Connect with us

Labarai

Rikici ya raba yara miliyan 1.8 da muhallansu a yankin Sahel – Save The Children

Published

on

Rikice-rikice da ake fama da su a ƙasashen Mali da Burkina Faso da Nijar, sun tilasta wa yara kusan miliyan 1.8 barin gidajensu, wanda ke nuna ƙaruwar hakan sau biyar cikin shekaru biyar da suka gabata, in ji ƙungiyar agaji ta Save the Children a ranar Alhamis.

Ƙungiyar mai zaman kanta ta ƙididdige adadin yaran da suka rasa matsugunansu a kasashen Sahel uku ta hanyar yin nazari kan alkaluman hukumar kula da ‘yan gudun hijira ta Majalisar Ɗinkin Duniya (UNHCR) da gwamnatocin kasashe da kuma kungiyar kula da masu ƙaura ta duniya (IOM).

Binciken ya nuna cewa adadin yaran da aka tilasta wa barin gidajensu ya ƙaru daga kusan 321,000 a shekarar 2019 zuwa kusan miliyan 1.8 a yau.

“Rikicin, wanda aka manta da shi a tsakiyar Sahel ya kasance daya daga cikin mafi munin bala’in gaggawa na jinƙai a duniya, wanda ya fi muni la’akari da yadda cewa wannan rikicin ya fi shafar yara kuma mafi ƙarancin shekaru a duniya,” in ji Vishna Shah, Daraktar Ƙungiyar a yankin Sahel.

Ta ƙara da cewa, “Miliyoyin yara na rayuwa ne a cikin ƙaurace wa mummunan rikicin da ba za a iya misalta su ba, wadannan yaran sun riga sun kasance za su taso a daya daga cikin wuraren da ke da wahala a duniya sakamakon rasa gidajensu da al’ummominsu da duk abin da suka sani.”

KU KUMA KARANTA: Australia ta goyi bayan ƙudurin MƊD na tsagaita wuta a Gaza

Ita ma ƙasar Cote d’Ivoire wacce ta fice daga yakin basasar da ta yi a shekarar 2011, ƙamarin da tashe-tashen hankula a yankin Sahel ke yi na shafarta, in ji kungiyar Save the Children.

Rikici a makwabciyarta Burkina Faso da Mali ya haifar da karuwar yara masu neman mafaka sau goma sha biyu a kasar, daga kusan 2,450 a karshen shekarar 2022 zuwa kusan 29,700 a halin yanzu.

Yara su ne kashi 40 cikin 100 na mutanen da ke gudun hijira a duniya, a cewar Majalisar Dinkin Duniya, amma sun fi yawa a yammaci da tsakiyar Afirka.

Sun kai kusan kashi 58 cikin 100 na waɗanda aka tilasta musu yin gudun hijira, a cikin nazarin da Save the Children ta yi.

Ƙasashen Burkina Faso da Mali da Nijar dai na fama da tashe-tashen hankula da juyin mulki da fatara da ƙarancin abinci na tsawon shekaru.

Mummunan cin zarafi da ake yi wa yara a cikin rikice-rikice da suka hada da kisa da raunata su da sacewa da saka yara kanana cikin kungiyoyi masu dauke da makamai ko kuma a matsayin sojoji ya karu a cikin ‘yan shekarun nan, musamman a Mali, in ji kungiyar Save the Children.

Haka kuma yankin Sahel na kan gaba wajen fuskantar matsalar sauyin yanayi.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like