Connect with us

Ƙasashen Waje

Nijar ta gaza biyan bashin da ya kai dala miliyan ɗari biyar – WAEMU

Published

on

Jamhuriyar Nijar ta gaza biyan bashin fiye da dala miliyan ɗari biyar tun da sojoji suka kifar da gwamnatin farar-hula a watan Yulin da ya gabata, a cewar ƙungiyar da ke sa ido kan kuɗaɗen yankin Yammacin Afirka.

Umoa-titres, wadda ke lura da Harkokin Kuɗi na Ƙungiyar Ƙasashen Yammacin Afirka (WAEMU), ta wallafa sanarwa guda takwas tun farkon wannan shekara da ke jan hankalin masu zuba jari cewa Nijar ta “gaza cika alƙawuran da ta ɗauka na kasuwar hada-hadar kuɗi ta Gwamnati”.

Ta ce ana bin ƙasar bashin da ya kai CFA biliyan 313 ($515m) tun da sojoji suka ƙwace mulki a watan Yuli wanda ya kamata ta biya ranar 16 ga watan Fabrairu.

“Ya kamata a sani cewa wannan batu na gaza biyan bashi ya faru ne a lokacin da shugabannin ƙasashe da gwamnatoci na ƙungiyar da ke lura da Harkokin Kuɗi na Ƙasashen Yammacin Afirka suka sanya wa Nijar takunkumai kan harkokin kuɗi,” kama yadda Umoa-titres ta bayyana ranar Litinin.

Umoa-titres ce ke da alhakin gudanarwa da tallata harkokin kuɗi na Yammacin Afirka, waɗanda suka haɗa ƙasashe takwas da ke amfani da CFA franc a matsayin kuɗinsu — Ivory Coast, Senegal, Togo, Burkina Faso, Mali, Guinea-Bissau, Nijar da Benin.

KU KUMA KARANTA: Za mu ci gaba da tattaunawa da Nijar domin samun maslaha – ECOWAS

A makon jiya, cibiyar Moody’s da ke auna ƙarfin iya biyan bashin ƙasashe da tattalin arzikinsu ta rage matsayin Nijar na iya biyan bashi daga matakin Caa2 zuwa Caa3 karo na uku a jere tun da sojoji suka yi juyin mulki.

“Takunkuman da aka sanya wa ƙasar tun ƙarshen watan Yulin 2023 sakamakon juyin mulkin da sojoji suka yi sun ta’azzara mawuyacin hali na tattalin arziki sannan sun yi tarnaƙi ga gwamnati wajen iya biyan bashi,” a cewar cibiyar.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Ƙasashen Waje

Mutumin da ya fi kowa tsallake haɗari a duniya ya mutu

Published

on

Mutumin da ya fi kowa tsallake haɗari a duniya ya mutu

Mutumin da ya fi kowa tsallake haɗari a duniya ya mutu

Daga Ibraheem El-Tafseer

Frane Selak ya kasance wanda ya fi kowa tsallake rijiya da baya a duniya.

A shekarar 1962 ya tsallake haɗarin jirgin ƙasa wanda mutane 17 suka mutu, a 1963 jirgi ya faɗi da shi kowa ya mutu sai shi kaɗai ko ƙwarzane bai yi ba.

A shekarar 1966 motar safa ta lume da su a rafi mutum huɗu sun mutu amma Frane bai samu ko ƙwarzane ba a yayin da a shekarar 1973 motarsa ta kama da wuta ya tsallake rijiya da baya, ya kuma tsallake haɗarin taho mu gama da mota ta yi da shi ya tsira ya kuma lashe yuro dubu ɗari takwas a Caca a shekarar 2003.

KU KUMA KARANTA: Labarin zuwa Hajji mai ban mamaki

Continue Reading

Ƙasashen Waje

Isra’ila ta ƙaddamar da sabbin hare-hare a kudancin Gaza

Published

on

Isra'ila ta ƙaddamar da sabbin hare-hare a kudancin Gaza

Isra’ila ta ƙaddamar da sabbin hare-hare a kudancin Gaza

Isra’ila ta ƙaddamar da sabbin hare-hare a kudancin Gaza, inda ta tilasta wa ɗaruruwan Falasɗinawa tserewa bayan da soji suka kuma ba da umarnin ƙaurace wasu yankuna masu yawan jama’a.

KU KUMA KARANTA: Sojojin Isra’ila sun ce an yi musayar wuta da dakarun Masar

Waɗanda suka shaida lamarin sun ce an kai hari da dama a ciki da wajen birnin Khan Younis, inda aka hallaka mutane takwas kuma mutane sama da 30 suka samu raunuka, cewar wata majiyar lafiya da kuma ƙungiyar Red Crescent ta Falasɗinawa.

Continue Reading

Ƙasashen Waje

Farashin man fetur zai ƙaru a watan Yuli a Ghana – COPEC

Published

on

Farashin man fetur zai ƙaru a watan Yuli a Ghana - COPEC

Farashin man fetur zai ƙaru a watan Yuli a Ghana – COPEC

Ƙungiyar Kare Haƙƙin Masu Amfani da Man Fetur a Ghana ta yi hasashen cewa akwai yiwuwar a samun ƙarin farashin man fetur a ƙasar a farkon watan Yulin 2024.

Ƙungiyar ta Chamber for Petroleum Consumers (COPEC) ta ce akwai alamu masu ƙarfi da ke nuna cewa farashin fetur da man dizel da gas zai ƙaru baki ɗaya a gidajen man da ke faɗin ƙasar, kamar yadda kamfanin watsa labarai na ƙasar Ghana ya ruwaito.

COPEC ɗin ta ce za a samu ƙarin farashin ne sakamakon yadda farashin Cedi ɗin a ƙasar ke ƙara karewa idan aka kwatanta da dalar Amurka.

COPEC ɗin ta yi hasashen cewa farashin man fetur ɗin wanda za a rinƙa sayarwa a gidan mai zai ƙaru da kashi 2.17 cikin 100, wanda hakan ke nufin zai ƙaru daga Cedi 14.17 zuwa Cedi 15.20 a duk lita.

Sai kuma farashin dizel ana sa ran ya ƙaru zuwa 15.21 a kowace lita ɗaya, sai kuma na gas ya koma tsakanin Cedi 13.24 zuwa Cedi 14.64 a duk kilo ɗaya.

KU KUMA KARANTA: Ɗan Ghana ya kafa tarihi na rungumar bishiyoyi a duniya

Ƙungiyar ta COPEC ta bayar da shawara ga gwamnatin Ghana da ta yi duk mai yiwuwa domin rage harajin da yake a kan gas ko kuma yin tallafi a farashinsa domin bayar da dama ga ‘yan ƙasar su same shi a farashi mai rahusa.

Ta kuma yi ƙira ga gwamnati da kada ta yi ƙasa a gwiwa wajen dawo da matatar mai ta Tema a kan aiki (TOR) don kaucewa ko kuma rage shigo tattacen man fetur wanda a wani lokacin ake samun gurɓatacce.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like