Connect with us

Ƙasashen Waje

Sharuɗɗan da ƙasa za ta cika kafin ficewa daga ECOWAS

Published

on

Tun bayan da ƙasashen Nijar da Burkina Faso da Mali suka sanar da aniyarsu ta ficewa daga ECOWAS, jama’a da dama ke ta ce-ce-ku-ce dangane da hakan inda wasu ke tambaya ko shin ƙasashen suna da damar ficewa daga ƙungiyar a duk wani lokaci da suke so.

Tun bayan kafa ECOWAS a 1975, akwai yarjejeniya a rubuce wadda ta zama dokar gudanarwar ƙungiyar bayan shugabannin ƙasashen ƙungiyar 16 sun saka mata hannu, inda aka sake sabunta yarjejeniyar a shekarar 1993 inda shugabannin ƙasashen ƙungiyar waɗanda suka zama 15 daga baya suka saka mata hannu.

Yarjejeniyar ta tanadi abubuwa da dama da suka shafi tsare-tsare da dangantaka da kuma yadda za a gudanar da ayyukan ƙungiyar.

Babbar tambayar da jama’a suka fi yi a halin yanzu ita ce ko akwai matakai da aka tanada kafin ficewa daga ECOWAS?

KU KUMA KARANTA: Najeriya ta ce ba ta ji daɗin ficewar Nijar, Mali da Burkina Faso daga ECOWAS ba

A cikin sashe na 91 na ƙundin yarjejeniyar ECOWAS ta 1993, an tanadi wasu hanyoyi da ƙasa mambar ƙungiyar za bi kafin ficewa.

“Duk wata ƙasa mamba da ke son ficewa daga ƙungiyar za ta bayar da sanarwa a rubuce ga Babban Sakataren ƙungiyar shekara guda kafin ficewar, wanda shi kuma zai shaida wa jihohi mambobi.

“Zuwa lokacin da wa’adin zai kawo ƙarshe, idan ba a janye ƙudirin ba, ƙasar za ta kasance ta fita daga ƙungiyar,” kamar yadda yarjejeniyar ta ce.

Yarjejeniyar ta tanadi cewa a cikin shekara ɗaya da bayar da wannan sanarwar, akwai buƙatar ƙasar da ke son ficewar ta ci gaba da bin dokoki da tsare-tsaren ƙungiyar kamar yadda yarjejeniyar ta tanada.

Tun bayan juyin mulki na baya-bayan nan da aka yi a Nijar wanda aka hamɓarar da Shugaba Mohamed Bazoum, ƙasashen Nijar da Burkina Faso da Mali suka ƙara haɗa kansu tare da bijire wa ECOWAS.

Duka ƙasashen uku sojoji ne ke mulkinsu bayan sojojin sun yi wa gwamnatocin farar hula juyin mulki, dalilan da ya sa kenan ECOWAS ɗin ta saka musu takunkumai.

An ta ƙoƙarin sulhu tsakanin ƙasashen da ECOWAS sai dai abin ya ci tura.

Bayan haka ƙasashen sun ƙulla ƙawancen Sahel Alliance ko kuma Liptako-Gourma wadda wasu ke kallo tamkar kishiya ce ga ECOWAS.

Ƙasashen sun ce wannan yarjejeniyar da suka yi za ta mayar da hankali wurin ci-gabansu ta fannin tsaro da tattalin arziki.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Ƙasashen Waje

Harin ta’addanci ya kashe sama da mutane 20 a Mali

Published

on

Harin ta'addanci ya kashe sama da mutane 20 a Mali

Harin ta’addanci ya kashe sama da mutane 20 a Mali

Wani hari da ake kyautata zaton masu ikirarin jihadi ne suka kai ƙauyen Djiguibombo da ke kusa da garin Bandiagara a yankin tsakiyar ƙasar Mali, ya yi sanadiyar mutuwar fararen hula 20, kamar yadda wasu hukumomin yankin biyu suka tabbatar.

Majiyoyin da suka nemi a sakaya sunansu sun tabbatar da mutuwar mutane 20, sannan suka ce yadda lamuran tsaro suka taɓarɓare a yankin, ya hana jami’an tsaro kai ɗauki wajen.

Wani jagoran matasan yankin shi ma da ya nemi a sakaya sunansa, ya ce tun a farkon daren ranar Litinin ɗin data gabata ne maharan suka kai farmakin, inda suka kwashe tsawon sa’oi uku a cikin garin.

KU KUMA KARANTA: Isra’ila ta kashe ‘yan jarida 106 a yakin da take yi a Gaza — Jami’ai

Ya ce sama da mutane 20 ne aka kashe a harin, kuma fiye da rabinsu matasa ne inda aka ranke musu harsuna.

Kasar Mali dai na fama da matsalolin tsaro na ƙungiyar Al-Qaeda da kuma na IS tun a shekarar 2012, inda ya bazu kasashen Burkina Faso da Nijar da ke makwabtaka da ita.

Tun bayan ƙwace mulki da sojoji suka yi a kasar a shekarar 2020, hukumomi  ke jin tsoron fitowa fili su sanar da labarin hare-haren ta’addancin da ake kai wa kasar da ke Yammacin Afrika.

Continue Reading

Ƙasashen Waje

A shirye muke mu yaƙi Hizbollah idan har ta kama – Ministan Tsaron Isra’ila

Published

on

A shirye muke mu yaƙi Hizbollah idan har ta kama - Ministan Tsaron Isra'ila

A shirye muke mu yaƙi Hizbollah idan har ta kama – Ministan Tsaron Isra’ila

Ministan Tsaron Isra’ila Yoav Gallant ya ce sojojin Isra’ila za su kasance a shirye don daukar duk wani matakin da ya dace kan ƙungiyar Hizbullah ta ƙasar Labanon, ko da yake abin da ake so shi ne cimma matsaya ta shawarwari.

Muna kai wa ƙungiyar Hizbullah hari sosai a kowace rana kuma za mu kai ga cikakken shiri na ɗaukar duk wani mataki da ake buƙata a ƙasar Labanon, ko kuma cimma wani shiri daga matsayi mai ƙarfi.

KU KUMA KARANTA: Gaza ya zama gidan marayu kuma maƙabartar yara mafi girma a duniya – Emine Erdogan

Mun fi son tsari, amma idan aka kai mu maƙura za mu san yadda za mu yi yaƙi,” an ruwaito Gallant a wata sanarwa da ofishinsa ya fitar.

Continue Reading

Ƙasashen Waje

Mutum 12 ne suka mutu, 20 suka jikkata a wani hari da aka kai wata kasuwa a Yammacin Sudan

Published

on

Mutum 12 ne suka mutu, 20 suka jikkata a wani hari da aka kai wata kasuwa a Yammacin Sudan

Mutum 12 ne suka mutu, 20 suka jikkata a wani hari da aka kai wata kasuwa a Yammacin Sudan

Aƙalla mutum 12 ne suka mutu yayin da wasu 20 suka jikkata a jiya Laraba a wani hari da aka kai kan wata kasuwar dabbobi da ke El Fasher, babban birnin jihar Darfur ta Arewa a Yammacin Sudan.

A wata sanarwa da kwamitin sulhu na kwamitocin ‘yan gwagwarmaya na El Fasher ya fitar ya ce “harbin bindigogi a kasuwar dabbobi da ke birnin El Fasher ya yi sanadin mutuwar fararen hula 12 da kuma wasu 20 da suka samu raunuka daban-daban.”

Tun da fari a ranar Larabar da safe, kwamitocin ‘yan gwagwarmaya sun ce dakarun Rapid Support Forces (RSF) sun kai mummunan hari El Fasher da manyan bindigogi.

Tun a ranar 10 ga Mayu, aka fara ƙazamin fada tsakanin sojojin Sudan da RSF a El Fasher. Majalisar Dinkin Duniya da ƙungiyoyin agaji na ƙasa da ƙasa ke amfani da birnin a matsayin cibiyar ayyukan jinƙai ga yankin Darfur.

Rikicin Sudan ya ɓarke ne a cikin watan Afrilun 2023 tsakanin Janar Abdel Fattah al-Burhan da kwamandan RSF Mohamed Hamdan Dagalo kan yarjejeniyar shigar da RSF cikin rundunar soja.

KU KUMA KARANTA: Adadin mutanen da suka rasa muhalli a sassan duniya ya zarta miliyan 114 — MƊD

Ya yi sanadin mutuwar mutum sama da 16,000, da raba kusan mutum miliyan 10 da muhallansu, sannan sama da miliyan 25 na buƙatar agajin jinƙai, lamarin da ya zama mafi girma a duniya ta ɓangaren matsalar rashin matsuguni da yunwa, a cewar MƊD.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like