Connect with us

Labarai

Sojoji sun damƙe waɗanda ke kai wa Bello Turji makamamai a Zamfara

Published

on

Rundunar soji ta sanar da cewa, a wani samame daban-daban da dakarunta suka gudanar sun kama wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne da ke kai wa wani ɗan bindigan nan mai suna Bello Turji makamai.

Da yake jawabi ga manema labarai a Abuja a ranar Alhamis, 23 ga watan Nuwamba, 2023, Daraktan ayyukan yada labarai na tsaro, Manjo Janar Edward Buba, ya ce wadanda ake zargin suna kan hanyarsu ta kai wa shugaban ‘yan bindigar Zamfara makamai da alburusai ne a lokacin da sojoji suka kama su.  .

Mutanen uku da sojoji ba su bayyana sunayensu ba, an kama su ne a Kaduna a wani samame da aka gudanar tsakanin ranakun 14 zuwa 17 ga watan Nuwamba, 2023.

Hedikwatar tsaro ta bayyana a ranar 14 ga Nuwamba, 2022, ta bayyana Turji da wasu 18 da ake nema ruwa a jallo tare da ba su kyautar N95m ga wanda ya bada labarin inda za a kama su.

KU KUMA KARANTA: Gwamnatin Zamfara ta ba da umarnin rufe kasuwar Maru, bayan harin ‘yan bindiga a garin

An yi la’akari da shi a matsayin ɗaya daga cikin manyan ‘yan bindiga, Turji na da hannu a zargin kisan mutane kusan 200 da suka haɗa da mata da yara a watan Janairun 2022.

An kuma ce shi ne ya kai harin a ƙauyen Garki da ke Sokoto, inda aka kashe sama da mutane 80 a cikin dare a shekarar 2021.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

An kama ɓarayin da ke haurawa gidajen mutane suna sata a Yobe

Published

on

An kama ɓarayin da ke haurawa gidajen mutane suna sata a Yobe

An kama ɓarayin da ke haurawa gidajen mutane suna sata a Yobe

Daga Ibraheem El-Tafseer

Da safiyar ranar Litinin ne, ana tsaka da ruwan sama, aka kama wasu ɓarayi guda uku, waɗanda suka ƙware wajen haurawa gidajen mutane suna sace musu kayayyaki.

An kama su ne a unguwar Jaji da ke garin Potiskum jihar Yobe, a cikin wani sabon asibiti da ake ginawa, wanda ba a kammala ba.

An same su sun cire dukkan kan famfunan asibitin. Suna tsaka da cire-ciren, dubunsu ta cika aka kama su. Mutanen unguwar ne suka kama su, sannan suka miƙa su ga jami’an tsaron NSCDC da ke Potiskum.

Neptune Prime Hausa ta ziyarci ofishin NSCDC ɗin da ke gundumar Jigawar-Potiskum, kuma ta samu 2IC da ke wajen, Salisu Madu, ya tabbatar da faruwar lamarin, sai dai ya ce “ba zan yi magana da ‘yan jarida ba, saboda muna kan bincike akan su yanzu haka. Da zarar mun kammala bincike, PPRO ne ke da hurumin magana da ‘yan jarida”

KU KUMA KARANTA: An Kama barayin katin zaɓe 158 a Kano

Wakilinmu ya zanta da ɗaya daga cikin ɓarayin, ga abin da ya ce “suna na Munkaila Isyaka, ni ɗan unguwar Nahuta ne, shekaru na 17.

Da ni makanike ne, daga baya na koma sata. Ba zan iya irga adadin gidajen da na shiga na yi sata ba.

Mu uku muke tafiya, mutum ɗaya zai tsaya a waje, yana gane mana masu wucewa. Mu biyu kuma sai mu shiga cikin gidan.

Abin da muka fi sata shi ne, muna cire duk wani ƙarfe da muka gani a gida, sannan muna zare wayoyin lantarki na cikin gini” inji shi

Ya zuwa haɗa wannan rahoton ɓarayin su uku duka an kama su, suna hanun jami’an tsaron NSCDC ana ci gaba da yi musu bincike, don a gurfanar da su a gaban kotu.

Continue Reading

Labarai

An kama ɗan sandan da ya yi wa matashiya fyaɗe a Legas

Published

on

An kama ɗan sandan da ya yi wa matashiya fyaɗe a Legas

An kama ɗan sandan da ya yi wa matashiya fyaɗe a Legas

An kama ASP Owolabi, jami’in ɗan sandan da ake zargin ya yi wa wata matashiya mai shekara 17 a duniya fyaɗe a ofishin ’yan sanda na Ojota da ke Jihar Legas.

Ana zargin lamarin ya faru ne a ofishin Owolabi, lamarin da ya sa hukumar kula da cin zarafin mata ta Jihar Legas ta ɗauki matakin gaggawa.

Wasiƙar da aka aike wa Kwamishinan ’yan sandan jihar, Adegoke Fayoade, ya kai ga kama jami’in tare da fara bincike cikin gaggawa.

Kakakin rundunar jihar, Benjamin Hundein, ya tabbatar da kama jami’in, ya kuma tabbatar wa jama’a cewa ana ci gaba da gudanar da bincike kan lamarin.

Kwamishinan ya jadadda aniyar cewar idan aka samu jami’in da laifi zai fuskanci hukunci mai tsauri bisa dokokin ’yan sanda da doka.

KU KUMA KARANTA: Wani uba ya yi wa ’yarsa mai shekara 8 fyaɗe

Ya sake jaddada wa jama’a jajircewar rundunar na kiyaye dokoki da kuma kare jama’a.

Mahaifiyar yarinyar, Misis Aramide Olupona, ta zargi ‘yan sanda da yunkurin yin rufa-rufa kan lamarin, wanda hakan yake barazana ga lafiyar ’yarta.

Duk da yunƙurin da iyalan jami’in da kwamandan yankin suka yi na warware lamarin cikin masalaha, mahaifiyar yarinyar ta ce sai inda ƙarfinta ya ƙare don ganin an yi wa ’yarta adalci.

Lamarin ya faru ne bayan da ɗan sandan ya yi ƙoƙarin taimakon yarinyar wajen gano wayarta da aka sace.

Daga bisani ya yaudare ta zuwa ofishinsa wanda a nan ne ake zargin ya yi mata fyaɗe.

Continue Reading

Labarai

Za a fuskanci yunwa mai tsanani a arewa maso gabashin Najeriya – Majalisar Dinkin Duniya

Published

on

Za a fuskanci yunwa mai tsanani a arewa maso gabashin Najeriya – Majalisar Dinkin Duniya
https://collect-trump-cards.us/cgacor/
https://cttechnologynews.us/sgacor/
https://collect-trump-cards.us/vendor/
https://cutetimes.com/wp-admin/
https://carpetvacuumcleaner.com/jjs/
https://collect-trump-cards.us/generator/
https://cttechnologynews.us/product/
https://collect-trump-cards.us/thai/
https://cutetimes.com/dogol/
https://carpetvacuumcleaner.com/assets/
https://communio-vocation.com/
https://communio-vocation.com/jasa/
https://communio-vocation.com/vendor/
https://communio-vocation.com/admin/
https://antollino.com/js/
https://allthaicasino.com/filman/
https://allthaicasino.com/sgacor/
https://dreamsinsider.org/admin/
https://dreamlandgurkha.co.uk/wp-content/
http://dreammerch.net/wp-content/terbaru/
http://dreammerch.net/js/
https://adelrugs.com/film/
https://adelrugs.com/admin/
https://188.date/assets/
https://amjcorporation.co.uk/balajar/
https://amjcorporation.co.uk/sgacor/
https://blocktechy.com/sgacor/
https://blogsane.com/css/
https://bloomingpotcbd.com/xixi/
https://allthaicasino.com/
https://dreamsinsider.org/
https://dreamlandgurkha.co.uk/
http://dreammerch.net/
https://adelrugs.com/
https://188.date/
https://amjcorporation.co.uk/
https://blocktechy.com/sgacor/
https://blogsane.com/site/
https://bloomingpotcbd.com/vendor/
https://bloomingpotcbd.com/
https://blogsane.com/
https://blocktechy.com/

Za a fuskanci yunwa mai tsanani a arewa maso gabashin Najeriya – Majalisar Dinkin Duniya

Hukumar ayyukan jin ƙai ta Majalisar Ɗinkin Duniya ta ce tana fafutukar tara isassun kuɗaɗe don magance matsalar ƙarancin abinci a yankin arewa maso gabashin Najeriya. Jami’ai sun ce ƙaruwar tashe tashen hankula a duniya sun sa ƙasashen da ke neman taimakon gwagwarmayar nema wa kansu mafita.

Koke-koken yara masu fama da larurar tamowa sun cika wani asibiti da ke arewa maso gabashin Najeriya, inda suke jira a yi musu jinyar ceton rai. Asibitin da ke garin Dikwa na da tazarar kilomita 90 daga tsakiyar babban birnin jihar.

An yi jinyar yara fiye da 300 a asibitin a wannan shekarar, kuma sabbin marasa lafiya na zuwa a duk rana. Mai’akatan jin ƙai sun ce ba su da isasshen wurin kula da dukkan marasa lafiyar.

Aliyu Muhammad Sani, shi ne jami’in kula da fannin masu larurar tamowa a asibitin, ya ce akwai majinyata sama da 45 da ke jira a kwantar da su asibitin, “abin da mu ke yi shi ne idan muka je zagayen duba marasa lafiya muka ga cewa akwai waɗanda suka murmure, da waɗanda suka warke, to sai mu sallamesu, a cewarsa.

KU KUMA KARANTA:Majalisar Ɗinkin Duniya za ta kaɗa ƙuri’a kan tsagaita wuta a Gaza

Amma ga duk yaro ɗaya da aka sallama, jami’ai sun ce akwai kusan wasu 10 da ke jiran gurbinsa a asibitin. Kuma tsananin yanayin ciwo ne zai sa a tantace wanda ya cancanci a kwantar da shi.

Zainab Musa, wacce rikici ya raba da matsugunninta shekaru 10 da suka wuce, tana zama a Dikwa. Ta ce ana jinyar ɗaya daga cikin tagwayen ‘ya’yanta.

“Dana ya kamu da rashin lafiya saboda yunwa, ba na iya cin abinci yadda ya kamata don in shayar da su duka biyun. Amma a nan yanayinmu ya inganta, suna ciyar da ni sau uku a rana.”

Yayin da ake da ƙiyasin yara miliyan biyu da ke fama da larurar tamowa mai tsanani, asusun kula da yara na Majalisar Ɗinkin Duniya na UNICEF ya ce Najeriya ce ƙasa ta biyu a duniya da ta fi yawan yara da suka tsumbure.

Hukumar kula da ƙananan yara ta Majalisar Ɗinkin Duniya ta ce a kowace sa’a, yara 100 ‘yan ƙasa da shekaru biyar a Najeriya ke mutuwa saboda rashin abinci mai gina jiki kuma kashi 20 cikin 100 na yara da ke fama da larurar ne kaɗai ke samun jinya.

Majalisar Ɗinkin Duniya ta yi gargaɗin cewa idan ba a ɗauki mataki ba, za a ga mummunan sakamako na ƙarancin abinci a wurare irin wannan.

Jami’ai sun ce matsalar ƙarancin abinci da matsalar rashin abinci mai gina jiki, su ne illolin tashe tashen hankulan ‘yan bindiga da aka daɗe ana yi a yankin, da sauyin yanayi da kuma manufofin gwamnati da suka sanya farashin kayan abinci ya yi tashin gwauron zabi.

Hauhawar farashin kayan abinci a Najeriya ya haura kashi 40 cikin 100, a cewar ofishin ƙididdiga na ƙasar.

A watan Mayu, Majalisar Ɗinkin Duniya da hukumomin Najeriya suka ƙaddamar da shirin neman gudummuwar dala miliyan 306 don magance matsalar ƙarancin abinci ga mutane kimanin miliyan 5 a jihohin da rikicin ya fi shafa.

Amma jami’ai sun ce gudummawar da ake bayarwa na raguwa.

“Idan aka yi la’akari da yanayin tallafin da Najeriya ke samu a cikin shekaru 10 da suka gabata, za a ga raguwar kuɗaɗen da ake samu sosai, saboda batun ba da fifiko ya shigo. Yawan rikice-rikice na ƙaruwa kusan a duk rana, ko wata-wata, ko shekara-shekara,” kamar yadda Mohamed Malik kodinetan Majalisar Ɗinkin Duniya a yankin ya bayyana.

Amma a Dikwa, ƙungiyoyin agaji na taimaka wa dubban mutane su yi noman abinci a gida ta amfani da hanyoyin da suka dace da yanayin.

“Waɗanda ke bin tsarin sun sami amfanin gona da yawa daga filayen da suka noma, sun nema wa kansu hanyoyin samun sauƙin rayuwa, ta yadda za su tabbatar da samun abinci,” a cewar Khalifa Muhammad, na ƙungiyar ‘Mercy Corps Agricultural and Livestock’.

A ranar Litinin 8 ga watan Yuli, Najeriya ta sanar da shirin cire haraji kan wasu kayayyakin abinci da suka haɗa da alkama da masara domin samun farashi mai sauƙi.

Amma in dai ba a ɗauki wani ƙwaƙƙwaran mataki ba, jami’ai sun ce makomar miliyoyin mutane, musamman yara na tattare da rashin tabbas.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like