Connect with us

Ƙasashen Waje

Sojoji sun roƙi kotun ECOWAS ta tilasta wa makwabtan Nijar ɗage takunkumai

Published

on

Gwamnatin mulkin sojin Nijar ta buƙaci Kotun Afirka ta Yamma ta ECOWAS da ta ba da umarnin ɗage takunkuman da maƙwabtanta suka ƙaƙaba wa ƙasar sakamakon juyin mulkin da aka yi a watan Yuli, inda aka hamɓarar da zaɓaɓɓen shugaban ƙasar.

“Babu wani ɓangare na al’ummar Nijar da waɗannan takunkuman ba su shafa ba” waɗanda suka janyo wahalhalu na tattalin arziki a daya daga cikin ƙasashen mafi talauci a duniya, a cewar Youkaila Yaye, ɗaya daga cikin lauyoyin gwamnatin mulkin sojan, yayin da yake yi wa kotun jawabi a zaman da aka yi a ranar Talata a Abuja, babban birnin Najeriya.

Bayan da manyan sojoji suka hamɓarar da shugaban ƙasar Nijar Mohamed Bazoum, ƙasar ta fuskanci takunkuman tattalin arziki daga ƙungiyar ECOWAS da kuma wasu ƙasashen da suka haɗa da Amurka da suke bayar da agajin kiwon lafiya da tsaro da kayayyakin more rayuwa.

KU KUMA KARANTA: An rantsar da mambobin hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa a Nijar

Makwabtan kasashe sun rufe iyakokinsu da Nijar kuma an katse sama da kashi 70 na wutar lantarkinta, wacce Najeriya ke bayarwa, bayan dakatar da hada-hadar kuɗaɗe da ƙasashen Yammacin Afirka.

An rufe ƙadarorin Nijar a bankunan ƙasashen waje tare da hana ɗaruruwan miliyoyin daloli na agaji.

Takunkuman su ne mafi tsauri da ƙungiyar ƙasashen yankin ta ƙaƙaba wa ƙasar, a yunƙurin da take yi na daƙile juyin mulki a yankin Sahel na Afirka mai fama da rikici.

Sai dai ba su yi wani tasiri ko kaɗan ba wajen rage burin gwamnatin mulkin sojan, wadda ta ci gaba da nuna ƙarfin ikonta yayin da miliyoyin mutane a Nijar ke fuskantar ƙunci.

A yayin zaman kotun, lauyoyin gwamnatin sun bayyana yadda takunkuman ke cutar da Nijar: Yara ba sa iya komawa makaranta saboda ƙarancin kayayyaki. Kayayyaki na ƙarewa a shagunan sayar da magunguna. Harkokin kasuwancin sun tsaya cak saboda tsadar kayayyaki.

Yaye ya zargi ECOWAS da ladabtar da ‘yan Nijar kan juyin mulkin ta hanya mai tsauri fiye da yadda ta yi ga wasu ƙasashen da aka yi juyin mulki, “musamman dangane da hada-hadar kuɗi.

Gwamnatin mulkin sojin ta buƙaci kotun da ta sassauta takunkuman har sai an yanke hukunci. Sai dai ECOWAS ta nuna rashin amincewa da buƙatar tasu.

Lauyan ECOWAS, Francois Kanga-Penond, ya ce ba a amince da gwamnatin mulkin soja a ƙarƙashin tsarin ƙungiyar ba kuma ba ta da ikon shigar da irin wannan ƙara a kotu.

Kotun ta ɗage zaman har zuwa ranar 7 ga watan Disamba.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Ƙasashen Waje

Mutumin da ya fi kowa tsallake haɗari a duniya ya mutu

Published

on

Mutumin da ya fi kowa tsallake haɗari a duniya ya mutu

Mutumin da ya fi kowa tsallake haɗari a duniya ya mutu

Daga Ibraheem El-Tafseer

Frane Selak ya kasance wanda ya fi kowa tsallake rijiya da baya a duniya.

A shekarar 1962 ya tsallake haɗarin jirgin ƙasa wanda mutane 17 suka mutu, a 1963 jirgi ya faɗi da shi kowa ya mutu sai shi kaɗai ko ƙwarzane bai yi ba.

A shekarar 1966 motar safa ta lume da su a rafi mutum huɗu sun mutu amma Frane bai samu ko ƙwarzane ba a yayin da a shekarar 1973 motarsa ta kama da wuta ya tsallake rijiya da baya, ya kuma tsallake haɗarin taho mu gama da mota ta yi da shi ya tsira ya kuma lashe yuro dubu ɗari takwas a Caca a shekarar 2003.

KU KUMA KARANTA: Labarin zuwa Hajji mai ban mamaki

Continue Reading

Ƙasashen Waje

Isra’ila ta ƙaddamar da sabbin hare-hare a kudancin Gaza

Published

on

Isra'ila ta ƙaddamar da sabbin hare-hare a kudancin Gaza

Isra’ila ta ƙaddamar da sabbin hare-hare a kudancin Gaza

Isra’ila ta ƙaddamar da sabbin hare-hare a kudancin Gaza, inda ta tilasta wa ɗaruruwan Falasɗinawa tserewa bayan da soji suka kuma ba da umarnin ƙaurace wasu yankuna masu yawan jama’a.

KU KUMA KARANTA: Sojojin Isra’ila sun ce an yi musayar wuta da dakarun Masar

Waɗanda suka shaida lamarin sun ce an kai hari da dama a ciki da wajen birnin Khan Younis, inda aka hallaka mutane takwas kuma mutane sama da 30 suka samu raunuka, cewar wata majiyar lafiya da kuma ƙungiyar Red Crescent ta Falasɗinawa.

Continue Reading

Ƙasashen Waje

Farashin man fetur zai ƙaru a watan Yuli a Ghana – COPEC

Published

on

Farashin man fetur zai ƙaru a watan Yuli a Ghana - COPEC

Farashin man fetur zai ƙaru a watan Yuli a Ghana – COPEC

Ƙungiyar Kare Haƙƙin Masu Amfani da Man Fetur a Ghana ta yi hasashen cewa akwai yiwuwar a samun ƙarin farashin man fetur a ƙasar a farkon watan Yulin 2024.

Ƙungiyar ta Chamber for Petroleum Consumers (COPEC) ta ce akwai alamu masu ƙarfi da ke nuna cewa farashin fetur da man dizel da gas zai ƙaru baki ɗaya a gidajen man da ke faɗin ƙasar, kamar yadda kamfanin watsa labarai na ƙasar Ghana ya ruwaito.

COPEC ɗin ta ce za a samu ƙarin farashin ne sakamakon yadda farashin Cedi ɗin a ƙasar ke ƙara karewa idan aka kwatanta da dalar Amurka.

COPEC ɗin ta yi hasashen cewa farashin man fetur ɗin wanda za a rinƙa sayarwa a gidan mai zai ƙaru da kashi 2.17 cikin 100, wanda hakan ke nufin zai ƙaru daga Cedi 14.17 zuwa Cedi 15.20 a duk lita.

Sai kuma farashin dizel ana sa ran ya ƙaru zuwa 15.21 a kowace lita ɗaya, sai kuma na gas ya koma tsakanin Cedi 13.24 zuwa Cedi 14.64 a duk kilo ɗaya.

KU KUMA KARANTA: Ɗan Ghana ya kafa tarihi na rungumar bishiyoyi a duniya

Ƙungiyar ta COPEC ta bayar da shawara ga gwamnatin Ghana da ta yi duk mai yiwuwa domin rage harajin da yake a kan gas ko kuma yin tallafi a farashinsa domin bayar da dama ga ‘yan ƙasar su same shi a farashi mai rahusa.

Ta kuma yi ƙira ga gwamnati da kada ta yi ƙasa a gwiwa wajen dawo da matatar mai ta Tema a kan aiki (TOR) don kaucewa ko kuma rage shigo tattacen man fetur wanda a wani lokacin ake samun gurɓatacce.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like