Online bahislerde yeniliğin ve kazancın buluşma noktası bettilt olmuştur.

Adres güncellemeleriyle sorunsuz bağlantı sağlayan bettilt önemlidir.

Dijital ortamda eğlencenin en güvenilir adresi bettilt oluyor.

HomeKisan KaiKotu a Kano...

Kotu a Kano ta yanke wa Amarya hukuncin kisa kan kashe Angonta bayan kwana 9 da aure

Kotu a Kano ta yanke wa Amarya hukuncin kisa kan kashe Angonta bayan kwana 9 da aure

Babbar kotun jihar Kano da ke zamanta a Miller Road, ƙarƙashin jagorancin Mai Shari’a Maryam Sabo, ta yanke wa Saudat Idris hukuncin kisa ta hanyar rataya bayan an same ta da laifin kashe mijinta, Salisu Idris, kwanaki tara kacal da ɗaura aurensu.

A lokcin yanke hukuncin, Mai Shari’a Maryam Sabo ta bayyana cewa kotun ta gamsu da hujjoji da shaidun da masu gabatar da ƙara suka gabatar. Ta ce lauyan gwamnati, Barista Lamido Abba Soran Ɗinki, ya gabatar da gamsassun hujjoji tare da shaidu biyu da suka tabbatar da aikata laifin, lamarin da ya sa kotun ta same ta da laifin kisan kai tare da yanke mata hukuncin kisa ta hanyar rataya.

Bayan kammala shari’ar, lauyan gwamnati, Barista Lamido Abba Soran Ɗinki, ya bayyana gamsuwarsa da hukuncin da kotun ta yanke, yana mai cewa an yi adalci bisa hujjojin da aka gabatar.

Sai dai lauyan da ke kare Saudat Idris ya bayyana cewa ba su gamsu da hukuncin ba, yana mai cewa za su ɗaukaka ƙara zuwa Kotun Ɗaukaka Ƙara domin neman a sake duba hukuncin da aka yanke.

Get notified whenever we post something new!

spot_img

Create a website from scratch

Just drag and drop elements in a page to get started with Newspaper Theme.

Continue reading

Allah Ya yiwa fitaccen ɗan wasan Barkwanci, Sani Tumbeleƙe rasuwa

Allah Ya yiwa fitaccen ɗan wasan Barkwanci, Sani Tumbeleƙe rasuwa Rahotanni daga Asibitin Koyarwa na Barau Dikko da ke Kaduna, ya bayyana cewa fitaccen wasan Barkwanci nan Sani Gwarzo Tumbeleƙe rasuwa. Ku kuma karanta: ‘Yar shekaru 24, ta zama ɗaliba ta...

‘Yar shekaru 24, ta zama ɗaliba ta farko da ta kammala karatun Digiri a fannin Shari’a da sakamako mafi daraja

'Yar shekaru 24, ta zama ɗaliba ta farko da ta kammala karatun Digiri a fannin Shari'a da sakamako mafi daraja Wata matashiya mai shekaru 24, Aisha Widad Yahaya, wadda ita ce uwa ga yaro ɗaya kuma matar aure, ta kafa...

An yi jana’izar ‘yan Shi’a 5 da suka rasu a hatsarin mota a hanyar Tattakin Arba’een a Abuja

An yi jana'izar 'yan Shi'a 5 da suka rasu a hatsarin mota a hanyar Tattakin Arba'een a Abuja 'Yan'uwa Musulmi, Almajiran Shaikh Ibraheem Zakzaky (H), sun gudanar da jana'izar 'yan'uwa biyar a muhallin Darur Rahma dake garin Zariya ranar Laraba,...

Enjoy exclusive access to all of our content

Get an online subscription and you can unlock any article you come across.