Connect with us

Ƙasashen Waje

Mutum 20 sun rasu a harin da RSF ta kai wani ƙauye na Sudan

Published

on

Rundunar RSF ta Sudan ta kashe aƙalla mutum 20 a wani hari da ta kai wani ƙauye da ke kudancin Khartoum babban birnin ƙasar, kamar yadda wani kwamiti na ƴan gwagwarmaya a ƙasar ya tabbatar.

Kamfanin dillancin labarai na AFP ya ruwaito cewa RSF “ta kai hari kan ƙauyen Um Adam” mai nisan kilomita 150 daga Sudan a ranar Asabar, kamar yadda sanarwar da kwamitin ya fitar ta bayyana.

Yaƙi tsakanin sojojin Sudan ƙarkashin jagorancin Abdel Fattah al-Burhan da kuma rundunar RSF ƙarƙashin jagorancin Mohamed Hamdan Daglo ya soma ne 15 ga watan Afrilu.

An kashe dubban mutane, daga ciki har da wasu 15,000 da aka kashe a gari ɗaya a yankin Darfur, kamar yadda Majalisar Ɗinkin Duniya ta tabbatar.

Yaƙin ya kuma raba sama da mutum miliyan 8.5 da muhallansu tare da lalata ababen more rayuwa da dama da ke Sudan ɗin.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin tsohon firaiministan Sudan Hamdok da laifin ‘tunzura’ mutane su yi yaƙi

Harin da aka kai a ranar Asabar ya yi sanadin “sama da mutum 200 sun samu rauni, sama da 20 kuma sun rasu,” in ji sanarwar.

Wata majiya daga asibitin Manaqil mai nisan kilomita 80, ta tabbatar wa kamfanin dillancin labarai na AFP cewa sun karɓi “sama da mutum 200 waɗanda suka samu rauni, wasu daga cikinsu an yi jinkirin kai su”.

“Muna fuskantar ƙarancin jini kuma ba mu da isassun ma’aikatan lafiya,” kamar yadda majiyar ta ƙara da cewa.

Sama da kaso 70 cikin 100 na kayayyakin kiwon lafiya da ke Sudan ba su aiki, kamar yadda Majalisar Ɗinkin Duniya ta bayyana, inda waɗanda suka rage kuma suna karɓar marasa lafiya fiye da yadda za su iya ɗauka.

Duka ɓangarorin da ke rikici da juna na zargin juna da aikata laifukan yaƙi, daga ciki har da kai hari kan fararen hula da buɗe wuta kan mai uwa da wabi da sace-sace da hana kai kayan agaji.

Tun bayan ƙwace iko da jihar Al-Jazira da ke kudancin Khartoum a watan Disamba, RSF ɗin ta ci gaba da yin ƙawanya da kai hari a duka ƙauyuka daga ciki har da Um Adam.

Zuwa watan Maris, aƙalla ƙauyuka 108 a faɗin ƙasar aka ƙona “ko dai baki ɗaya ko kuma wani ɓangare”, kamar yadda wata cibiya da ke bincike ta Birtaniya mai suna Centre for Information Resilience ta gano.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Ƙasashen Waje

Jami’ai a Gaza sun zaƙulo gawawwakin Falasɗinawa 21 daga cikin ɓaraguzai

Published

on

Jami'ai a Gaza sun zaƙulo gawawwakin Falasɗinawa 21 daga cikin ɓaraguzai

Jami’ai a Gaza sun zaƙulo gawawwakin Falasɗinawa 21 daga cikin ɓaraguzai

Jami’an kare farar hula a Gaza sun zaƙulo gawawwaki 21 na Falasɗinawa daga cikin ɓaraguzai a ranar Lahadi bayan wani hari da Isra’ila ta kai a Zirin Gaza.

Wata majiya daga ɓangaren kiwon lafiya ta bayyana cewa an gano gawar mutum shida sakamakon harin da Isra’ila ta kai a birnin Rafah inda aka kai su asibitin Khan Younis.

Haka kuma an ƙara zaƙulo wasu gawawwakin uku daga cikin ɓaraguzai a yammacin Gaza, kamar yadda Hukumar Kare Fararen Hula ta Gaza ta bayyana a wata sanarwa.

READ ALSO: Isra’ila ta kashe Falasɗinawa 29 a harin da ta kai a wata makaranta a Gaza

Jami’an sun ƙara gano wasu gawawwakin goma a unguwar Tel al-Hawa da ke kudu maso yammacin Gaza.

Sai kuma mazauna sansanin gudun hijira na Nuseirat sun gano gawawwakin mutum biyu a tsakiyar Zirin Gaza, kamar yadda shaidu suka bayyana.

Continue Reading

Ƙasashen Waje

Faɗa da ruwan bama-bamai a birnin Gaza bayan ba da umarnin kwashe jama’a

Published

on

Faɗa da ruwan bama-bamai a birnin Gaza bayan ba da umarnin kwashe jama'a

Faɗa da ruwan bama-bamai a birnin Gaza bayan ba da umarnin kwashe jama’a

An gwabza ƙazamin faɗa da ruwan bama-bamai a birnin Gaza da wasu yankunan Falasɗinawa a yau Juma’a yayin da masu shiga tsakani ke ci gaba da kokarin dakatar da yakin da ya shiga cikin wata na goma.

Shugaban Amurka Joe Biden ya faɗa a taron Ƙungiyar Tsaro ta NATO a birnin Washington jiya Alhamis cewa jami’an diflomasiyyar Amurka, duk da matsalolin da ake fuskanta, suna samun “ci gaba” tare da masu shiga tsakani na ƙasa da ƙasa wajen cimma yarjejeniyar tsagaita wuta tare da jaddada cewa “lokaci ya yi da za a kawo ƙarshen wannan yaƙi”.

KU KUMA KARANTA: Isra’ila ta kashe Falasɗinawa 29 a harin da ta kai a wata makaranta a Gaza

Kafofin yaɗa labarai masu alaƙa da mahukuntan yankin Hamas, sun ce sojojin Isra’ila sun ƙaddamar da sabbin hare-haren sama fiye da 70.

Ma’aikatar Lafiya ta Gaza ta ba da rahoton mutuwar mutum 32, tana mai cewa “an kai waɗanda suka mutun, waɗanda akasarinsu yara da mata ne zuwa asibitoci cikin dare, saboda kisan kiyashin da ake ci gaba da yi”.

Rundunar sojin Isra’ila ta ce tana kuma gwabza faɗa a yankin Rafah da ke kudancin ƙasar, inda dakarunta suka “kawar da ‘yan ta’adda da dama a hare-hare ta sama”.

Continue Reading

Ƙasashen Waje

Fursunoni sun tsere daga gidan yarin Nijar da ke tsare da masu ta da ƙayar baya

Published

on

Fursunoni sun tsere daga gidan yarin Nijar da ke tsare da masu ta da ƙayar baya

Fursunoni sun tsere daga gidan yarin Nijar da ke tsare da masu ta da ƙayar baya

Ma’aikatar Harkokin Cikin gida ta Jamhuriyar Nijar ta ce ta umarci sassan bincike na ƙasar da su kasance cikin shirin ko ta kwana bayan da fursunoni suka tsere a ranar Alhamis daga gidan yari mai cike da mai tsaro na Koutoukale inda ake tsare fursunonin da suka haɗa da masu ikirarin jihadi.

Sanarwar da ma’aikatar ta fitar ba ta bayyana adadin fursunonin da suka tsere daga Koutoukale da ke da tazarar kilomita 50 daga arewa maso yammacin Yamai babban birnin kasar ba, ko kuma yadda suka yi hakan. A cikin shekarun 2016 da 2019, an taɓa daƙile yunƙurin fasa gidan yarin.

Fursunonin gidan yarin sun haɗa da waɗanda ake tsare da su daga rikicin kasar da kungiyoyin da ke ɗauke da makamai masu alaƙa da al Qaeda da IS da kuma waɗanda ake zargin mayaƙan Boko Haram ne.

Hukumomin yankin sun kafa dokar hana fita da dare a cikin garin Tillaberi, wanda ke yanki ɗaya da gidan yarin, amma ba su yi ƙarin bayani ba.

KU KUMA KARANTA: Fursunoni 118 sun tsere daga gidan yarin Suleja

Jamhuriyar Nijar da maƙwabtanta da ke tsakiyar yankin Sahel na cikin sahun gaba wajen yaƙi da masu ikirarin jihadi da ke ci gaba da ƙaruwa tun shekarar 2012, lokacin da mayaƙan da ke da alaƙa da al-Qaida suka fara ƙwace wasu sassan kasar ta Mali.

Dubban mutane ne aka kashe a cikin tashe-tashen hankulan tare da raba wasu sama da miliyan uku da muhallansu, lamarin da ya ƙara rura wutar rikicin jinƙai a wasu ƙasashe mafiya talauci a duniya.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like