Connect with us

Labarai

Masu masana’antu sun amince da ƙaddamar da katin lamunin kuɗin dala a Najeriya

Published

on

Kwana biyu bayan ƙaddamar da katin lamuni na kuɗin dala a Najeriya, wato American Express Credit Card, irinsa na farko a Afrika, masana tattalin arziƙi sun fayyace bambancinsa da kuɗin Crypto, yayin da masu masana’antu ke cewa, akwai buƙatar wayar da kan ‘yan kasuwa akan alfanun aiki da katin.

A ranar Alhamis ne kamfanin American Express ya ƙaddamar da katin lamuni na kuɗin dala a birnin Legas, a wani mataki na sauƙaƙa wa ‘yan Najeriya musamman ‘yan kasuwa a harkokinsu da ke da alaƙa da kuɗaɗen ƙetare na dala.

Dakta Lawan Habib Yahya, masanin tattalin arziƙi ne a Najeriya, ya yi ƙarin bayani dangane da alaƙar wannan katin na lamunin kuɗin dala da kuma darajar takardun kuɗin Najeriya na Naira.

“Idan buƙatun neman musayar kuɗaɗen ƙetare na dala suka ragu daga kamfanoni da ɗaiɗaikun mutane, saboda suna samun waɗannan kuɗaɗen ta hanyar katin lamuni daga kamfanin American Express Credit Card, to babu shakka darajar naira na iya ƙaruwa saboda dama yawaitar buƙatun kuɗin dalar ne ke daga farashinta,” a cewar Dakta Lawan.

Da alama dai masu masana’antu a Najeriya sun yi maraba da wannan yunƙuri na ƙaddamar da katin lamuni na kuɗin dala a Najeriya, kamar yadda Alhaji Sani Hussaini Sale, mamba a kwamitin ƙoli na ƙungiyar masu masana’antu ta Najeriya (MAN), kuma mataimakin shugaban cibiyar kula da harkokin kasuwanci, masana’antu, ma’adinai, da ayyukan noma ta jihar Kano (KACCIMA) ya bayyana.

“Dama kokawar cinikayya da ƙasashen waje ta zama da wahala saboda dalar na neman ta tada hankali, amma zuwan wannan tsari na katin ba da lamuni na kuɗin dala zai magance ƙalubalen, musamman yadda idan aka ba ka kuɗi daga dala dubu ɗaya zuwa dubu 20 za su taimaka sosai, a cewar Alhaji Sani.

KU KUMA KARANTA:Muna ƙoƙarin kuɓutar da ɗaliban jami’ar da ‘yan bindiga suka sace – Gwamnatin Kogi

Ya kuma ce “Fatan mu shi ne wannan kamfani na American Express credit Card ya iso Kano a arewacin Najeriya, don mu haɗa hannu da shi a cibiyarmu. Zamu sada shi da ‘yan kasuwa domin wayar da kansu game da alfanun wannan tsari da ya zo da shi”.

Amma a cewar, Dakta Lawan Habib Yahya, akwai bambanci a tsakanin katin lamuni na American Express Credit Card da kuɗaɗen Crypto da ake hada-hadarsu a kafar zamani ta Intanet.

“Shi kuɗin Crypto kuɗi ne da ake juya shi ta kafar sadarwa ta Intanet, ba kuɗi ne lakadan ba, amma shi American Express Credit Card kudi ne lakadan za’a saka maka a katinka kuma ka yi sayayya ko cinikayya da shi a kasashen waje, kamar yadda za ka yi amfani da katinka na bankin Najeriya takardun kuɗi na naira su fita,” inji Dakta Lawan.

Baya ga Najeriya, kamfanin American Express ya ce yana da burin faɗaɗa wannan tsari na katin lamunin kuɗin dala zuwa sauran ƙasashen Afrika kamar su Rwanda da Ghana.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

'Yansanda

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

Published

on

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

Rundunar ’yan sandan Najeriya ta tube wa wasu jami’an ta biyar kaki sakamakon zargin su da karɓar cin hancin kuɗi kimanin Naira miliyan uku.

Mataimakin Shugaban ’yan Sanda mai kula da Shiyya ta shida ta da ke Jihar Kuros Riba, Jonathan Towuru, ya sanar a Kalaba cewa ’yan sandan sun kwace kuɗin ne da bakin bindiga a hannun wani mai abin hawa.

A makon jiya ne aka zargi jami’an da ƙwayar kuɗin da bakin bindiga a hannun wani mutum da rundunar ta sakaya sunansa.

Yanzu haka waɗanda ake zargin an tuɓe masu kaki amma ana tsare da su ana bincike, da zarar an same su da laifi kotu za a turasu ta yanke masu hukuncin da ya dace.

KU KUMA KARANTA: ’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe

Mataimakin shugaban ’yan sandan ya ce waɗanda ake zargin su da karɓar cin hancin kuɗi Naira milyan uku daga wannun wani.

Ko a kwanan baya irin haka ta taba faruwa a kan babbar hanyar Kalaba zuwa Ikom inda aka kama wasu ’yan sanda kan karbar na goro.

Tafiya a kan hanyar na yawan zargin ’yan sanda da kula da shingen bincike a kan hanyar da yawan tatsar su kuɗi.

Continue Reading

Labarai

Ƙaramar Hukumar Kwami ta kafa kwamitin tsaro saboda rikicin manoma

Published

on

Ƙaramar Hukumar Kwami ta kafa kwamitin tsaro saboda rikicin manoma

Ƙaramar Hukumar Kwami ta kafa kwamitin tsaro saboda rikicin manoma

A ƙoƙarinsa na kauce wa rikicin manoma da makiyaya da ke yawan faruwa a lokacin damuna, Shugaban Karamar Hukumar Kwami a Jihar Gombe, Dakta Ahmed Wali Doho, ya kafa kwamitin tsaro da sanya ido kan ɓangarorin.

Da yake zantawa da manema labarai a ofishinsa da ke garin Malam Sidi, shugaban karamar hukumar, ya bukaci manoma da su guji noma burtalolin shanu, wanda hakan ke haifar da rikici tsakaninsu da makiyaya, da ke haifar da asarar rayuka.

Su ma makiyayan ya gargade su da cewa su guji shiga gonakin manoma, saboda hakan ne ke jawo rikici idan suka cinye musu amfanin gona.

A cewarsa, lokacin girbi me aka fi samun rikicin manoma da makiyayan, saboda haka kwamitin zai ci gaba da sa ido daga yanzu har zuwa lokacin girbin don ganin ba a samu rikici ba.

KU KUMA KARANTA: Gwamna Yusuf ya amince da sayen taki na naira biliyan 5 don manoman Kano

Ya ƙara da cewa, kusancin garin Kwami da rafi ya sa ya zama wuri mai kyau don noman rani.

Don haka ya ja hankalin manoman yankin da su yi amfani da wannan damar wajen bunkasa tattalin arzikinsu.

Ya jaddada cewa noman rani na da matukar muhimmanci wajen magance matsalar karancin abinci a Najeriya.

Hakan ne ya sa suka haɗa kan matasan yankin don su fara noman rogo da zai taimaka wajen shawo kan matsalar ƙarancin abinci da rage wa manoma tsadar takin zamani.

Continue Reading

Labarai

’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe

Published

on

’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe

’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe

Rundunar ’yan sandan jihar Yobe ta ƙaddamar da shirin yin gyara da kuma tantance ’yan banga domin kawar da ɓata-garin cikin

Rundunar ’yan sandan jihar Yobe ta ƙaddamar da shirin yin gyara da kuma tantance ’yan banga domin kawar da bata-gari a cikinsu.

Kwamishin ’yan sandan jihar, Garba Ahmed, ya sanar da shirin bayan an kama wasu ’yan banga uku da aikata manyan laifuka.

Ya jaddada muhimmancin sake duba ayyukan ’yan banga a jihar, duk da  muhimmiyar rawar da suke takawa wajen taimaka wa jami’an tsaro a yaki da miyagun laifuka.

Ya ce yin gyaran da kuma tantancewa ya zama dole sakamakon ƙorafe-ƙorafen neman yin hakan daga jama’a.

Ya bayyana cewa jama’a sun yi ƙiran ne bayan kama wasu ’yan banga uku da laifin hada baki wajen shiga gida, sata, ƙwace da kuma sayar da kayan sata a Damaturu.

Wata sanarwa da DSP Dungus Abdul Karim, kakakin rundunar, ya fitar, ta ce wasu daga cikin ’yan banga sun kai korafi bayan faruwar lamarin.

KU KUMA KARANTA: Ƴan bindiga sun kashe mutum 12 a Kaduna, sun kai hari a ofishin ƴan sanda a Zamfara

“A ranar 27 ga watan Yuni, 2024, rundunar ta amsa kiran wani mai shago a Damaturu, wanda ya dauki ’yan banga aikin gadi, amma suka kwashe kayan shagon na makudan kudade ba tare da bayani ba.

“Bincike ya kai ga kama wasu mutane biyu da kayan sata da ake zargin sun saya ne daga wani dan banga wanda nan take aka kama shi.

“Ana shawarta jama’a da su yi taka-tsan-tsan wajen daukar masu gadi, sannan su kai rahoton ’yan banga da aka ga suna aikata laifi a bakin aikinsu.”
Sanarwar ta ci gaba da cewa, rundunar tana ɓullo da tsare-tsare don daukar bayanan ’yan banga domin sa ido kan ayyukansu.

Ta ci gaba da cewa ofisoshin ’yan sanda na yankuna da ke jihar za su jagoranci wannan aikin tantancewan domin kawar da baragurbi a cikin ’yan banga.

“Don  haka ake ƙira ga jama’a da su ci gaba da tallafa wa ’yan sanda wajen jainrahoton ayyukan jami’an tsaron da ba su dace ba a hedkwatar jihar ta lamba 07068858500, ko kuma a gabatar da wasikar korafin ga kwamishinan ’yan sanda  ta hanyar kakakin rundunar,” in ji sanarwar.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like