Connect with us

Siyasa

Zaben APC: Bola Tinubu Ya Buƙaci Abokan Karawarsa Da Su Haɗa Kai Domin Binne Jam’iyyar PDP

Published

on

Daga; USMAN NASIDI, Kaduna.

DAN takarar kujerar shugabancin Kasar Najeriya a karkashin Jam’iyyar APC, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu ya buƙaci sauran ‘yan takarar da suka kara da shi a zaben fidda gwani na Jam’iyyar da su zo su hada kai domin ciyar da kasar gaba tare da kara karfafa Jam’iyyar a babban zaben da ke tafe a shekarar 2023, domin murkushe Jam’iyyar adawa ta PDP.

Tsohon Gwamnan Jihar Legas, Bola Ahmed Tinubu ya bayyana hakan ne a jawabin da ya gabatar jim kadan bayan bayyana shi a matsayin wanda ya yi nasarar lashe zaben fidda gwani na Jam’iyyar ta APC da Kuri’u 1271 a babban taron Jam’iyyar da ya gudana a filin wasa na Eagle Square dake garin Abuja a ranar laraba.

Ya kara da cewa wannan ranar da aka bayyana shi a matsayin zababben dan takarar a matsayin wata babbar rana a bisa kudirinsa na ganin cewa ya zama Shugaban Kasar Najeriya a shekarar 2023, kuma wannan zaben da aka yi wacce ya yi nasarar zama dan takarar Jam’iyyar na nuni da cewa nasara tasu ce a zaben duka gari mai zuwa domin alamu sun tabbatar da cewa shi ne dan takarar da zai yi nasara a matsayin Shugaban Kasar.

Ya ce ” a wasu yan kwanakin baya, ada Shugaban Jam’iyyar Abdullahi Adamu yaso ya kashe Jam’iyyar ta hanyar neman kakaba mana wani dan takara a matsayin wanda aka amince da shi da sunan an yi sulhu, toh amma yanzu na tabbata al’amura zasu daidaita domin kasancewa ta zababben dan takarar Jam’iyyar na nuni da cewa nasara ce ke biye da mu kuma wacce za ta karya Jam’iyyar adawa ta PDP.”

“A yanzu ina matukar Jindadin da farin ciki bisa wannan karamci da aka yi mun na tsayar da ni dan takarar Jam’iyyar, kuma ina mai Jinjinawa abokan karawa ta bisa kokarin da suka yi, amma ina rokonsu da su dawo su zo mu hada kai domin ganin mun samu cikakken hadin kai ta yadda zamu karasa murkushe Jam’iyyar PDP ta mutu na har abada a zaben duka gari a shekarar 2023.”

“Naji mamakin yadda aka yi Shugaban Majalisar Dattawa Sanata Ahmad Lawan ya nemi karawa da ni bayan na fi shi komai da cancanta kuma ni ba sa’ansa ba ne a harkar Siyasa, toh amma na jinjina masa bisa kokarin da ya yi na raya Kasa da Jam’iyyarmu ta APC a yayin gudanar da harkokinsa a matsayin Shugaban Majalisar.”

“Jam’iyyar PDP ba ta da wani abin da za ta yi tutiya da shi duba da irin yadda ta yi watse da damar ta a shekaru goma sha shida da suka yi a mulki, kuma suka bar ayyuka da dama ba tare da kammalawa ba, sannan ta kawo yunwa, talauci da rashin tsaro ga al’ummar kasar, don haka za mu yi kokarin magance duk wadannan matsalolin idan muka shiga gidan Gwamnati.”

“Babu wani sauran abun da ya ragewa Jam’iyyar PDP illa mu fatattake ta, kana mu karasa kashe ta a zabe mai zuwa idan lokaci ya yi, saboda haka duk yan takarar da muka kara da su, su zo muyi tafiya tare don mu kaiga cimma wannan burin na mu na ganin bayan Jam’iyyar adawar kuma mu samarwa kasarmu mafita daga cikin wannan halin kangin da muke ciki na tsananin rayuwa da talauci.” Inji Tinubu

Dan takarar Jam’iyyar APC na Shugaban Kasa, ya yaba da kwazon mataimakin Shugaban Kasar Najeriya, Farfesa Yemi Osinbajo ya yi, kana tare da shugaban Majalisar Dokokin Tarayyar Najeriya Honarabul Femi Gbajiamela da zuri’arsa domin ganin sun taimaka wajen samun nasararsa a wannan zaben fidda gwanin.

Acewarsa, duk wadanda ada basu mara masa baya ba, basu da wani abun damuwa ko fargaba dangane da yin hakan domin shi ya yafe musu kuma bai riki kowa a rai ba saboda haka za su iya zuwa su tafi tare a wannan tafiyar ta shi domin samun nasarar ciyar da kasar gaba baki daya duk da cewa bai yi zaton masu zaben yan takarar ba za su zabe shi a matsayin dan takarar Jam’iyyar.

Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, ya jinjinawa masu zaben yan takarar wadanda akalla sun samu kwanaki uku zuwa hudu da zummar ganin sun gudanar da harkokin siyasarsu na zaben yan takarar da suke so, don haka ba shi da wani abun da zai iya basu ko yi musu face ya yi musu addu’a da fatan alheri.

1 Comment

1 Comment

  1. Pingback: PDP ta maka Tinubu kotu bisa zargin safarar miyagun ƙwayoyi | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Siyasa

APC ta dakatar da ɗan Majalisa kan cin amana a Zamfara

Published

on

APC ta dakatar da ɗan Majalisa kan cin amana a Zamfara

Jam’iyyar APC reshen Jihar Zamfara ta dakatar da Ɗan Majalisar Wakilai, Aminu Jaji bisa wasu zarge-zargen da ake yi masa na cin amanar jam’iyyar.

Sakataren Yaɗa Labarai na Jam’iyyar APC na Jihar, Malam Yusuf Idris ne ya sanar da dakatarwar a wani taron manema labarai a Gusau a ranar Juma’a.

Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa, Jaji yana wakiltar mazaɓar Ƙaura-Namoda/Birnin-Magaji a Majalisar Wakilai a ƙarƙashin jam’iyyar APC.

Idris ya ce wasu zarge-zargen da ake yi wa Ɗan Majalisar sun haɗa da aikata rashin gaskiya da rashin zuwa tarurrukan jam’iyyar da kuma sauran ayyuka.

KU KUMA KARANTA: Kotun Najeriya ta bayar da umarnin dakatar da asusun banki fiye da dubu 1

Ya ce, matakin ya biyo bayan sanarwar dakatarwar da aka yi wa Jaji daga shugabannin jam’iyyar APC na mazaɓar Birnin-Magaji bisa zargin cin amanar jam’iyyar da dai sauran abubuwan da suka saɓa wa jam’iyyar.
Idris ya ce, “Kwamitin zartaswa na jam’iyyar APC na ƙaramar hukumar Birnin Magaji ne ya miƙa sanarwar dakatarwar zuwa hedikwatar jam’iyyar APC ta jihar.

Bayanai sun ce kwamitin zartaswar jam’iyyar APC na jihar ya gudanar da taron gaggawa a sakatariyar jam’iyyar da ke Gusau a ranar Juma’a 17 ga watan Mayu, 2024, inda aka gabatar da batun dakatar da Jaji ga ‘yan majalisar zartarwar jihar.

Continue Reading

Labarai

Tsohon gwamnan Katsina, Shema ya sauya sheƙa zuwa APC

Published

on

Tsohon gwamnan jihar Katsina, Ibrahim Shema, a hukumance ya koma jam’iyyar APC Mai mulki a jihar.

Shema, ya kasance gwamnan jihar a tsakanin shekarar 2007 zuwa 2015, a ƙarƙashin jam’iyyar PDP.

Tsohon gwamnan ya yi rajista ne a ofishin jam’iyyar na mazaɓar Shema, ƙaramar hukumar Dutsin-ma, inda shugaban jam’iyyar na jihar, Sani Aliyu-Daura ya ba shi katin zama ɗan jam’iyyar APC.

Lambar katin Shema ta zama ɗan jam’iyyar ita ce: 26551.

KU KUMA KARANTA:Gwamnatin Yobe za ta mayar da kwale-kwalen Dufuna mai shekaru 8,000 zuwa cibiyar yawon buɗe ido

Malam Aliyu-Daura ya yabawa Gwamna Dikko Raɗɗa da kuma tsohon gwamnan jihar Aminu Masari wanda ya gada, a bisa rawar da suka taka wajen ganin Shema ya sauya sheƙa.

Don haka ya tabbatar wa tsohon gwamnan cewa za a yi masa adalci kamar kowane ɗan jam’iyya.

Shugaban ma’aikata na Raɗɗa, Jabiru Abdullahi-Tasuri, shi ne ya miƙa katin zama ɗan jam’iyya ga Shema a madadin gwamnan a jiya Alhamis a Dutsin-ma.

Continue Reading

Labarai

Fusatattun matasa sun lakaɗawa kwamishina duka a wajen zaɓen fidda gwani

Published

on

Banji Ajaka, kwamishinan lafiya na jihar Ondo, ya gamu da fushin matasa a jiya Asabar yayin da ake gudanar da zaɓen fidda gwani na gwamna na jam’iyyar APC mai mulki a jihar.

Daily Trust ta gano cewa Dakta Ajaka, wanda ke Mazaɓar Ugbo 3, a ƙaramar hukumar, ana zarginsa da ɓoye takardar sakamakon zaɓen.

Shaidu sun tabbatar da faruwar lamarin a wata tattaunawa da suka yi da manema labarai, inda suka yi zargin cewa fusatattaun matasan ‘ya’yan jam’iyyar APC ne da ke adawa da tsarin da aka bi wajen gudanar da zaɓen.

Ɗaya daga cikin waɗanda suka shaida lamarin, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya bayyana cewa rikicin ya faro ne lokacin da ‘yan ɗaya ɓangaren na jam’iyyar suka buƙaci ganin takardar sakamakon zaɓen na fidda gwani.

KU KUMA KARANTA:An yi jana’izar tsohon gwamnan Ondo, Rotimi Akeredolu

“Sun fusata ne suka buƙaci jami’in zaɓe ya ba su takardar sakamakon zaɓen sai kuwa ya ce ta na wajen Ajaka.

“Don haka suka yi masa duka a wurin, inda kuma garinsu ne. Jama’a sun fusata sosai da lamarin, inda rigimar ta ƙare a wajen.”

Da yake tabbatar da faruwar lamarin, Dakta Ajaka ya ce an zarge shi ne da riƙe takardar sakamakon zaɓen.

Ya yi bayanin cewa a lokacin da yake ƙoƙarin bayyana kansa, ’yan daban sun auka masa inda suka yi masa mugun duka.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like