‘Yan sanda sun kama mutane biyu da laifin daɓa wa matashi wuƙa, ya mutu har lahira

Rundunar ‘yan sandan jihar Legas ta kama wasu mutane biyu da ake zargi da daɓa wa wani yaro ɗan shekara 13 wuƙa ya mutu har Lahira a kan mallakar silifas ɗin roba.

Kakakin rundunar ‘yan sandan, SP Benjamin Hundeyin, ya tabbatar wa Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya batun.

Hundeyin ya ce lamarin ya faru ne a ranar Lahadi da misalin ƙarfe 6:00 na yamma, a Iganmu, ƙarƙashin gadar.

Ya ce rundunar ‘yan sanda ta Ijora Badia ta samu labarin ne daga bakin wani jama’a da abin ya shafa cewa wasu matasa na haɗa kansu domin tayar da zaune tsaye a yankin Iganmu.

Kakakin ya ce rikicin ya samo asali ne sakamakon zargin kashe wani yaro ɗan shekara 13 mai suna Ekene.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan sanda sun kama wata mata da ta yanka ‘yar aikinta da wuƙa a Legas

Hundeyin ya ce, nan take tawagar ‘yan sintiri suka je wurin da lamarin ya faru inda suka tarar da wanda abin ya shafa a cikin jininsa.

“Bayanan da aka samu a wurin sun nuna cewa an yi zargin wasu maza biyu ne suka caka masa wuƙa a kan wata ƙaramar matsala da ta shafi mallakar takalmin silipas na roba.

“An kuma tattaro cewa waɗanda ake zargin sun tsere daga wurin bayan sun aikata laifin.

An bi wasu sahihan hanyoyi wanda ta kai ga kama su, su biyun Ahmed mai shekaru 28 da Umaru Abubakar mai shekaru 18.

“An duba wanda abin ya shafa, yayin da aka ga wani rami mai zurfi da ake zargin ya samu rauni ne daga wuƙa a gefen dama na ƙirjinsa.

Nan take aka garzaya da shi babban asibitin Ajeromi domin samun kulawar gaggawa.

“Duk da haka, ya mutu yayin da yake karɓar magani. An kai gawarwaki zuwa babban asibitin Yaba domin adanawa tare da tantance gawar,” inji shi.

Wanda ya yi hoton ya ce an ɗauki hoton inda lamarin ya faru, yayin da aka kai waɗanda ake zargin zuwa tashar domin yi musu tambayoyi, inda suka amsa laifin da suka aikata.

Hundeyin ya ce mahaifiyar marigayiyar, Chizoba Agu na layin dogo, Ijora Badia, ta zo asibiti inda ta bayyana marigayin a matsayin ɗanta.

Ya ce za a miƙa waɗanda ake zargin zuwa sashin binciken manyan laifuka na jihar Panti domin gudanar da bincike mai zurfi.


Comments

2 responses to “‘Yan sanda sun kama mutane biyu da laifin daɓa wa matashi wuƙa, ya mutu har lahira”

  1. […] KU KUMA KARANTA: ‘Yan sanda sun kama mutane biyu da laifin daɓa wa matashi wuƙa, ya mutu har lahira […]

  2. […] KU KUMA KARANTA: ‘Yan sanda sun kama mutane biyu da laifin daɓa wa matashi wuƙa, ya mutu har lahira […]

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *