HomeSiyasaObi ya bukaci...

Obi ya bukaci Tinubu ya dakatar da shirin kafa ‘yasandan jihohi sai bayan zaɓen 2027

Dan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NDC, Peter Obi, ya buƙaci Shugaba Bola Tinubu da ya dakatar da aiwatar da tsarin kafa ‘yansandan jihohi har sai bayan babban zaɓen shekarar 2027.

Obi ya bayyana haka ne bayan majalisar dokoki ta ƙasa ta amince da kudirin kafa ‘yansandan jihohi domin inganta tsaro da rage nauyin rundunar ‘yansandan ƙasa.

A cikin wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na X, Obi ya ce duk da cewa kafa ‘yansandan jihohi mataki ne mai kyau, akwai fargabar cewa tsarin na iya zama abin amfani na siyasa idan aka fara aiwatar da shi kafin zaɓen 2027.

Tsohon gwamnan jihar Anambra ya ce ya kamata a samar da hukumomin sa ido masu zaman kansu domin hana gwamnoni ko wasu ‘yan siyasa amfani da rundunar wajen murƙushe abokan hamayya.

Obi ya ce babu tabbacin cewa gwamnatin yanzu ba za ta yi amfani da tsarin ‘yan sandan jihohi wajen tasiri kan zaɓen 2027 ba, saboda haka ya nemi a jinkirta aiwatar da shi har bayan zaɓen.

Sai dai masu goyon bayan tsarin suna ganin cewa kafa ‘yansandan jihohi zai taimaka wajen inganta tattara bayanan sirri, kusantar jami’an tsaro da al’umma da kuma saurin magance matsalolin tsaro, yayin da masu adawa ke fargabar yiwuwar amfani da su don manufofin siyasa.

Get notified whenever we post something new!

spot_img

Create a website from scratch

Just drag and drop elements in a page to get started with Newspaper Theme.

Continue reading

Kotu ta soke rajistar jam’iyyar NDC

Babbar kotun tarayya da ke Lokoja a jihar Kogi ta soke hukuncin da ta yanke a baya wanda ya umarci hukumar zabe mai zaman kanta (INEC) ta yi wa jam’iyyar NDC rajista a matsayin jam’iyyar siyasa kamar yadda jaridar...

NANS Shiyya ta Arewa Maso Yamma da NEARLS Sun Kulla Yarjejeniyar Fahimtar Juna ta Shekaru Uku

Daga Idris Umar, Zaria Ƙungiyar Ɗaliban Najeriya (NANS) Shiyya ta A (Arewa maso Yamma) da National Agricultural Extension and Research Liaison Services (NEARLS) sun rattaba hannu kan Yarjejeniyar Fahimtar Juna (MoU) ta tsawon shekaru uku domin bunƙasa kasuwancin noma, ƙarfafa...

Shugaba Tinubu, ya shawarci ‘yan Najeriya da su sanya idanu kan yadda gwamnatocin jihohi da na ƙananan hukumomi ke kashe kuɗaɗe

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya bukaci kafafen yada labarai su rika sanya ido ga jihohi da kananan hukumomi kan yadda suke amfani da kudaden da suke karba daga gwamnatin tarayya. Tinubu ya bayyana hakan ne a ranar Juma’a yayin...

Enjoy exclusive access to all of our content

Get an online subscription and you can unlock any article you come across.