Za a yi babban taron Majalisar Ɗinkin Duniya don iganta ci gaba

0
66
Za a yi babban taron Majalisar Ɗinkin Duniya don iganta ci gaba

Za a yi babban taron Majalisar Ɗinkin Duniya don iganta ci gaba

Taron Majalisar Ɗinkin Duniya na nan gaba wani lamari ne mai ban sha’awa wanda ya jawo hankalin shugabannin duniya, sanannun masana, da masu fafutuka don tunkarar wasu manyan ƙalubale na zamaninmu.

Taron wanda aka yi a shalkwatar Majalisar Ɗinkin Duniya dake Birnin New York na ƙasar Amurka, na da nufin ba da damar samar da hanyoyin da za a iya aiwatar da su, waɗanda ke inganta makomar duniya mai dorewa, daidaito da kuma lumana.

Ta hanyar tattara muryoyi daban-daban, taron yana haɓaka cikakkiyar magana kan sarrafa sarƙaƙiya na duniyarmu da ke kara samar da haɗin kai.

A wannan shekara, taron ya ta’allaka ne kan taken ” Samar Da Hanyoyi Daban-daban Don Samun Ingantacciyar Gobe,” tare da fitar da muhimmacin daukar matakin da ya dace don tunkarar matsalolin gaggawa da ke fuskantar bil’adama.

KU KUMA KARANTA: Isra’ila tana shirin kai farmaki a wani sansanin ‘yan gudun hijira a Gaza

Dubban ƙalubalen duniya juma damamammaki:

A sahun gaba a taron kolin shi ne nazari mai zurfi kan yanayin duniya na zamani, inda shugabanni ke fuskantar ƙalubale masu tarin yawa.

Waɗannan sun haɗa da ƙara tashe-tashen hankula na geopolitical, barazanar sauyin yanayi da ke ci gaba da tabarbarewa, da fadada rarrabuwar kawuna na tattalin arziki.
Duk da haka, a cikin waɗannan ƙalubalen akwai damar da ba a taba ganin irin ta ba don sauyi da ƙirƙira.

Tattaunawar taron ta ta’allaka ne kan muhimmancin samar da tsayayyen tsari na duniya don tunkarar waɗannan muhimman batutuwa.

Da yake jaddada mahimmancin haɗin kai akan gasa, shugabanni da mahalarta suna ba da shawara ga hanyar haɗin gwiwa don magance matsalolin da suka wuce iyaka da buƙatun mutum.

Shugabanni sun binciko yadda al’ummomi za su iya tafiya cikin sarƙaƙiya ta duniyar zamani ta hanyar salo iri-iri da suka hada da ci gaba mai ɗorewa, ci gaban fasaha, da daidaiton zamantakewa.

Tattaunawar ba wai kawai tana nufin samar da cikakken dabaru ba ne, har ma tana neman samar da haɗin kai don aiwatar da waɗannan dabarun yadda ya kamata.

KU KUMA KARANTA: Shugabannin ƙasashen ƙungiyar AES sahel za su gudanar da taron ƙoli a Yamai

Tabbatar da ci gaba mai ɗorewa da samar da kuɗi domin ci gaba:

Ɗorewar ci gaba, cibiya ce da ke da burin samar da kuɗi da zai kasance wani  muhimmin shinge ga cimma waɗannan buƙatun, tare da buƙatar sabbin hanyoyin samar da kuɗaɗe damin samun nasara.
Shugabanni suna buƙatar nuna mahimmancin haɗin gwiwar jama’a da masu zaman kansu da yuwuwar yin amfani da fasaha don buɗe sabbin albarkatu.

Ƙirƙirar tsarin ilimi da kiwon lafiya masu yawa da tsaftataccen ruwa da kula da tsafta ya fi zamuwa cikin sauƙi, kuma ana iya samunsa a yanzu fiye da lokacin da daidaiton ci gaban waɗannan tsare-tsaren ke da nufin cimma burin al’umma.

Wannan haɓakar araha na nuna haɓakar wadata da buƙatun abubuwan haɗin gwiwar saka hannun jari.

Sha’awar al’umma ta haifar da wannan ci gaba a cikin wadata da bukatun wadannan sassa na saka hannun jari ya ga ƙoƙarin haɓakawa da jawo hankalin albarkatun kudi daban-daban.

Zaman lafiya da tsaro na ƙasa da ƙasa:

Zaman lafiya da tsaro na ƙasa da ƙasa muhimmin batu ne da ya kamata a mai da hankali a kai, musamman dangane da tashe-tashen hankula da ke tasowa.

Ƙira a zauna lafiya ya kara zama wani buri na shugabanni da al’ummar duniya waɗanda ke fuskantar ƙalubalen tsaro marasa adadi da suke fuskanta a yau.

Amma duk da haka sha’awar zaman lafiya ta nuna ya fi karfin samunsa, yayin da duniya ta kasance cikin rashin tsaro kamar yadda aka saba da yake-yake, rikice-rikice na cikin gida, ta’addanci, da yaɗuwar makaman nukiliya.

KU KUMA KARANTA: Mawallafin jaridar Neptune Prime ya gina makaranta da asibiti a Yobe (Hotuna)

Wannan shi ne kawai gaskiyar da ke ci gaba da mamaye duniyarmu, kuma yana ƙara mana ƙaimi na ci gaba da gwagwarmaya don magance waɗannan barazanar tsaro da gina duniya mai zaman lafiya.

Shugabannin duniya suna ba da gudummawa sosai ga zaman lafiya da tsaro lokacin da suke jagoranci daga ciki, ba daga waje kawai ba, da kuma lokacin da suke habaka dangantaka ga mabiyansu masu kima da hadin kai.

Don inganta taron koli na makomar zaman lafiya, Cibiyar Zaman Lafiya da warware rikice-rikice (IPCR) ta shirya wani taron a ranar 3 ga watan Yuli a zauren Majalisar Ɗinkin Duniya don tattauna sabuwar Agenda don zaman lafiya, wani shiri da Sakatare-Janar na Majalisar Ɗinkin Duniya ya ƙaddamar.

 Taron na da nufin lalubo hanyoyin warware matsalolin zaman lafiya da tsaro, daidai da kudurin Majalisar Ɗinkin Duniya na samar da zaman lafiya, adalci, da daidaito a duniya.

Kimiyya, fasaha, da haɗin gwiwar dijital:

Yayin da duniya ke tasowa cikin gaggawa a cikin zamani na dijital, ana duba aikin kimiyya, fasaha, da ƙirƙira.

Taron ya kamata ya yi nufin cewa haɗin gwiwar dijital na da mahimmanci don magance matsalolin duniya kamar annoba, sauyin yanayi, da rashin daidaiton tattalin arziki.

Ya kamata shugabanni su ba da shawarar samar da daidaito wajen samun fasaha da samar da tsare-tsare masu inganta ƙirƙire-ƙirƙire tare da kare hakkin dan’adam.

KU KUMA KARANTA: Za a fuskanci yunwa mai tsanani a arewa maso gabashin Najeriya – Majalisar Dinkin Duniya

Shugabanni na buƙatar ginshikai waɗanda ke haɓaka kima yayin kiyaye haqqin ɗan adam, cikin sirri da tsaro.

 Don inganta haɗin gwiwar ƙasashen duniya don sauye-sauye na dijital da kuma daidaita yarjejeniyar don dacewa da yanayin kasa, ɗaya daga cikin sakamakon da aka ba da shawara na taron makomar gaba, Ƙungiyar Kwararrun Ƙungiyoyin Jama’a ta Najeriya, tare da Ma’aikatar Sadarwa da Tattalin Arziki na Digital, sun yi nazari kan matsayin Najeriya a karo na 3 na Global Digital Compact da aka yi wa kwaskwarima a ranar 15 ga watan Agusta a zauren Majalisar Ɗinkin Duniya da ke Abuja.

Matasa da tsarekun da za su zo nan gaba:

Karfafawa matasa da ba da fifiko ga tsararraki masu zuwa wata muhimmiyar rawa ce da matasa ke takawa wajen samar da ci gaba da samar da makoma mai ɗorewa.

 Ya kamata shugabanni su gane cewa ƙaruwar yawan matasa a duniya ba wai gaskiyar al’umma ba ce kawai. Har ma da ƙarfi na canji, mai kawo sabbin ra’ayoyi, ƙirƙira, da nuna himma a kan teburi.

Akwai buƙatar a himmatu wajen sa matasa su aiwatar da shawarwari, tun daga matakin gida zuwa na duniya, tabbatar da jin muryoyinsu da kuma daraja ra’ayoyinsu.

Wannan ya haɗa da samar wa matasa damar samun ingantaccen ilimi, horarwa da ƙwarewa, da samun damar jagoranci, ba su damar haɓaka kwarewar jagoranci da ƙwarewar da suka dace don samar da ingantaccen canji.

Ta hanyar ba da fifiko ga ƙarfafawa matasa da haɗin gwiwa tsakanin al’ummomi, ya kamata shugabanni su yi azamar samar da kyakkyawar makoma mai ma’ana, daidaito da kuma ɗorewa, inda matasa ba kawai a su shirya domin su yi jagoranci ba, har ma da samar da kayan aiki don tunkarar ƙalubalen da ke gabansu.

A halin da ake ciki, a shirye-shiryen taron koli na gaba mai zuwa, Majalisar Ɗinkin Duniya a Najeriya tare da haɗin gwiwar Ma’aikatar Raya Matasa da Haɗin Gwiwar Ƙungiyoyin Farar Hula sun shirya taron tuntubar matasa na ƙasa a watan Yuni, a zauren Majalisar Ɗinkin Duniya.

Tattaunawar ta samar da wani dandali ga matasa don shiga tattaunawa mai ma’ana, muhawara, da tattaunawa mai ma’ana, mai da hankali kan batutuwa kamar ilimi, aikin yi, kiwon lafiya, sauyin yanayi, da kuma shiga siyasa.

KU KUMA KARANTA: Turkiyya ta la’anci farfagandar Isra’ila a kafafan sada zumunta na yanar gizo, ta sha alwashin kare Gaza

 Hakkin Dan’Adam:
Dole ne shugabanni su sake jaddada aniyarsu na kiyaye ƙa’idojin kare hakkin bil’adama na ƙasa da ƙasa da aka zayyana a cikin Yarjejeniyar Hakkokin ɗan Adam ta duniya.

Dole ne su magance ci gaba da cin zarafi kamar aikin tilastawa, cin zarafi na jinsi, da kuntatawa kan ‘yancin fadar albarkacin baki, wadanda ke ci gaba da shafar al’ummomin duniya.

 Ci gaban ‘yancin ɗan’adam yana da alaƙa da wasu batutuwa masu mahimmanci na duniya kamar rage talauci, inganta sakamakon kiwon lafiya, haɓaka ilimi, da magance sauyin yanayi.

A wani ɓangare na shirye-shiryen taron koli na gaba, Majalisar Ɗinkin Duniya (UNIC) ta gudanar da tattaunawa da ƙungiyoyin kare hakkin bil’adama da masana shari’a, da masu ruwa da tsaki a fannin fasaha da kuma ‘yan jarida, dangane da “Dokar da’a ta sa kai don tabbatar da bayanan da aka bayar a baya dandali na dijital” (Takaitacciyar Siyasa ta 8) da Sakatare-Janar ya gabatar kuma an aika da martani daga wadannan tattaunawa zuwa salkwatar New York ta hanyar dandali na dijital da aka kirkira musamman don tattara bayanai daga ofisoshin sashe.

Sauyin Yanayi:
A cikin yarjejeniyar sauyin yanayi ta Birnin Paris na shekarar 2015, kasashe 193 sun ƙuduri aniyar bunƙasa tsare-tsare na yanayi na ƙasa da ke nuna “mafi girman burinsu,” da kuma sabunta wadannan tsare-tsare duk bayan shekaru biyar don cimma burinsu.

Tsarin alƙawari da bita na Paris yana buƙatar kuma waɗannan tsare-tsare na yanayin ƙasa su kasance daidai da ƙayyadaddun yanayin zafi a duniya zuwa ƙasa da 2°C da kuma yin kokarin kiyaye yanayin zafi ƙasa da 1.5° a ma’aunin salshiyos dangane da matakan masana’antu.

Cimma waɗannan buƙatun na buƙatar sauyi a duniya zuwa tattalin arzikin sifili, wani muhimmin aiki wanda ba a cika samun lokaci ba kuma har ya zuwa yanzu ba a aiwatar da shi a ma’aunin da ake bukata ba.

Sauyin yanayi yana daya daga cikin ma’anar barazanar lokacinmu kuma saurin lalata carbon yana ba da dama ga tattalin arziki, samar da ayyukan yi, kiwon lafiya da wadata, da kuma hanyar magance rashin adalci na zamantakewa da muhalli.

Yarjejeniyar Paris ta nuna wani muhimmin lokaci a cikin wannan gwagwarmayar yanayi, yayin da yake nuna hadin kai a duniya da nufin ba da shawara “don nuna goyon baya ga ƙalubalen da ke tattare da sauyin yanayi da matsalolin muhalli.”

Yunƙurin siyasa don aiwatar da ayyukan yanayi mai ban sha’awa bai taba yin girma ba. Yayin da yarjejeniyar Paris ta fara aiki a watan da ya gabata, shugabannin kasashen duniya da suka fara aiwatara da aikin sauyin yanayin sun hade wuri guda fiye da kowane lokaci.

Daidaiton Jinsi:

Duniya na fuskantar ɗaya daga cikin batutuwan da suka fi fuskantar kalubale a zamaninmu – kuma shi ne batun daidaiton jinsi. Akwai sama da mutane biliyan 6 a wannan duniyar; mata suna wakiltar kusan kashi 51% na sa.

A cikin wannan kashi 51%, biliyan 1.2 daga cikinsu suna cikin halin talauci kuma ba su iya karatu ba. Suna karbar mafi ƙarancin albashi fiye da maza kuma suna fuskatarn cutarwa na tashin hankali fiye da maza.

Ɗaya daga cikin kalubalen farko da mata ke fuskanta a duniya a yau shi ne yadda mata suka fi yawa a cikin talakawa.

Mata ba su ci moriyar irin nasarorin da ake samu a fannin ilimi da matakan samun kudin shiga ba duk da cewa su ne kashi daya na al’ummar duniya.

Ga mafi yawan mata a duniya waɗanda har yanzu suke cikin matsanancin talauci, waɗannan batutuwan da za mu lissafa sun fi damunsu: wato abinci, sutura, da matsuguni.

A yawancin sassan duniya, rayuwar ‘ya’ya mata ta kasance gajeriya kuma mai tsanani; ana ciyar da su ba ta hanyar da ta dace ba, kuma ana nuna musu wariya ta fuskar zamantakewa da doka.

Lokacin da albarkatu suka yi ƙaranci, maza na iya samun fiye da kaso ɗaya na abinci, wanda ke haifar da tamowa ga ‘yan mata.

KU KUMA KARANTA: Majalisar Dattawan Amurka ta ba da tallafin dala biliyan 26.6 ga Isra’ila

Lokacin da dukiyar iyali ta kasance karkashin haraji, sau da yawa ana ci gaba da habakawa ga mata da ‘yan mata da ke kan hanya.

Yanayin tattalin arziki ya kan tilasta wa mata yin aiki a kananan ayyuka, ayyuka na karshe waɗanda galibi ke sanya su cikin hatsari ga cin zarafi.

Don inganta daidaiton jinsi, Majalisar Ɗinkin Duniya (UN Women, UNIC, UNFPA, da UNIDO) a Najeriya sun shirya taron farko na duniya “Mu Mata: Tattaunawar Tsare-Tsare” da nufin ba da fifiko da bukatu da buri na yanzu da na gaba. Wannan yunkuri ya karfafawa mata da ‘yan mata, ya kara fadakar da muryoyinsu wajen tsara kyakkyawar makoma mai daidaito da dorewa.

Jerin tattaunawar ya tattaro mata daga sassa daban-daban da ƙungiyoyi shekaru don samar da canji mai kyau ta hanyar wargaza shinge da gina gadoji.
Mataimakin Sakatare-Janar na Majalisar Ɗinkin Duniya (DSG) da ministar harkokin waje da hadin gwiwar Jamus, Svenja Schulze, ne suka kaddamar da jerin sabbin hanyoyin tattaunawa a cikin watan Satumba na 2023, a gefen taron koli na ci gaba mai dorewa (SDG).

Yayin da ake shirin fara taron koli na gaba na Majalisar Ɗinkin Duniya, ya kamata tattaunawa da alkawuran su kasance da kyakkyawan fata na hadin gwiwar ƙasa da ƙasa a shekaru masu zuwa.

Ci gaba, nauyi ne na shugabannin duniya, ‘yan kasa, da kuma al’ummomi masu zuwa su rungumi ruhin haɗin gwiwa da ƙirƙira don neman ci gaba mai ɗorewa ga kowa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here