Connect with us

Labarai

Za a samu ambaliyar ruwa a jihar Kwara – NEMA

Published

on

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta ƙasa, (NEMA), ta sanar da mazauna jihar Kwara kan wata ambaliyar ruwa da ke tafe a bana 2023.

Hukumar ta shawarci hakiman ƙauye da gundumomi da kuma malaman addini musamman na al’umma da su fara shirye-shirye domin daƙile illolin da ambaliyar ruwan za ta haifar.

Hakan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da shugabar hukumar ta NEMA a Minna, Zainab Suleiman-Sa’idu ta fitar, wacce ta bayyanawa kamfanin dillancin labarai na Najeriya a Ilorin ranar Litinin.

KU KUMA KARANTA: Wasu jihohi a arewacin Najeriya za su fuskaci ƙarancin ruwan sama – NEMA

Ta ce sanarwar ta zama dole ne biyo bayan rahoton ambaliyar ruwa na shekara-shekara, AFO, wanda Hukumar Kula da Ruwa ta Najeriya, NIHSA ta fitar da hasashen yanayi na 2023 da Hukumar Kula da Yanayi ta Najeriya, NiMET ta yi.

Ta ƙara da cewa, rahotannin biyu sun samo asali ne daga binciken kimiyya da suka nuna cewa ƙasar za ta fuskanci yiyuwar ambaliya ta ɓangarori uku, da suka haɗa da hadari mai yawa, matsakaici da kuma ƙarancin hadari.

Ta ci gaba da cewa, rahoton ya kuma bayyana jihar Kwara na cikin jihohin da ke fama da matsalar ambaliya.

Don haka ta shawarci shugabannin al’umma da su gaggauta jagorantar al’ummar da al’ummominsu daban-daban wajen gano magudanan ruwa da aka toshe don sharewa da kwashewa.

Hukumar ta kuma buƙaci shugabannin al’umma da su wayar da kan mutanen da suka gina kan filayen ambaliyar ruwa da kuma waɗanda ke zaune a bakin kogi domin su koma wurare masu tsaro da kuma tudu.

Bisa ga 2023 AFO, ana sa ran za a yi ambaliyar ruwa a jihar daga watannin Agusta, Satumba da Oktoba. “A bayyane yake cewa ambaliyan ruwa na 2023 ba wai kawai mazauna karkara da ke zaune a bakin kogi ke barazana ba, saboda ana sa ran ambaliyar ruwa a biranen jihar Kwara sosai.

“Rigakafin ba kawai ya fi kyau ba har ma yana da arha, hukumar ta yi imanin cewa idan aka yi biyayya da waɗannan gargaɗin, za a ceci rayuka da dukiyoyin mutane,” in ji ta.

2 Comments

2 Comments

  1. Pingback: Bana za a samu ambaliyar ruwa a jihar Ekiti – NEMA | Neptune Prime Hausa

  2. Pingback: NiMet ta yi hasashen za a yi kwanaki uku ana ƙwalla rana da gajimare | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like