Connect with us

Labarai

Nijar ‘yan’uwanmu ne, kar a tura sojoji su yaƙe su – El-Zakzaky ga Tinubu

Published

on

Jagoran Harkar Musulunci a Najeriya (Islamic Movement), Shaikh Ibraheem El-Zakzaky ya gargaɗi shugaba Bola Tinubu akan tura dakarun soji a jamhuriyar Nijar, inda ya bayyana cewa suna da tarihi tare don haka ‘yan uwan juna ne.

El-Zakzaky ya bayyana haka ne a lokacin da yake jawabi ga gungun masu karatun Alkur’ani a lokacin da suka kai masa ziyara a gidansa da ke Abuja.

Shaikh Zakzaky ya ƙara da zargin Faransa da Amurka da son amfani da Najeriya wajen kai wa Jamhuriyar Nijar hari.

“Ba zato ba tsammani, Faransa da Amurka suna son amfani da Najeriya wajen kai wa Nijar hari.

Wannan abin mamaki ne matuƙa ganin yadda Najeriya da Nijar mutane ɗaya ne.

Ko kudancin Najeriya ba haka yake ba, mu a arewacin Najeriya muna da dauloli waɗanda Shehu Usman Danfodio da Kanem Borno suka kafa.

Yankunan irin waɗannan masarautu ne aka yayyanka don samar da Nijar da Najeriya.”

KU KUMA KARANTA: Ecowas za ta gudanar da taron ƙoli kan Nijar a Abuja

“Na taɓa gaya muku Gazargamu babban birnin Kanem Borno ne ko? Katangar birnin ba ta cika ba saboda har yanzu akwai ragowar gine-ginen.

Yana iya ba ku sha’awa ku lura cewa rabin katangar tana gefen iyakar Nijar ne, sauran kuma tana cikin Najeriya. Lokacin da aka raba kan iyakokinmu, ba su ɗauki tarihinmu a cikin sani ba.

“Kamar yadda nake gaya muku, an raba yankin Borno gida huɗu, Najeriya, Kamaru, Chadi, da Nijar.

Yawancin yankin na Borno ne. Bugu da ƙari, idan aka duba yankin daular Shehu Usman, daga Borno har zuwa Sakkwato, an raba kowane gari gida biyu”, inji shi.

El-Zakzaky ya ci gaba da cewa, “Idan ka duba yankin Haɗeja, an mayar da wani yanki nasa zuwa Nijar. Wani yanki na yankin Gumel wani yanki ne na Nijar.

Idan ka haye kan iyakar Maigatari, har yanzu kana cikin yankin Gumel amma an miƙa wani yankin ga Nijar. Wani sashe na Kazaure ma yana cikin Nijar ne.”

“Wannan ita ce makomar Daura. Wani babban yanki na Daura shi ma ya zama yankin Nijar.

An kuma raba Katsina gida biyu: Katsinan Maraɗi da Katsina ta Najeriya. An raba su duka. Haka kuma an raba daular Gobir tsakanin Nijar da Najeriya. Garin da aka haifi Shehu Usman Ɗanfodio, Marata, yana cikin Nijar.”

Ya ce alaƙar al’adu da Nijar da Najeriya ke da su ya fi kusanci fiye da yadda mutane ke zato, inda ya bayyana cewa su tagwaye ne, tushensu da ɗabi’u ɗaya ne. “Su ’yan’uwanmu ne, tun da yake garin mahaifinmu Shehu Ɗanfodiyo, yana cikin ƙasarsu.

Abin mamaki ne yadda waɗannan marasa tausayi suke so su yi amfani da ƙasar nan su kai wa ’yan’uwanmu hari, don kawai su yi kisan kiyashi na ’yan’uwa, ko?” “Na ji cewa wasu ‘yan Nijar sun yi iƙirarin cewa Najeriya za ta kai musu hari. Ina ba da shawarar ku daina wannan tunanin.

Ko da barazanar mamayewa ta bayyana da gaske, Allah Ya kiyaye, ba mu ne muke kawo muku hari ba. Hannun wani mai iko ne a bayan fage tare da haɗin gwiwar shugaban ƙasa za su kawo muku hari, amma ba ’yan Najeriya ba.

“Ba a tuntuɓe mu ba, ba ma goyon bayansa, kuma babu yadda za a yi mu kashe juna.

Don haka ba Najeriya ce za ta kai hari ba, wasu ƙasashen waje ne ke son yin amfani da Najeriya wajen yin hakan. Sun saba da wannan.

“Sun taɓa yin hakan bayan juyin juya halin Musulunci a Iran lokacin da suka yi amfani da Saddam Hussein wajen mamaye Iran.

Yaƙin dai ya shafe shekaru 8 ana gwabzawa yayin da mutanen Iran da Iraƙi al’umma ɗaya ne. Dangantakar al’adu da suke da ƙarfi ta yadda wani ɗan Iraƙin ke riƙe da wani babban muƙami a Iran.

“Ayatullah Sahrudi wanda shi ne babban alƙalin kasar Iran, dan ƙasar Iraƙi ne. Shi ne babban alƙalin ƙasar Iran.

Za ku ga makamai da yawa da ‘yan Iraƙin ke ba su, kuma babu wanda ya tayar da gira a kan lamarin kawai saboda suna ganin juna ɗaya.”

1 Comment

1 Comment

  1. Pingback: Ba mu kai wa jamhuriyar Nijar hari ba – Faransa | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like