Jami’ar Maryam Abacha American University Kano, ta fitar da sanarwar cewa Dr. Nasa’i Gwadabe, Lakcaran da aka lakaɗa wa duka kan zargin lalata da ɗaliba, ba ma’aikacin ta ba ne, sai dai ya yi aiki ne a jami’ar a matsayin ʼvisiting lecturerʼ na tsawon shekara guda, amma wa’adin aikinsa ya ƙare a watan Mayun 2026, kuma ba a sabinta kwantiraginsa ba. Kamar yadda Malam Ali Kakaki na Jami’ar MAAUN ɗin ya sanar.
Ku kuma karanta: Farfesa Mansur Yelwa ya sauka daga limancin masallacin jami’ar ATBU
Kazalika jami’ar ta musanta rahotannin da ke cewa wata ɗaliba ta shafe shekara biyu ba tare da kammala karatu ba, da kuma zargin cewa akwai ɗalibar da ke digiri na biyu da abin ya shafa.
MAAUN ta jaddada cewa tana da manufar hana cin zarafi ta hanyar lalata, tare da buƙatar kafafen yaɗa labarai da jama’a su riƙa bayar da rahotanni bisa sahihan bayanai.


