Tsohon babban limamin Jami’ar Abubakar Tafawa Balewa (ATBU) da ke Bauchi, Farfesa Mansur Isa Yelwa, ya bayyana cewa amincewar da mahukuntan jami’ar suka bai wa ƙungiyar ɗaliban Tijjaniyya (TIMSAN) domin gina masallaci a harabar jami’ar ce ta sa ya yi murabus daga mukaminsa.
Farfesa Yelwa ya ce amincewa da gina masallacin na iya haifar da rarrabuwar kawuna tsakanin ɗalibai da mabiya ƙungiyoyi daban-daban a jami’ar.
Ya bayyana cewa idan aka bai wa Tijjaniyya damar gina masallaci, sauran ƙungiyoyi irin su Ƙadiriyya, Izala, Salafiyya da Shi’a ma za su nemi irin wannan dama, lamarin da ka iya kawo rashin jituwa a jami’ar.
Ku kuma karanta: A kan wayar Android, Matashi a Yobe, ya yi tafiyar kilomita 4, ɗauke da buhun shinkafa a kansa
Tsohon limamin ya ce tun lokacin da ya zama babban limami shekaru 17 da suka gabata, ya yi aiki wajen haɗa kan musulman jami’ar ba tare da nuna bambanci ba, amma ya yi zargin cewa an ba da wannan izini ba tare da tuntubar sa ba.
Ya bayyana cewa ba zai koma mukaminsa ba har sai mahukuntan jami’ar sun janye amincewar da suka bai wa TIMSAN.
Sai dai daraktan hulɗa da jama’a na jami’ar, Zailani Bappa, ya kare matakin da jami’ar ta ɗauka, yana mai cewa an bi doka da ƙa’ida wajen bayar da izinin.
Ya ce jami’ar ba za ta hana duk wani halastaccen aikin addini da ba ya barazana ga zaman lafiya ba, yana mai ƙara da cewa ƙungiyar TIMSAN ba ta nemi gina sabon masallacin Juma’a ba, sai dai filin gudanar da wasu ayyukanta na addini.
Bappa ya kuma bayyana cewa majalisar SHURA ta musulman jami’ar ta shiga cikin tattaunawar da aka yi kafin a amince da buƙatar, yana mai jaddada cewa jami’ar na ci gaba da ƙoƙarin tabbatar da zaman lafiya da haɗin kai tsakanin mabiya addinai da mazhabobi daban-daban.


