Connect with us

Labarai

Ƙungiyoyin dattawan arewa da na Ibo, sun koka kan yawan yawace-yawacen Tinubu

Published

on

Daga Ibraheem El-Tafseer

Ƙungiyar dattawan arewacin Najeriya da takwararta ta Ohanaeze Ndigbo mai kare muradun al’ummar Igbo da wasu ƙungiyoyin farar hula sun bayyana rashin jin daɗinsu game da tafiya zuwa Paris da shugaba Bola Ahmad Tinubu ya yi daidai lokacin da ƙasar ke fama da ƙaruwar matsalar tsaro.

A ranar Laraba 24 ga watan Janairu ne shugaba Tinubu ya tafi zuwa Faransa domin wata ziyara ta ƙashin kai.

Wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban, Ajuri Ngelale ya fitar gabanin tafiyar, ta ce Tinubu zai koma Najeriya cikin makon farko na watan Fabarairu.

Sai dai ƙungiyoyin a hirarsu da jaridar Daily Trust sun koka cewa babu gaskiya cikin sanarwar tafiyar la’akari da yadda aka ƙira tafiyar ta “ƙashin kai”.

Matakin ƙungiyoyin na zuwa ne bayan da shi ma tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar ya soki Tinubu inda ya bayyana shakku game da maƙasudin tafiyar tasa zuwa Faransa yayin da ake fuskantar ƙaruwar matsalar ‘yan bindiga da sauran matsalolin tsaro da ke ci gaba da ta’azzara.

KU KUMA KARANTA: Ganganci ne Atiku ya ce Tinubu ba ya aikinsa yadda ya kamata – Fadar shugaban Najeriya

Sai dai Fadar shugaban ƙasar ta ce duk da cewa Tinubu ba ya ƙasar, yana aiki tuƙuru domin kawo sauƙin matsalolin kuma yana bai wa hukumomin tsaro dukkanin goyon bayan da suke buƙata domin samun nasara kan masu aikata miyagun laifuka da nufin fitar da Najeriya daga halin rashin tsaron da take ciki.

Tinubu dai ya sa ƙafa ya fice daga ƙasar yayin da ake tsokaci game da jerin hare-haren da aka kai a Filato da sace-sacen jama’a a Abuja, babban birnin ƙasar da kuma hari na baya-bayan nan na sace ɗalibai da malaman makaranta a jihar Ekiti da ke kudu maso yammacin Najeriya.

Ƙungiyar dattawan arewacin Najeriyar ta ce tafiyar ta Tinubu zuwa Paris a irin wannan yanayi da ake ciki a kasar manuniya ce cewa shugaban ya duƙufa ne wajen cimma ƙudurorinsa na kashin kai a maimakon bai wa yan Najeriya kwarin gwiwa a lokacin da suke bukatar hakan.

Daraktan yada labarai na ƙungiyar, Abdulazeez Sulaiman ya ce ƙungiyar tana ganin matakin na shugaban ƙasar na tabbatar da damuwar da ake nunawa cewa Najeriya ta faɗa cikin matsalar rashin shugabanci na gari da rashin nuna damuwa da tausayi.

A nata ɓangaren, ƙungiyar Ohanaeze Ndigbo ta yi allah-wadai da tafiyar ta shugaba Tinubu zuwa Paris a halin taɓarɓarewar tsaro da sauran ƙalubale da ake ciki.

Babban sakataren kungiyar, Mazi Okechukwu Isiguzoro ya ce bulaguron da Tinubu ya yi na zuwa ne a lokacin da ƙasar ke fuskantar ƙalubalen tattalin arziƙi.

Isiguzoro ya yi ƙira ga Tinubu da ya yi wa ‘yan Najeriya bayani dalilin yin irin waɗannan tafiye-tafiye.

Shi ma shugaban ƙungiyar tabbatar da jagoranci na gari, GGT, Mista Tunde Salman ya ce da alama shugaba Tinubu ya bai wa wasu manyan jami’ai har da mataimakin shugaban ƙasa damar tafiyar da al’amuran.

Ya ba da misali da wani ƙwarya-ƙwaryan taro da aka shirya kan tsaro game da ƙaruwar matsalar a arewacin Najeriya, inda mataimakin shugaban ƙasa da ministocin tsaro suka zama masu taka rawa sosai a taron.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Shugabannin soja na yankin Sahel suna gudanar da taro a Nijer, yayin da ECOWAS ke taro a Najeriya

Published

on

Shugabannin soja na yankin Sahel suna gudanar da taro a Nijer, yayin da ECOWAS ke taro a Najeriya

Shugabannin soja na yankin Sahel suna gudanar da taro a Nijer, yayin da ECOWAS ke taro a Najeriya

Afirka ta Yamma mai rarrabuwan kai ta gudanar da tarukan ƙolin shugabannin ƙasa guda biyu a ƙasashe daban-daban biyu a ƙarshen makon, inda aka gudanar da taro farko ranar Asabar a Nijar tsakanin shugabannin mulkin soja na yankin Sahel.
A gefe guda kuma za a gudanar da wani taron ƙoli ranar Lahadi a Najeriya inda shugabannin sauran ƙasashe mambobin ƙungiyar tattalin arziƙin yankin ta ECOWAS za su hallara.

Taron ƙolin da ake yi yau Asabar a Yamai babban birnin Jamhuriyar Nijar, zai kasance karo na farko tsakanin shugabannin sojojin sabuwar ƙungiyar haɗin kan yankin Sahel wato Alliance of Sahel States ko kuma AES.

Mali, Burkina Faso da Nijar su ne suka kafa yarjejeniyar kare juna a watan Satumba, waɗanda suka bar babbar ƙungiyar ECOWAS a cikin watan Janairu.

Ficewar su daga ECOWAS, wani ɓangaren ya samo asali ne daga zargin da suke yi cewa Paris tana yiwa ƙungiyar katsalandan kana ba ta ba da taimakon da ya kamata a yaƙi da masu iƙirarin yaƙin jihadi.

Ficewar ta sa ƙasashen uku sun janye kansu daga Faransa da ta yi musu mulkin mallaka, suka kori sojojin Faransa masu yaƙi da masu iƙirarin jihadin kana suka juya zuwa ga ƙasashen da suke ƙira da aminan gaskiya, da suka haɗa da Rasha da Turkiya da kuma Iran.

KU KUMA KARANTA:Shugabannin Nijar, Mali da Burkina Faso sun kafa ƙungiyar haɗaka

Idan aka yi la’akari da munanan tashe-tashen hankula na ‘yan jihadi da ƙasashen uku ke fuskanta, “yaƙin da ta’addanci” da “ƙarfafa haɗin gwiwa” za su kasance kan ajandar taron ƙolin na yau Asabar, a cewar fadar shugaban ƙasar Burkina Faso.

Taron ƙolin da za a gudanar ranar Lahadi a Abuja zai ba shugabanni a ƙasashen ECOWAS damar tattaunawa a kan irin alaƙa da za su ƙulla da ƙungiyar ta AES.

Bayan wasu tarurrukan da suke yi tsakanin ƙasashe biyu, shugabannin uku na yankin Sahel sun yi taro a karon farko tun bayan da suka hau karagar mulki ta hanyar juyin mulki tsakanin shekarar 2020 zuwa 2023.

Continue Reading

Labarai

Nan da 2030 za a fuskanci matsananciyar yunwa a Nijeriya — Majilisar Ɗinkin Duniya

Published

on

Nan da 2030 za a fuskanci matsananciyar yunwa a Nijeriya — Majilisar Ɗinkin Duniya

 

Nan da 2030 za a fuskanci matsananciyar yunwa a Nijeriya — Majilisar Ɗinkin Duniya

Majalisar Ɗinkin Duniya ta yi gargaɗin cewar ‘yan Najeriya miliyan 82, kimanin kashi 64 na ‘yan ƙasar ka iya fuskantar matsalar yunwa nan da shekarar 2030.

Haka kuma MƊD ta yi ƙira da gwamnatin ƙasar ta magance matsalar sauyin yanayi da matsalar ƙwari da sauran abubuwan da yi wa harkar noma barazana.

Jaridun Najeriya sun ambato jami’in Majalisar Ɗinkin Duniyar, Taofiq Braimoh – wanda ya wakilci kodinetan ayyukan jin ƙai na hukumar abinci da ayyukan noma na majalisar na bayyana haka lokacin da yake jawabi kan matsalolin ƙarancin abinci a taron ƙaddamar da shirin bunƙasa ayyukan noma na ‘CropWatch’ a birnin Abuja.

KU KUMA KARANTA:Majalisar Ɗinkin Duniya ta yi maraba da sakin yara 21 da aka yi garkuwa da su

Mista Braimoh ya ce akwai buƙatar gwamnatin Najeriya ta ɗauki matakan da suka dace cikin gaggawa don magance matsalar.

“Gwamnatin Najeriya tare da haɗin gwiwa masu ruwa da tsaki, sun gudanar da bincike na shekara-shekara da suka saba gudanarwa kan abinci. Sakamakon binciken ya tayar da hankali, kimanin mutum miliyan 82 ne za su fuskanci yunwa nan da 2030,” kamar yadda Jaridun ƙasar suka ambato Braimoh na bayyanawa.

Ya ci gaba da cewa matsalar rashin abinci da ƙasar ke fama da shi, baya rasa nasaba da matsalar sauyin yanayi da duniya ke fama da ita, da matsalar ƙwari da wasu abubuwa da ke yi wa harkar noma barazana a ƙasar.

Hasashen na Majalisar Ɗinkin Duniyar na zuwa ne a daidai lokacin da ƙasar ke fama da matsalar tsadar abinci, lamarin da ya tilasta wa gidaje da dama haƙura da sayen abincin da suka saba ci.

A cikin rahotonta baya-bayan nan, hukumar ƙididdigar ƙasar ta ce farashin abinci a ƙasar ya ƙaru zuwa kashi 40.66 a watan Mayu, matakin da aka jima ba a ga irinsa ba.

Continue Reading

Labarai

Yarjejeniyar Auren Jinsi: Gwamnatin Najeriya za ta kai jaridar Daily Trust kotu

Published

on

Yarjejeniyar Auren Jinsi: Gwamnatin Najeriya za ta kai jaridar Daily Trust kotu

Yarjejeniyar Auren Jinsi: Gwamnatin Najeriya za ta kai jaridar Daily Trust kotu

Daga Idris Umar, Zariya

Gwamnatin tarayyar Najeriya ta ce za ta maka jaridar Daily Trust a kotu, tare da shigar da ƙorafi game da ita, a gaban ƙungiyar masu gidajen jarida ta Najeriya saboda abin da ta ƙira ”yaɗa kalaman neman tayar da rikici da karya aikin jarida”

Ministan yaɗa labaran Najeriya, Mohammed Idris ya ce gwamnatin tana sane da yadda a cikin ‘yan watannin baya, jaridar Daily Trust ke yaɗa labaran da ke neman gogawa gwamnatin kashin kaji.

Da ya ke magana a wajen wani taron manema labarai a ranar Asabar, ministan yaɗa labaran ya kafa hujja da labaran da jaridar Daily Trust ta wallafa a game juyin mulkin Nijar, da wanda ya ce jaridar ta rubuta a kan shirin sauya sunan titin Murtala Muhammad da ke Abuja zuwa Wole Soyinka da kuma na baya bayan nan a game da sanya hannu a kan yarjejeniyar da ta shafi amincewa da auren jinsi.

KU KUMA KARANTA: Alaƙar soyayya tsakanin jinsi ɗaya ta haramta a Iraƙi

Ya yi bayanin cewa a dukkan labaran, gwamnatin ta gano yadda jaridar ta bayar da rahoto ba tare da gabatar da hujja ko shaidun zargin da ta yi ba, lamarin da kuma gwamnatin ke kallo a matsayin wani yunƙuri na wallafa ƙarya domin tunzura jama’a.

Ya ce: ‘’Ba mu taɓa tunanin Daily Trust da mutanen da ke da ita za su kai wannan mataki ba wajen neman tayar da rikici a ƙasar nan, ta hanyar zargin cewa gwamnati ta sanya hannu a kan yarjejeniyar tallata auren jinsi. Wannan tsabar zalunci ne saboda babu wannan tanadi a cikin yarjejeniyar.’’

Ministan ya koka da yadda wannan labarin ya janyo huɗuba mai zafi daga wasu malaman addini da kuma jefa jama’a cikin halin ɗarɗar, wanda kuma ya ce jaridar ce ta janyo.

KU KUMA KARANTA: Malaman addini a Malawi sun yi zanga-zangar nuna rashin amincewa da auren jinsi

Saboda haka, ministan ya ce ‘’Gwamnatin tarayya za ta bi duk hanyoyin da doka ta amince da su, domin neman haƙƙi a kotu.’’

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like