuna bambanci ba, amma ya yi zargin cewa an ba da wannan izini ba tare da tuntubar sa ba.

Ya bayyana cewa ba zai koma mukaminsa ba har sai mahukuntan jami’ar sun janye amincewar da suka bai wa TIMSAN.

Sai dai daraktan hulɗa da jama’a na jami’ar, Zailani Bappa, ya kare matakin da jami’ar ta ɗauka, yana mai cewa an bi doka da ƙa’ida wajen bayar da izinin.

Ya ce jami’ar ba za ta hana duk wani halastaccen aikin addini da ba ya barazana ga zaman lafiya ba, yana mai ƙara da cewa ƙungiyar TIMSAN ba ta nemi gina sabon masallacin Juma’a ba, sai dai filin gudanar da wasu ayyukanta na addini.

Bappa ya kuma bayyana cewa majalisar SHURA ta musulman jami’ar ta shiga cikin tattaunawar da aka yi kafin a amince da buƙatar, yana mai jaddada cewa jami’ar na ci gaba da ƙoƙarin tabbatar da zaman lafiya da haɗin kai tsakanin mabiya addinai da mazhabobi daban-daban.

Get notified whenever we post something new!

spot_img

Create a website from scratch

Just drag and drop elements in a page to get started with Newspaper Theme.

Continue reading

Kotu ta umarci Sheikh Abduljabbar ya gabatar da litattafan da ya yi amfani da su wajen kafa hujja a shari’ar farko

Babbar kotun jihar Kano mai sauraron ƙorafe-ƙorafen ɗaukaka ƙara ta saurari ƙarar da Sheikh Abduljabbar Nasir Kabara ya shigar yana ƙalubalantar hukuncin kisa da Kotun Shari’ar Musulunci ta Kofar Kudu ta yanke masa kan zargin ɓatanci ga Annabi Muhammad...

A kan wayar Android, Matashi a Yobe, ya yi tafiyar kilomita 4, ɗauke da buhun shinkafa a kansa

Matashi a garin Gashuwa ta jihar Yobe, mai suna Umar Aminu Ahmad, wanda aka fi sani da Umar Ɗan Paleti, ya ɗauki buhun shinkafa a kansa, mai nauyin kilogram 100 inda ya yi tafiyar tsawon kilomita 4, don ya...

Katin shedar ɗan ƙasa ya fallasa kwamandojin Boko Haram 7 da suka dawo daga aikin Hajji – Minista

Ministan harkokin cikin gida, Dakta Olubunmi Tunji-Ojo, ya bayyana cewa tsarin tantance bayanan ’yan ƙasa na Hukumar NIMC ya taimaka wajen cafke wasu mutane bakwai da ake zargin manyan kwamandojin Boko Haram da ISWAP ne yayin da suke dawowa...

Enjoy exclusive access to all of our content

Get an online subscription and you can unlock any article you come across.