Connect with us

'Yansanda

Yadda tsohon Kwamishina ya kashe abokinsa kan ‘Yarsa da yake nema

Published

on

Ana zargin Basarake kana tsohon kwamishinan yaɗa labarai na Bauchi Mohammed Galadima Damina da kisan abokinsa, kana maƙwabcinsa mai suna Adamu Babanta, wanda yake zargin tsohon Kwamishinan da yunƙurin yin lalata da ‘yarsa.

Lamarin ya faru ne a unguwar Yelwan Lebra, da ke wajen birnin Bauchi da yammacin Lahadi, 30 ga Oktoba, 2022.

Rahotanni sun nuna cewa Marigayin , mai shekaru 68, wanda tsohon ma’aikacin gwamnatine ya kama amininsa tare da ‘yarsa a yammacin ranar Lahadi, yana ƙoƙarin yaudararta domin yayi lalata da ita, lamarin da ya ɓata masa rai ya kuma yi yunƙurin ɗaukar mataki amma abokin nasa ya buge shi da mota, lamarin da yayi ajalinsa.

Kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito, tsohon Kwamishinan ya taɓa riƙe muƙamin kwamishinan yada labarai da kuma Kwamishinan ayyuka na musamman a lokacin mulkin tsohon gwamna Isa Yuguda a karo na biyu. Kana yana riƙe da sarautar gargajiya ta Galadiman Dass a masarautar Dass ta jihar Bauchi.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan sanda sun shawo kan matasan da suka fito zanga-zanga bayan kashe wani mai shekara 67

Mazauna yankin sun shaida cewa wanda ake zargin ya kira ‘yar abokinsa ta waya domin tazo su haɗu da shi a wani gidan mai.

A cewar wani ɗan uwan mamacin da bai so a bayyana sunansa ba, Galadiman na Dass da marigayin abokai ne kuma makwabta ne.

“Ana zargin cewa Galadima ya yi yunƙurin yin lalata da ‘yar amininsa mai shekaru 18, mai suna Khadija, bayan yayi ta bibiyarta da ta zo su haɗu, inda yayi ta tura mata katin waya.

“Hakan ne ya sanya Khadija ta shaida wa mahaifiyarta, wacce ta shaida wa mahaifin yarinyar cewa abokinsa na neman ‘yarsa da lalata, amma yaƙi yarda da maganar sai a ranar Lahadin da tsohon Kwamishinan ya kira Khadija ya kuma nemi ta same shi a Unguwar Yelwan Lebura, sai mahaifin nata ya nemi ta fita zai biyo bayanta ya tabbatar.

Ko da ta tafi ta tarar da tsohon Kwamishinan, inda ya buɗe mata mota ta shiga, hakan ne yasa Marigayin ya doshi motar abokinsa a fusace ko da tsohon Kwamishinan ya gan shi sai yayi yunqurin barin wajen da motar, yayin da Marigayin ya cusa hannunsa cikin motar yana ƙoƙarin kashe injin motar, nan take tsohon Kwamishinan ya buge kan abokinsa a jikin garun da ke gefe, ya kuma take kafafunsa da motar lamarin da yayi sanadiyar mutuwarsa bayan an yi ƙoƙarin ceton rayuwarsa a asibitin koyarwa na jami’ar Abubakar Tafawa Ɓalewa” inji shi.

Al’ummar ‘yankin sun gudanar da zanga zanga a ranar Litinin inda suka tushe hanyoyi suka hana zirga zigar ababan hawa har sai da jami’an tsaron da suka haɗarda soji da ‘yan sanda suka kwantar da tarzomar da ta biyo bayan zanga zangar.

Hukumar ‘yan sanda a jihar ta Bauchi ta tabbatar da faruwar lamarin, a cewar mai magana da yawun rundunar ‘yan sanda a jihar Bauchi Ahmed Wakili, rundunar ‘yan sandan na bincike game da lamarin.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

'Yansanda

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

Published

on

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

Rundunar ’yan sandan Najeriya ta tube wa wasu jami’an ta biyar kaki sakamakon zargin su da karɓar cin hancin kuɗi kimanin Naira miliyan uku.

Mataimakin Shugaban ’yan Sanda mai kula da Shiyya ta shida ta da ke Jihar Kuros Riba, Jonathan Towuru, ya sanar a Kalaba cewa ’yan sandan sun kwace kuɗin ne da bakin bindiga a hannun wani mai abin hawa.

A makon jiya ne aka zargi jami’an da ƙwayar kuɗin da bakin bindiga a hannun wani mutum da rundunar ta sakaya sunansa.

Yanzu haka waɗanda ake zargin an tuɓe masu kaki amma ana tsare da su ana bincike, da zarar an same su da laifi kotu za a turasu ta yanke masu hukuncin da ya dace.

KU KUMA KARANTA: ’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe

Mataimakin shugaban ’yan sandan ya ce waɗanda ake zargin su da karɓar cin hancin kuɗi Naira milyan uku daga wannun wani.

Ko a kwanan baya irin haka ta taba faruwa a kan babbar hanyar Kalaba zuwa Ikom inda aka kama wasu ’yan sanda kan karbar na goro.

Tafiya a kan hanyar na yawan zargin ’yan sanda da kula da shingen bincike a kan hanyar da yawan tatsar su kuɗi.

Continue Reading

'Yansanda

‘Yan sanda sun kama mutum 2 da ake zargin sace mahaifiyar Rarara

Published

on

Yan sanda sun kama mutum 2 da ake zargin sace mahaifiyar Rarara

‘Yan sanda sun kama mutum 2 da ake zargin sace mahaifiyar Rarara

Rundunar ’yan sandan Jihar Katsina ta sanar da cafke wasu mutum biyu bisa zargin hannu a garkuwa da mahaifiyar fitaccen mawaƙin siyasar nan, Dauda Kahutu Rarara.

Mai magana da yawun rundunar a Katsina, ASP Abubakar Sadiq Aliyu ya ce “muna tsare da mutum biyu kan lamarin, muna ci gaba da bincike.”

Tun farko, Kwamishinan tsaro na Jihar Katsina, Nasiru Mu’azu ya ce an sace dattijuwar ce a daren Juma’a a ƙauyen Kahutu da ke Karamar Hukumar Ɗanja.

Mu’azu ya ce waɗanda suka sace matar sun yi hakan ta hanyar bi ta bayan gida, inda suka sace ta ba tare da jami’an da ke tsaron gidan sun sani ba.

Ya kuma bayyana cewa tuni aka tura jami’an tsaro waɗanda suka bazama cikin dazuka domin bin sawun ’yan bindigar.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan bindiga sun yi garkuwa da mahaifiyar mawaƙi Rarara

Neptune Prime Hausa ta ruwaito shaidu a kauyen sun ce da misalin karfe daya na dare ne dandazon ’yan bindiga suka kutsa gidan dattijuwar suka yi awon gaba da ita.

“A kafa suka zo, ba su yi harbi ba a lokacin da suka ka yi awon gaba da ita cikin ’yan mintoci.

“Dattijuwar ba ta bijire musu ba a lokacin da suka memi ta biyo su.

“Duk da cewa ’yan bindigar sun samu wasu mutane a gidan, amma mahaifiyar Rarara kaɗai suka ɗauka.

“Babu wani yunƙuri da aka yi na tunkarar ’yan bindigar a lokacin da suke tafiya da ita saboda bindigogin da suke ɗauke da su,” in ji wani mazaunin ƙauyen na Kahutu.
Ya ce, “Watakila maharan sun bar baburansu ne daga nesa suka tako zuwa cikin ƙauyen a kafa.

“Muna rokon Allah Ya kuɓutar da ita cikin koshin lafiya domin tana taimaka mana sosai a wannan ƙauyen.

“Danta Rarara mai yawan taimakon al’umma ne, kuma ya kawo mana abubuwan ci gaba sosai a garinmu,” in ji shi.

Continue Reading

'Yansanda

‘Yan sanda sun kama kawali na ’yan bindiga

Published

on

'Yan sanda sun kama kawali na ’yan bindiga

‘Yan sanda sun kama kawali na ’yan bindiga

Daga Muhammad Kukuri 

Wani wanda yake kai wa ’yan bindiga karuwai domin yin lalata da su ya shiga hannun jami’an tsaro.

’Yan sanda sun bayyana cewa kawalin ya kuma ƙware wajen yin safarar makamai ga ƙungiyar jagoran ’yan bindiga mai suna Arɗo, wanda ake nema ruwa a jallo a yankin Kagarko da ke Jihar Kaduna.

An kuma gano cewa mutumin wanda yake harkar hada-hadar tura kuɗi ta PoS, shi ke kai wa iyalan ’yan bindiga kuɗaɗe a yankin na Kagarko.

Dubun kawalin ta cika ne a yayin wani samamen haɗin gwiwa da ’yan sanda suka gudanar a yankin.

Kwamishinan ’Yan Sandan Birnin Tarayya, ya sanar ranar Talata cewa wanda ake zargin ya shaida musu cewa shi ke tsara yadda ake kai wa ’yan bindiga karuwai da miyagun ƙwayoyi da ma’aikatan lafiya a duk lokacin da suke buƙata.

KU KUMA KARANTA: Ƴan sanda a Kano sun kai mutanen da ake zargi da sayar da dala ba bisa ƙa’ida ba kotu

“Ya kuma amsa cewa yana yin dakon kuɗi tare da rabawa ga iyalan ’yan bindiga.

“A cewarsa, kuɗaɗen da ya raba wa iyalan ’yan bindiga sun haura Naira miliyan ashirin,” in ji kwamishinan ’yan sandan.

Igwe ya ce wanda ake zargin ya tabbatar musu cewa ’yan bindigar da ke ƙarƙashin Ardo sun kai 15 kowannensu da bindiga ƙirar AK-47.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like