Dan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NDC, Peter Obi, ya buƙaci Shugaba Bola Tinubu da ya dakatar da aiwatar da tsarin kafa ‘yansandan jihohi har sai bayan babban zaɓen shekarar 2027.
Obi ya bayyana haka ne bayan majalisar dokoki ta ƙasa ta amince da kudirin kafa ‘yansandan jihohi domin inganta tsaro da rage nauyin rundunar ‘yansandan ƙasa.
A cikin wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na X, Obi ya ce duk da cewa kafa ‘yansandan jihohi mataki ne mai kyau, akwai fargabar cewa tsarin na iya zama abin amfani na siyasa idan aka fara aiwatar da shi kafin zaɓen 2027.
Tsohon gwamnan jihar Anambra ya ce ya kamata a samar da hukumomin sa ido masu zaman kansu domin hana gwamnoni ko wasu ‘yan siyasa amfani da rundunar wajen murƙushe abokan hamayya.
Obi ya ce babu tabbacin cewa gwamnatin yanzu ba za ta yi amfani da tsarin ‘yan sandan jihohi wajen tasiri kan zaɓen 2027 ba, saboda haka ya nemi a jinkirta aiwatar da shi har bayan zaɓen.
Sai dai masu goyon bayan tsarin suna ganin cewa kafa ‘yansandan jihohi zai taimaka wajen inganta tattara bayanan sirri, kusantar jami’an tsaro da al’umma da kuma saurin magance matsalolin tsaro, yayin da masu adawa ke fargabar yiwuwar amfani da su don manufofin siyasa.


