Connect with us

Laifi

’Yan sanda sun kama wani matashi kan zargin satar kuɗi ta na’urar ATM

Published

on

’Yan sanda sun kama wani matashi kan zargin satar kuɗi ta na’urar ATM

’Yan sanda sun kama wani matashi kan zargin satar kuɗi ta na’urar ATM

Daga Muhammad Kukuri

Rundunar ’yan sandan jihar Gombe ta kama matashin, wanda ake wa inkiya da Mai Shanawa ne kan zargin aikata yaudara da satar kuɗi da katin ATM ta na’urar PoS.

Matashin ya faɗa komar ’yan sanda ne bayan wani mazaunin garin Abuja Bula, da ke Karamar Hukumar Kwami ya kai rahoto ofishin ’yan sanda na Dukku a ranar 22 ga Watan Mayu 2024.

Muhammad yana zargin matsahin da yaudarar sa da kuma satar kudi a asusun bankinsa a banki a lokacin da yaje cire kuɗi da katinsa na ATM.

Ya ce bayan ya saka katinsa  na’urar ATM ba ta ba shi kudin ba, ashe matashin yana biye da shi a baya, sai ya yaudare shi cewa ya shiga cikin banki ya yi musu bayani.

KU KUMA KARANTA: Ƴan sandan Najeriya sun kama waɗanda ake zargi da satar mutane a titin Abuja-Kaduna

Bai ankara ba, ashe a lokacin matashin ya zare masa katin ya bar shi a wajen.

Mutumin ya ci gaba da cewa, yana tsaye yana jira can sai yaga sako an cire Naira dubu ɗari uku daga asusunsa ta wani POS da ke kusa da bankin a garin na Dukku.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ’yan sandan jihar, ASP Buhari Abdullahi, ya ce bayan  samun rahoton ƙorafin suka shiga bincike suka yi sa’ar kama wanda ake zargin.

ASP Buhari Abdullahi ya ce a yayin binciken sun samu katunan cire kuɗi na ATM daban-daban har guda 21, ciki harda na wanda ya kai ƙorafin, a hannun matashin.

Sannan ya ce suna kan ci gaba da bincike, da zarar sun kammala za su tura wanda ake zargin zuwa kotu.

Laifi

Wani uba ya yi wa ’yarsa mai shekara 8 fyaɗe

Published

on

Wani uba ya yi wa ’yarsa mai shekara 8 fyaɗe

Wani uba ya yi wa ’yarsa mai shekara 8 fyaɗe

Wani mai sayar da maganin gargajiya ya gurfana a gaban kotu bisa zarginsa da yi wa ɗiyarsa mai shekaru takwas fyaɗe.

An gurfanar da magidancin mai shekaru 35 a kan tuhume-tuhume guda na fyaɗe, wanda rundunar ‘yan sandan ta ce ya saba wa sashe na 25 (a) na dokar cin zarafin jama’a ta jihar Ondo ta shekarar 2021.

Dan sanda mai shigar da ƙara, Sufeto Martins Olowofeso, ya shaida wa kotun cewa an kama wanda ake ƙara ne a ranar 18 ga watan Yuni, 2024 bayan rahoton da aka kai ga sashin yaki da garkuwa da mutane na ’yan sanda a Alagbaka, cewa ya yi wa ’yarsa fyaɗe.

Daga bisani an tsare wanda ake tuhuma don ci gaba da bincike.

A cewar Mista Olowofeso, wanda ake zargin tare da matarsa ​​sun gudu daga gidansu bayan aikata laifin inda suka je Jihar Osun suka samo rahoton likita na ƙarya, da ke nuna babu wani abu da ya samu yarinyar.

Ya kuma shaida wa kotun cewa jami’in bincike na ’yan sanda ya sake yin wani gwaji a Akure, wanda ya nuna cewa an zakke wa yarinyar, kuma ta kwashe kwanaki uku tana zubar da jini.

A cewar Olowofeso, wanda ake tuhumar ya amsa laifin da ake zargin sa da shi a lokacin da jami’in da ke binciken ya yi amsa tambayoyi.

KU KUMA KARANTA: An ɗaure ɗan shekara 17 shekaru 14 a kurkuku saboda fyaɗe

Olowofeso ya buƙaci kotun da ta ci gaba da tsare wanda ake ƙara a gidan gyaran hali na Olokuta har zuwa lokacin da za ta samu da shawara daga sashen shigar da kara na gwamnati (DPP).

Lauyan wanda ake ƙara, G.O Omoedu, ya shaida wa kotun cewa an kai wa wanda yake karewa sammaci ƙurarren lokaci kuma zai buƙaci lokaci domin ya mayar da martani kan batun shari’a.

Ya buƙaci kotun da ta dage ci gaba da shari’ar don ba shi damar amsa buƙatar ci gaba da sauraren ƙarar.

Majistare B.A. Alipohul ya bayar da umarnin a ci gaba da tsare wanda ake ƙara a hannun ’yan sanda sannan ya dage shari’ar zuwa ranar 4 ga watan Yulin 2024.

Continue Reading

Laifi

’Yan bindiga sun sace Hakimi da manoma 2 a Kaduna

Published

on

’Yan bindiga sun sace Hakimi da manoma 2 a Kaduna

’Yan bindiga sun sace Hakimi da manoma 2 a Kaduna

’Yan bindiga sun yi garkuwa da Hakimin Tunburku, Malam Ashiru Sherehu da ke Ƙaramar Hukumar Giwa a Jihar Kaduna.

Rahotanni sun bayyana cewar, maharan sun yi awon gaba da Sherehu a kan hanyarsa ta dawowa daga gona a ranar Asabar.

’Yan bindiga sun addabi yankin da ke gundumar Fatika a ‘yan kwanakin nan da hare-hare.

A cewar wani mazaunin yankin, Ahmadu, manoma ba sa iya zuwa gonakinsu da ke da nisan kilomita kaɗan daga garin saboda tsoron kada a kashe su ko kuma a sace su.

Wani basaraken gargajiya a yankin kuma Sarkin Fadan Galadimawa, Husseini Umar, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce an yi garkuwa da hakimin ƙauyen da misalin ƙarfe 5 na yammacin ranar Asabar.

KU KUMA KARANTA: Ƴan bindiga sun yi garkuwa da ɗalibai da dama a jihar Delta

“Yana dawowa daga gonarsa da ke Tunburku sai ‘yan bindigar suka tare shi suka tafi da shi. Har yanzu ba mu ji daga gare su ba; kuma ba su tuntuɓe mu ba,” in ji shi.

A cewar Hussaini, an kuma sace wasu manoma biyu a yankin Sabon Layi da ke gundumar Kidandan a lokacin da suke aiki a gonakinsu a ranar Lahadi da rana.

Ya bayyana cewar mutanen ƙauyen da lamarin ya faru a gabansu sun kasa yin komai saboda ’yan bindigar na ɗauke da makamai.

Umar, ya koka kan yadda ’yan bindiga ke yi wa manoma ɗauki ɗai-ɗai a yankin.

Amma, ya yaba da ƙoƙarin sojojin da aka tura yankin, sai dai ya roƙi gwamnati da ta aike da ƙarin jami’an tsaro masu yawa saboda yadda rashin tsaro ke ƙara ta’azzara a yankin.

Rundunar ’yan sandan Jihar Kaduna ba ta ce komai kan faruwar lamarin ba.

Jin ta bakin kakakin rundunar, ASP Mansir Hassan, ya ci tura domin ba ya amsa ƙiran waya.

Continue Reading

Labarai

Harin ƙunar baƙin wake ya kashe mutane 6 a Borno – ‘Yansanda

Published

on

Harin ƙunar baƙin wake ya kashe mutane 6 a Borno – ‘Yansanda

Harin ƙunar baƙin wake ya kashe mutane 6 a Borno – ‘Yansanda

Daga Ibraheem El-Tafseer

Aƙalla mutane shida ne suka mutu inda wasu 15 suka jikkata a wani harin ƙunar baƙin wake da aka kai a garin Gwoza na jihar Borno.

Wani abin takaici ya faru ne a lokacin da ‘yar ƙunar baƙin wake ta tayar da bam a garin Gwoza, ranar Asabar.

Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya, (NAN), ya ruwaito cewa an kai harin ne a wani wurin shaƙatawa na motoci da ake ƙira Marrarraban Gwoza.

Kwamishinan ‘yansandan jihar Borno Yusuf Lawal ya tabbatar da faruwar harin yana mai cewa wata ‘yar ƙunar baƙin wake ce ta kai harin.

Lawal ya ce jami’in ‘yansandan shiyyar Gwoza ne ya sanar da shi cewa aƙalla mutane shida ne suka mutu inda aka kwashe wasu 15 zuwa asibiti.

Wani ganau mai suna Buba, ya shaida wa NAN cewa ‘yar ƙunar baƙin waken ta nufi tsakiyar wani bikin aure ne, inda ta tayar da bam ɗin a nan.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan sanda sun kama mutum 2 da ake zargin sace mahaifiyar Rarara

Buba ya ce harin ya rusa farin ciki da murnar wannan rana ta musamman, inda ya bar iyalai da ‘yan uwa cikin makoki.

Wani wanda ya shaida lamarin, Muhammed Kasim, ya ce harin ya faru ne da misalin ƙarfe 1:30 na rana.

“Mun ji ƙarar fashewar abubuwa, tare da ƙura, sai muka ga gawarwaki a ƙasa.”

Ya ce an kwashe da dama daga cikin waɗanda lamarin ya rutsa da su zuwa asibiti yayin da aka tura jami’an tsaro domin dawo da zaman lafiya a yankin. (NAN).

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like