HomeAddiniKotu ta umarci...

Kotu ta umarci Sheikh Abduljabbar ya gabatar da litattafan da ya yi amfani da su wajen kafa hujja a shari’ar farko

Babbar kotun jihar Kano mai sauraron ƙorafe-ƙorafen ɗaukaka ƙara ta saurari ƙarar da Sheikh Abduljabbar Nasir Kabara ya shigar yana ƙalubalantar hukuncin kisa da Kotun Shari’ar Musulunci ta Kofar Kudu ta yanke masa kan zargin ɓatanci ga Annabi Muhammad (SAW).

A zaman kotun da aka gudanar, lauyoyin ɓangarorin biyu sun gabatar da hujjojinsu, inda lauyoyin Sheikh Abduljabbar suka roƙi kotun da ta soke hukuncin da aka yanke masa tare da wanke shi daga zargin.

Ku kuma karanta: Farfesa Mansur Yelwa ya sauka daga limancin masallacin jami’ar ATBU

Sai dai lauyoyin gwamnatin jihar sun buƙaci kotun da ta tabbatar da hukuncin da kotun farko ta yanke.

Alƙalin kotun, Mai Shari’a Nasir Saminu, ya umarci a gabatar masa da wasu litattafai da aka yi amfani da su a shari’ar kotun farko domin ci gaba da nazarin ƙarar.

Rahotanni sun ce kotun za ta sanar da ranar da za ta yanke hukunci kan ɗaukaka ƙarar a wani lokaci mai zuwa.

Get notified whenever we post something new!

spot_img

Create a website from scratch

Just drag and drop elements in a page to get started with Newspaper Theme.

Continue reading

Farfesa Mansur Yelwa ya sauka daga limancin masallacin jami’ar ATBU

Tsohon babban limamin Jami’ar Abubakar Tafawa Balewa (ATBU) da ke Bauchi, Farfesa Mansur Isa Yelwa, ya bayyana cewa amincewar da mahukuntan jami’ar suka bai wa ƙungiyar ɗaliban Tijjaniyya (TIMSAN) domin gina masallaci a harabar jami’ar ce ta sa ya...

A kan wayar Android, Matashi a Yobe, ya yi tafiyar kilomita 4, ɗauke da buhun shinkafa a kansa

Matashi a garin Gashuwa ta jihar Yobe, mai suna Umar Aminu Ahmad, wanda aka fi sani da Umar Ɗan Paleti, ya ɗauki buhun shinkafa a kansa, mai nauyin kilogram 100 inda ya yi tafiyar tsawon kilomita 4, don ya...

Katin shedar ɗan ƙasa ya fallasa kwamandojin Boko Haram 7 da suka dawo daga aikin Hajji – Minista

Ministan harkokin cikin gida, Dakta Olubunmi Tunji-Ojo, ya bayyana cewa tsarin tantance bayanan ’yan ƙasa na Hukumar NIMC ya taimaka wajen cafke wasu mutane bakwai da ake zargin manyan kwamandojin Boko Haram da ISWAP ne yayin da suke dawowa...

Enjoy exclusive access to all of our content

Get an online subscription and you can unlock any article you come across.