Online bahislerde yeniliğin ve kazancın buluşma noktası bettilt olmuştur.

Adres güncellemeleriyle sorunsuz bağlantı sağlayan bettilt önemlidir.

Dijital ortamda eğlencenin en güvenilir adresi bettilt oluyor.

HomeLabariA kan wayar...

A kan wayar Android, Matashi a Yobe, ya yi tafiyar kilomita 4, ɗauke da buhun shinkafa a kansa

Matashi a garin Gashuwa ta jihar Yobe, mai suna Umar Aminu Ahmad, wanda aka fi sani da Umar Ɗan Paleti, ya ɗauki buhun shinkafa a kansa, mai nauyin kilogram 100 inda ya yi tafiyar tsawon kilomita 4, don ya ci gasar wayar Android da suka yi.

Wannan lamari ya faru ne a jiya Jumu’a, a unguwar Tsamiya, Zangon Takari. Inda matasan suka yi gasa a kan duk wanda ya ɗauki buhun shinkafa mai nauyin kilogram 100, daga Zangon Takari zuwa Kara (sabuwar kasuwar ‘yan shinkafa), a cikin garin Gashuwa, to zai ba da wayarsa ta Android. Nan take Umar ya ce zai iya, shi ma Umar ya saka wayarsa, a kan idan bai kai ba, shi ma ya ba da wayarsa.

Ku kuma karanta: Katin shedar ɗan ƙasa ya fallasa kwamandojin Boko Haram 7 da suka dawo daga aikin Hajji – Minista

Aka ɗauko buhun shinkafa aka ɗora masa, tun daga Zangon Takari, har zuwa Kara, Umar ya kawo buhun shinkafar nan bai tsaya ba. Nan take aka ba shi waya ƙirar Android da aka yi gasa akai.

A wani faifayin ‘video’ da Neptune Prime ta samu, wanda Assalafy Multimedia take tattauna wa Umar ɗin, ya tabbatar da cewa lallai ya ɗauki buhun shinkafa ya yi tafiyar tsawon kilomita 4, bisa gasa da suka yi a tsakanin su, kuma ya ci wayar Android.

Da ake tambayarsa, kan cewa bayan wayar Android an ba shi dubu 100, sai Umar yace “Ni ba wanda ya ba ni dubu 100. Iya waya ce muka yi gasa a kanta, kuma ita aka ba ni. Sai dai a hanya ta tafiya, mutane sun yi ta jinjina min, wasu suna ba ni kuɗi, kuma hakan shi ne ya ƙara min ƙarfin gwiwa da kuzari har na yi nasara a wannan gasar.

“Lallai ni ban taɓa yin sana’ar dako ba, kawai dai na ga zan iya ne, shi ya sa na yi” inji Umar

Get notified whenever we post something new!

spot_img

Create a website from scratch

Just drag and drop elements in a page to get started with Newspaper Theme.

Continue reading

Allah Ya yiwa fitaccen ɗan wasan Barkwanci, Sani Tumbeleƙe rasuwa

Allah Ya yiwa fitaccen ɗan wasan Barkwanci, Sani Tumbeleƙe rasuwa Rahotanni daga Asibitin Koyarwa na Barau Dikko da ke Kaduna, ya bayyana cewa fitaccen wasan Barkwanci nan Sani Gwarzo Tumbeleƙe rasuwa. Ku kuma karanta: ‘Yar shekaru 24, ta zama ɗaliba ta...

‘Yar shekaru 24, ta zama ɗaliba ta farko da ta kammala karatun Digiri a fannin Shari’a da sakamako mafi daraja

'Yar shekaru 24, ta zama ɗaliba ta farko da ta kammala karatun Digiri a fannin Shari'a da sakamako mafi daraja Wata matashiya mai shekaru 24, Aisha Widad Yahaya, wadda ita ce uwa ga yaro ɗaya kuma matar aure, ta kafa...

An yi jana’izar ‘yan Shi’a 5 da suka rasu a hatsarin mota a hanyar Tattakin Arba’een a Abuja

An yi jana'izar 'yan Shi'a 5 da suka rasu a hatsarin mota a hanyar Tattakin Arba'een a Abuja 'Yan'uwa Musulmi, Almajiran Shaikh Ibraheem Zakzaky (H), sun gudanar da jana'izar 'yan'uwa biyar a muhallin Darur Rahma dake garin Zariya ranar Laraba,...

Enjoy exclusive access to all of our content

Get an online subscription and you can unlock any article you come across.