Babbar kotun jihar Kano mai sauraron ƙorafe-ƙorafen ɗaukaka ƙara ta saurari ƙarar da Sheikh Abduljabbar Nasir Kabara ya shigar yana ƙalubalantar hukuncin kisa da Kotun Shari’ar Musulunci ta Kofar Kudu ta yanke masa kan zargin ɓatanci ga Annabi Muhammad (SAW).
A zaman kotun da aka gudanar, lauyoyin ɓangarorin biyu sun gabatar da hujjojinsu, inda lauyoyin Sheikh Abduljabbar suka roƙi kotun da ta soke hukuncin da aka yanke masa tare da wanke shi daga zargin.
Ku kuma karanta: Farfesa Mansur Yelwa ya sauka daga limancin masallacin jami’ar ATBU
Sai dai lauyoyin gwamnatin jihar sun buƙaci kotun da ta tabbatar da hukuncin da kotun farko ta yanke.
Alƙalin kotun, Mai Shari’a Nasir Saminu, ya umarci a gabatar masa da wasu litattafai da aka yi amfani da su a shari’ar kotun farko domin ci gaba da nazarin ƙarar.
Rahotanni sun ce kotun za ta sanar da ranar da za ta yanke hukunci kan ɗaukaka ƙarar a wani lokaci mai zuwa.


