Online bahislerde yeniliğin ve kazancın buluşma noktası bettilt olmuştur.

Adres güncellemeleriyle sorunsuz bağlantı sağlayan bettilt önemlidir.

Dijital ortamda eğlencenin en güvenilir adresi bettilt oluyor.

HomeLabariBabban Malami a...

Babban Malami a FCE Potiskum, Dakta Mamuda ya rasu, yana da shekaru 62

Babban Malami a FCE Potiskum, Dakta Mamuda ya rasu, yana da shekaru 62

Al’ummar garin Potiskum sun shiga cikin makoki da juyayi na rasuwar Dakta Abdullahi Mamuda, Babban Malami a Kwalejin Ilimi ta Tarayya (FCET), Potiskum.

Dakta Mamuda ya rasu a ranar Laraba yana da shekaru 62 bayan gajeriyar rashin lafiya. Daktan ya rasu ne a Asibitin Legacy Clinic, Potiskum, inda yake karɓar kulawar likita.

Marigayin fitaccen malami ne kuma malami wanda ya yi wa Kwalejin Ilimi ta Tarayya (FCE), Potiskum hidima, a fannoni daban-daban. Tsohon Shugaba ne (Dean) a Tsangayar (School of Technical Education) kuma Malami ne da ake girmama shi sosai saboda gudummawar da ya bayar ga koyarwa, ci gaban ilimi da ci gaban ilimin fasaha.

Ku kuma karanta: Cikin Ruwan Sama, Islamiyyoyi sama da 700 ne suka fito zagayen Mauludin Annabi (SAWW) a Potiskum

Dakta Abdullahi Mamuda yana da digirin digirgir (PhD) a fannin Automobile Engineering, wanda ke nuna jajircewarsa ga ingancin ilimi da ci gaban sana’a a fannin ilimin fasaha.

Duk dai a cikin aikinsa na hidima ga ilimi, Dakta Mamuda shi ne Shugaban Kwamitin Ilimi na Makarantar Tunawa da Hafsatu Gimba, Potiskum, inda ya ba da gudummawa ga ci gaba da gudanar da makarantar.

Fitaccen ɗan jarida kuma mai taimakon al’umma, Dakta Hassan Gimba, Mawallafin Jaridar Neptune Prime ne gina makarantar. Matsayin Dakta Mamuda a matsayin Shugaban Kwamitin Ilimi ya ƙara nuna jajircewarsa wajen tallafawa ci gaban ilimi a cikin al’umma.

Ya rasu, ya bar mata biyu da ‘ya’ya 18, da kuma sauran dangi, abokan aiki, ɗalibai da abokan hulɗa waɗanda ke jimamin rasuwarsa.

Ɗaruruwan al’umma ne cikin juyayi, ciki har da malamai, shugabannin gargajiya, jami’an gwamnati, ɗalibai, abokan aiki, abokai da membobin al’umma, sun halarci sallar jana’izarsa a Fadar Sarkin Potiskum da misalin ƙarfe 5:00 na yamma a ranar Laraba.

Daga cikin waɗanda suka halarci sallar jana’izar akwai Sarkin Potiskum, Alhaji Umaru Bubaram, tare da sauran manyan mutane da membobin al’umma da yawa.

Yawan jama’ar da suka halarci jana’izar ya nuna girmamawa da tausayi da Dakta Mamuda ya samu a rayuwarsa ta hanyar hidimarsa ga ilimi da kuma al’umma baki ɗaya.

Al’umma da dama ne suka bayyana rasuwarsa a matsayin babban rashi ga Kwalejin Ilimi ta Tarayya (FCE), Potiskum, musamman tsangayar ( School of Technical Education), da kuma Makarantar Hafsatu Gimba Memorial, iyalansa, tsoffin ɗalibai da abokan aikinsa.

Za a yi ta tuna wa da Dakta Abdullahi Mamuda saboda shekarun da ya shafe yana hidima ga ilimi, nasarorin da ya samu a fannin ilimi da kuma gudummawar da ya bayar wajen ci gaban ilimin fasaha a Potiskum da ma wasu wurare.

Allah Ya gafarta masa kurakuransa, Ya ba shi hutu na har abada kuma Ya ba iyalansa, abokan aikinsa, dalibansa da masoyansa juriyar jure rashin. Ameen.

Get notified whenever we post something new!

spot_img

Create a website from scratch

Just drag and drop elements in a page to get started with Newspaper Theme.

Continue reading

‘Yansanda da Sojoji sun hana tsoffin Sojoji Zanga-zanga a ma’aikatar tsaro

'Yansanda da Sojoji sun hana tsoffin Sojoji Zanga-zanga a ma’aikatar tsaro ‘Yan sanda da sojoji sun tare tsoffin jami’an tsaro da suka yi ƙoƙarin gudanar da zanga-zanga a Ma’aikatar Tsaro kan batun rashin biyan wasu kuɗaɗen gyaran fansho da suke...

Alaƙa tsakanin Isra’ila da Qatar na ƙara tsami: Isra’ila ta haramta fitar da kayayyakin masana’antun sojinta zuwa Qatar

Alaƙa tsakanin Isra’ila da Qatar na ƙara tsami: Isra'ila ta haramta fitar da kayayyakin masana’antun sojinta zuwa Qatar Rahotanni daga Isra’ila sun ce gwamnatin ƙasar ta ɗauki matakin hana fitar da duk wani samfurin da ya shafi masana’antun sojojinta zuwa...

Amurka ta bayyana mutane 5 da suka kai hare-hare ta intanet a kan muhimman cibiyoyin ta

Amurka ta bayyana mutane 5 da suka kai hare-hare ta intanet a kan muhimman cibiyoyin ta Gwamnatin Amurka ta fitar da wata sanarwa mai cike da ƙayatarwa a ranar Juma’ar da ta gabata, inda ta bayyana sunayen mutane biyar da...

Enjoy exclusive access to all of our content

Get an online subscription and you can unlock any article you come across.